• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ribadu Zai Shugabanci Taron LEADERSHIP Da NDLEA Kan Yaki Da Miyagun Kwayoyi

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Rahotonni
0
Ribadu Zai Shugabanci Taron LEADERSHIP Da NDLEA Kan Yaki Da Miyagun Kwayoyi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai Bai Wa Shugaban Kasa Shawara kan Harkokin Tsaron Kasa, Malam Nuhu Ribadu ya ba da tabbacin zai halarci babban taron Kamfanin LEADERSHIP na hadin gwiwa da NDLEA kan yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi da sauran miyagun laifuka da rashin tsaro da kuma ci gaban kasa, a matsayin shugaban taron.

Taron mai taken, ‘Shan Miyagan Kwayoyi, Manyan Laifuka, Rashin Tsaro da Ci Gaban Kasa,’ wanda aka tsara gudanarwa a ranar 3 ga Agusta, 2023 a Babbar Cibiyar Taro ta Kasa da Kasa da ke Abuja, wani sabon yunkuri ne na shawo kan yawaitar bazuwar miyagun kwayoyin da ake fama da ita.

  • Yarjejeniyar Saukaka Zuba Jari Za Ta Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya Da Dala Triliyan 1
  • Tinubu Ya Ba Da Umarnin Fitar Da Takin Zamani Da Hatsi Don Rage Radadin Cire Tallafin Fetur

Wata sanarwa da hukumar gudanarwar Rukunan Kamfanonin LEADERSHIP, mai dauke da sa hannun babban edita kuma babban mataimakin shugaban kamfanin, Mista Azu Ishiekwene, ta bayyana cewa kamfanin jaridun tare da hadin gwiwar hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta Nijeriya (NDLEA) sun dauki nauyin gudanar da taron ne, “domin samar da mafita kan matsalar a wannan zamani da ake kara bullo da sabbin fasahohi da hanyoyin safara da rarraba miyagun kwayoyin.”

Ishiekwene ya kara da cewa taron na da nufin tattauna makomar yaki da miyagun kwayoyin ne bisa la’akari da yadda za a yi garambawul ga dokokin Nijeriya game da mallaka, amfani, hukunci, tarbiyyantarwa da kuma sake maido da wadanda kwaya ta tagayyara kan turba mai kyau.

“Kamar yadda binciken da Majalisar Dinkin Duniya ta yi kan amfani da kwayoyi a shekarar 2017, ya bayyana bisa kiyasi na adadin al’ummar Nijeriya miliyan 98, akwai miliyan 14.3 da ke amfani da miyagun kwayoyi.

Labarai Masu Nasaba

Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

“Wadannan alkaluma sun ninninka ba kawai bisa la’akari da karuwar jama’a da kuma yawan kalubalen zamantakewa da tattalin arziki ba, kai har ma da karuwar ta’addanci, fashi da makami, garkuwa da mutane, da sauran munanan laifuka. Wannan abu ne mai ban tsoro kuma yana bukatar gudunmawa ta gaggawa daga dukkan masu ruwa da tsaki a bangaren shugabannin Nijeriya da masu kishin kasa da kuma kamfanoni,” in ji sanarwar.

Ribadu, wanda ya kasance jagoran yaki da cin hanci da rashawa kuma shugaba na farko a hukumar yaki da masu zamba cikin aminci da karya tattalin arzikin kasa (EFCC), zai gabatar da jawabin bude taron a matsayinsa na shugaban taron.

Sanarwar ta kuma yi nuni da cewa, sabon mai ba wa shugaban kasar shawara a kan harkokin tsaron kasa (NSA) da ya zama na farko da aka nada a mukamin ba tare da ya taba yin aikin soja ba, tun bayan komawar mulkin dimokuradiyya a shekarar 1999, zai kara tagomashi kan abubuwan da za a tattauna a taron sakamakon yadda a aikace ya fahimci dabarun tattara bayanan sirri da yaki da laifuffuka a lokacin da yake EFCC har ya yi suna a duniya ta wannan fuskar tare da samun lambobin yabo.

Ta kuma kara da cewa, a bisa la’akari da bukatar gaggauta kawar da barazanar shan muggan kwayoyi da ta’addanci, fashi da makami, da yadda abin ke illata ci gaban kasa, taron na hadin gwiwa tsakanin LEADERSHIP da NDLEA ya kudiri aniyar fayyace sabbin hanyoyin sarrafa kwayoyin, da fataucinsu da rarraba su, da kuma yin tambayoyi kan kokarin da hukumomin da ke sahun gaba a yaki da ta’ammali da miyagun kwayoyin ke yi, tare da sake jaddada kiran shigar al’umma cikin lamarin.

Daga cikin manyan bakin da za su halarci taron akwai wadanda za su zo daga fadar shugaban kasa, majalisar dokoki ta kasa, sojoji, gwamnatocin jihohi, ma’aikatu da hukumomin gwamnati, sarakuna, jami’an diflomasiyya, hukumomin duniya, kamfanoni masu zaman kansu, malamai, kungiyoyi, Ofishin Majalisar Dinkin Duniya Mai Yaki da Miyagun Kwayoyi da Laifuffuka (UNODC), Sakatariyar Tarayyar Afirka da Ofishin Mai Ba Da Shawara Kan Tsaron Kasa (ONSA) da dai sauransu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: LEADERSHIPMiyagun KwayoyiNDLEARahotoRibadu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Atiku Ya Soki Shirin Tinubu Na Bai Wa ‘Yan Nijeriya Tallafin ₦8000

Next Post

Musabbabin Haramta Sana’ar Gwangwan A Jihar Borno

Related

Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa
Rahotonni

Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa

6 days ago
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya
Rahotonni

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

6 days ago
Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda
Rahotonni

Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

7 days ago
Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

4 weeks ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

4 weeks ago
Fyade
Rahotonni

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

1 month ago
Next Post
Musabbabin Haramta Sana’ar Gwangwan A Jihar Borno

Musabbabin Haramta Sana'ar Gwangwan A Jihar Borno

LABARAI MASU NASABA

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

August 21, 2025
Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

August 21, 2025
Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

August 21, 2025
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

August 21, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

August 21, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

August 21, 2025
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

August 21, 2025
Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.