ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Remi Tinubu Ta Sanya Wa Babban Dakin Taron Cibiyar Mata Ta Abuja Sunan Maryam Abacha

by Bello Hamza
3 years ago
Remi Tinubu

Uwargidan shugaban kasa Oluremi Tinubu, ta sauya sunan babban dakin taron ‘Maryam Babangida National Centre for Women Development’ zuwa sunan Dr. Maryam Abacha, matar tsohon shugaban kasa a mulkin soja, marigayi Janaral Sani Abacha.

 

Zauren wanda a da ake kira da ‘African Peace Mission Hall’, uwargidan shugaban kasar ce ta kaddamar da shi kuma aka canza masa suna zuwa Maryam Abacha, saboda irin gudummawar da ta bayar wajen samar da zaman lafiya a nahiyar Afrika.

ADVERTISEMENT
  • Uwargidan Shugaban kasa, Remi Tinubu Ta Ziyarci Buhari A Daura

A jawabinta, uwargidan shugaban kasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta ce taron muhimmi ne a kokarin hadin gwiwa wajen karfafa alaka tare da bunkasa ci gaban da aka samu wajen samun hadin kai da dawwamammen dangantaka a tsakanin mata.

 

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Ta bayyana Maryam Abacha a matsayin mace mai hazaka kuma jajirtacciya wajen ci gaban nahiyar Afrika baki daya.

 

“Shawararta ne ya samar da ma’aikatar harkokin mata ta tarayya tare da nada mace a matsayin minista, wanda hakan ya fadada zuwa jihohi daban-daban tare da girmama al’amuran matan Nijeriya.

 

“A kwanan nan a yayin sauya sunan wannan cibiya, na jaddada wa mata cewa su dinke barakar da ke tsakaninsu, su nuna halaye masu kyau da kuma mayar da hankali fiye da bambance-bambancen da ke tsakaninmu, kasancewar hadin kan mu a matsayin mata ya fi muhimmanci. Wannan taron yana da mahimmanci a yayin da ya zama babban dama na kafa tarihi wajen samar da dawwamammen zaman lafiya a cikin al’ummarmu.

 

“A yayin cimma burinmu, yana da kyau mu fahimta tare da karrama mutanen da suka taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa da zaman lafiya da kwanciyar hankali.”

 

Bayanin na uwargidan shugaban kasar ya yi daidai da tunanin sauran masu jawabi a wurin taron, ciki har da Darakta Janar na cibiyar, Misis Asabe Vilita Bashir, da Sakatariyar Ma’aikatar harkokin mata, Misis Monilola Udoh.

 

Dukkanninsu sun yi murnar yadda mata ke samun tagomashi a gwamnatance a fagen sake gina kasa.

 

A nata jawabin, Dakta Maryam Abacha ta yi addu’a ga kasar nan da kuma wannan gwamnati mai ci a karkashin jagorancin shugaban kasa Bola Tinubu da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima akan Allah ya ba su ikon cimma nasara.

 

Ta ce galibin matan da ke rike da madafun iko a yau suna da ilimi sosai, inda ta shawarce su a kan su yi amfani da damar da suka samu wajen yin ci gaban al’umma.

 

Ta yi fatan cewa uwargidan shugaban kasa, Sanata Oluremi Tinubu za ta yi aiki mai kyau.

 

Ta kuma ba da shawarar cewa ya kamata a karfafa wa dukkan mata gwiwa su zama masu amfani da kuma dacewa wajen ci gaban kasa.

 

“Ina so na roke ku da cewa ka da a bar mace a baya wajen daukar nauyi. Na yi farin ciki da na kasance jigo wajen kafa wannan cibiya kuma ina godiya ga uwargidan shugaban kasa da cibiyar bisa ganin na cancanci a sanya sunana a wannan katafaren gini haka”.

 

“Zan tattaro wasu tattaunawarmu da wasu ayyukanmu a cikin kundi kuma ina ƙarfafa ku da ku zama masu ƙwazo domin a zamaninmu, yawancin mu ba mu kammala karatun digiri ba. Mun yi iya bakin kokarinmu muka bar sauran amma yanzu muna da wadanda suka samu ilimi da wayewa da za su kai ‘yan Nijeriya mafi kyawun wuri ga mata”.

 

Taron ya kasance babban wuri wajen bayyana bayanan zaman lafiya da goyon baya a tsakanin mata.

Remi Tinubu
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Next Post
Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

‘Yansanda Sun Tabbatar Da Sace Basarake Da Matarsa A Jihar Nasarawa. 

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.