ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Remi Tinubu Ta Sanya Wa Babban Dakin Taron Cibiyar Mata Ta Abuja Sunan Maryam Abacha

by Bello Hamza
3 years ago
Remi Tinubu

Uwargidan shugaban kasa Oluremi Tinubu, ta sauya sunan babban dakin taron ‘Maryam Babangida National Centre for Women Development’ zuwa sunan Dr. Maryam Abacha, matar tsohon shugaban kasa a mulkin soja, marigayi Janaral Sani Abacha.

 

Zauren wanda a da ake kira da ‘African Peace Mission Hall’, uwargidan shugaban kasar ce ta kaddamar da shi kuma aka canza masa suna zuwa Maryam Abacha, saboda irin gudummawar da ta bayar wajen samar da zaman lafiya a nahiyar Afrika.

ADVERTISEMENT
  • Uwargidan Shugaban kasa, Remi Tinubu Ta Ziyarci Buhari A Daura

A jawabinta, uwargidan shugaban kasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta ce taron muhimmi ne a kokarin hadin gwiwa wajen karfafa alaka tare da bunkasa ci gaban da aka samu wajen samun hadin kai da dawwamammen dangantaka a tsakanin mata.

 

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Ta bayyana Maryam Abacha a matsayin mace mai hazaka kuma jajirtacciya wajen ci gaban nahiyar Afrika baki daya.

 

“Shawararta ne ya samar da ma’aikatar harkokin mata ta tarayya tare da nada mace a matsayin minista, wanda hakan ya fadada zuwa jihohi daban-daban tare da girmama al’amuran matan Nijeriya.

 

“A kwanan nan a yayin sauya sunan wannan cibiya, na jaddada wa mata cewa su dinke barakar da ke tsakaninsu, su nuna halaye masu kyau da kuma mayar da hankali fiye da bambance-bambancen da ke tsakaninmu, kasancewar hadin kan mu a matsayin mata ya fi muhimmanci. Wannan taron yana da mahimmanci a yayin da ya zama babban dama na kafa tarihi wajen samar da dawwamammen zaman lafiya a cikin al’ummarmu.

 

“A yayin cimma burinmu, yana da kyau mu fahimta tare da karrama mutanen da suka taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa da zaman lafiya da kwanciyar hankali.”

 

Bayanin na uwargidan shugaban kasar ya yi daidai da tunanin sauran masu jawabi a wurin taron, ciki har da Darakta Janar na cibiyar, Misis Asabe Vilita Bashir, da Sakatariyar Ma’aikatar harkokin mata, Misis Monilola Udoh.

 

Dukkanninsu sun yi murnar yadda mata ke samun tagomashi a gwamnatance a fagen sake gina kasa.

 

A nata jawabin, Dakta Maryam Abacha ta yi addu’a ga kasar nan da kuma wannan gwamnati mai ci a karkashin jagorancin shugaban kasa Bola Tinubu da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima akan Allah ya ba su ikon cimma nasara.

 

Ta ce galibin matan da ke rike da madafun iko a yau suna da ilimi sosai, inda ta shawarce su a kan su yi amfani da damar da suka samu wajen yin ci gaban al’umma.

 

Ta yi fatan cewa uwargidan shugaban kasa, Sanata Oluremi Tinubu za ta yi aiki mai kyau.

 

Ta kuma ba da shawarar cewa ya kamata a karfafa wa dukkan mata gwiwa su zama masu amfani da kuma dacewa wajen ci gaban kasa.

 

“Ina so na roke ku da cewa ka da a bar mace a baya wajen daukar nauyi. Na yi farin ciki da na kasance jigo wajen kafa wannan cibiya kuma ina godiya ga uwargidan shugaban kasa da cibiyar bisa ganin na cancanci a sanya sunana a wannan katafaren gini haka”.

 

“Zan tattaro wasu tattaunawarmu da wasu ayyukanmu a cikin kundi kuma ina ƙarfafa ku da ku zama masu ƙwazo domin a zamaninmu, yawancin mu ba mu kammala karatun digiri ba. Mun yi iya bakin kokarinmu muka bar sauran amma yanzu muna da wadanda suka samu ilimi da wayewa da za su kai ‘yan Nijeriya mafi kyawun wuri ga mata”.

 

Taron ya kasance babban wuri wajen bayyana bayanan zaman lafiya da goyon baya a tsakanin mata.

Remi Tinubu
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

‘Yansanda Sun Tabbatar Da Sace Basarake Da Matarsa A Jihar Nasarawa. 

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.