ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Remi Tinubu Ta Sanya Wa Babban Dakin Taron Cibiyar Mata Ta Abuja Sunan Maryam Abacha

by Bello Hamza
3 years ago
Remi Tinubu

Uwargidan shugaban kasa Oluremi Tinubu, ta sauya sunan babban dakin taron ‘Maryam Babangida National Centre for Women Development’ zuwa sunan Dr. Maryam Abacha, matar tsohon shugaban kasa a mulkin soja, marigayi Janaral Sani Abacha.

 

Zauren wanda a da ake kira da ‘African Peace Mission Hall’, uwargidan shugaban kasar ce ta kaddamar da shi kuma aka canza masa suna zuwa Maryam Abacha, saboda irin gudummawar da ta bayar wajen samar da zaman lafiya a nahiyar Afrika.

ADVERTISEMENT
  • Uwargidan Shugaban kasa, Remi Tinubu Ta Ziyarci Buhari A Daura

A jawabinta, uwargidan shugaban kasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta ce taron muhimmi ne a kokarin hadin gwiwa wajen karfafa alaka tare da bunkasa ci gaban da aka samu wajen samun hadin kai da dawwamammen dangantaka a tsakanin mata.

 

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Ta bayyana Maryam Abacha a matsayin mace mai hazaka kuma jajirtacciya wajen ci gaban nahiyar Afrika baki daya.

 

“Shawararta ne ya samar da ma’aikatar harkokin mata ta tarayya tare da nada mace a matsayin minista, wanda hakan ya fadada zuwa jihohi daban-daban tare da girmama al’amuran matan Nijeriya.

 

“A kwanan nan a yayin sauya sunan wannan cibiya, na jaddada wa mata cewa su dinke barakar da ke tsakaninsu, su nuna halaye masu kyau da kuma mayar da hankali fiye da bambance-bambancen da ke tsakaninmu, kasancewar hadin kan mu a matsayin mata ya fi muhimmanci. Wannan taron yana da mahimmanci a yayin da ya zama babban dama na kafa tarihi wajen samar da dawwamammen zaman lafiya a cikin al’ummarmu.

 

“A yayin cimma burinmu, yana da kyau mu fahimta tare da karrama mutanen da suka taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa da zaman lafiya da kwanciyar hankali.”

 

Bayanin na uwargidan shugaban kasar ya yi daidai da tunanin sauran masu jawabi a wurin taron, ciki har da Darakta Janar na cibiyar, Misis Asabe Vilita Bashir, da Sakatariyar Ma’aikatar harkokin mata, Misis Monilola Udoh.

 

Dukkanninsu sun yi murnar yadda mata ke samun tagomashi a gwamnatance a fagen sake gina kasa.

 

A nata jawabin, Dakta Maryam Abacha ta yi addu’a ga kasar nan da kuma wannan gwamnati mai ci a karkashin jagorancin shugaban kasa Bola Tinubu da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima akan Allah ya ba su ikon cimma nasara.

 

Ta ce galibin matan da ke rike da madafun iko a yau suna da ilimi sosai, inda ta shawarce su a kan su yi amfani da damar da suka samu wajen yin ci gaban al’umma.

 

Ta yi fatan cewa uwargidan shugaban kasa, Sanata Oluremi Tinubu za ta yi aiki mai kyau.

 

Ta kuma ba da shawarar cewa ya kamata a karfafa wa dukkan mata gwiwa su zama masu amfani da kuma dacewa wajen ci gaban kasa.

 

“Ina so na roke ku da cewa ka da a bar mace a baya wajen daukar nauyi. Na yi farin ciki da na kasance jigo wajen kafa wannan cibiya kuma ina godiya ga uwargidan shugaban kasa da cibiyar bisa ganin na cancanci a sanya sunana a wannan katafaren gini haka”.

 

“Zan tattaro wasu tattaunawarmu da wasu ayyukanmu a cikin kundi kuma ina ƙarfafa ku da ku zama masu ƙwazo domin a zamaninmu, yawancin mu ba mu kammala karatun digiri ba. Mun yi iya bakin kokarinmu muka bar sauran amma yanzu muna da wadanda suka samu ilimi da wayewa da za su kai ‘yan Nijeriya mafi kyawun wuri ga mata”.

 

Taron ya kasance babban wuri wajen bayyana bayanan zaman lafiya da goyon baya a tsakanin mata.

Remi Tinubu
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
Next Post
Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

‘Yansanda Sun Tabbatar Da Sace Basarake Da Matarsa A Jihar Nasarawa. 

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.