• English
  • Business News
Thursday, September 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ribadu Zai Shugabanci Taron LEADERSHIP Da NDLEA Kan Yaki Da Miyagun Kwayoyi

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Rahotonni
0
Ribadu Zai Shugabanci Taron LEADERSHIP Da NDLEA Kan Yaki Da Miyagun Kwayoyi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai Bai Wa Shugaban Kasa Shawara kan Harkokin Tsaron Kasa, Malam Nuhu Ribadu ya ba da tabbacin zai halarci babban taron Kamfanin LEADERSHIP na hadin gwiwa da NDLEA kan yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi da sauran miyagun laifuka da rashin tsaro da kuma ci gaban kasa, a matsayin shugaban taron.

Taron mai taken, ‘Shan Miyagan Kwayoyi, Manyan Laifuka, Rashin Tsaro da Ci Gaban Kasa,’ wanda aka tsara gudanarwa a ranar 3 ga Agusta, 2023 a Babbar Cibiyar Taro ta Kasa da Kasa da ke Abuja, wani sabon yunkuri ne na shawo kan yawaitar bazuwar miyagun kwayoyin da ake fama da ita.

  • Yarjejeniyar Saukaka Zuba Jari Za Ta Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya Da Dala Triliyan 1
  • Tinubu Ya Ba Da Umarnin Fitar Da Takin Zamani Da Hatsi Don Rage Radadin Cire Tallafin Fetur

Wata sanarwa da hukumar gudanarwar Rukunan Kamfanonin LEADERSHIP, mai dauke da sa hannun babban edita kuma babban mataimakin shugaban kamfanin, Mista Azu Ishiekwene, ta bayyana cewa kamfanin jaridun tare da hadin gwiwar hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta Nijeriya (NDLEA) sun dauki nauyin gudanar da taron ne, “domin samar da mafita kan matsalar a wannan zamani da ake kara bullo da sabbin fasahohi da hanyoyin safara da rarraba miyagun kwayoyin.”

Ishiekwene ya kara da cewa taron na da nufin tattauna makomar yaki da miyagun kwayoyin ne bisa la’akari da yadda za a yi garambawul ga dokokin Nijeriya game da mallaka, amfani, hukunci, tarbiyyantarwa da kuma sake maido da wadanda kwaya ta tagayyara kan turba mai kyau.

“Kamar yadda binciken da Majalisar Dinkin Duniya ta yi kan amfani da kwayoyi a shekarar 2017, ya bayyana bisa kiyasi na adadin al’ummar Nijeriya miliyan 98, akwai miliyan 14.3 da ke amfani da miyagun kwayoyi.

Labarai Masu Nasaba

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

“Wadannan alkaluma sun ninninka ba kawai bisa la’akari da karuwar jama’a da kuma yawan kalubalen zamantakewa da tattalin arziki ba, kai har ma da karuwar ta’addanci, fashi da makami, garkuwa da mutane, da sauran munanan laifuka. Wannan abu ne mai ban tsoro kuma yana bukatar gudunmawa ta gaggawa daga dukkan masu ruwa da tsaki a bangaren shugabannin Nijeriya da masu kishin kasa da kuma kamfanoni,” in ji sanarwar.

Ribadu, wanda ya kasance jagoran yaki da cin hanci da rashawa kuma shugaba na farko a hukumar yaki da masu zamba cikin aminci da karya tattalin arzikin kasa (EFCC), zai gabatar da jawabin bude taron a matsayinsa na shugaban taron.

Sanarwar ta kuma yi nuni da cewa, sabon mai ba wa shugaban kasar shawara a kan harkokin tsaron kasa (NSA) da ya zama na farko da aka nada a mukamin ba tare da ya taba yin aikin soja ba, tun bayan komawar mulkin dimokuradiyya a shekarar 1999, zai kara tagomashi kan abubuwan da za a tattauna a taron sakamakon yadda a aikace ya fahimci dabarun tattara bayanan sirri da yaki da laifuffuka a lokacin da yake EFCC har ya yi suna a duniya ta wannan fuskar tare da samun lambobin yabo.

Ta kuma kara da cewa, a bisa la’akari da bukatar gaggauta kawar da barazanar shan muggan kwayoyi da ta’addanci, fashi da makami, da yadda abin ke illata ci gaban kasa, taron na hadin gwiwa tsakanin LEADERSHIP da NDLEA ya kudiri aniyar fayyace sabbin hanyoyin sarrafa kwayoyin, da fataucinsu da rarraba su, da kuma yin tambayoyi kan kokarin da hukumomin da ke sahun gaba a yaki da ta’ammali da miyagun kwayoyin ke yi, tare da sake jaddada kiran shigar al’umma cikin lamarin.

Daga cikin manyan bakin da za su halarci taron akwai wadanda za su zo daga fadar shugaban kasa, majalisar dokoki ta kasa, sojoji, gwamnatocin jihohi, ma’aikatu da hukumomin gwamnati, sarakuna, jami’an diflomasiyya, hukumomin duniya, kamfanoni masu zaman kansu, malamai, kungiyoyi, Ofishin Majalisar Dinkin Duniya Mai Yaki da Miyagun Kwayoyi da Laifuffuka (UNODC), Sakatariyar Tarayyar Afirka da Ofishin Mai Ba Da Shawara Kan Tsaron Kasa (ONSA) da dai sauransu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: LEADERSHIPMiyagun KwayoyiNDLEARahotoRibadu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Atiku Ya Soki Shirin Tinubu Na Bai Wa ‘Yan Nijeriya Tallafin ₦8000

Next Post

Musabbabin Haramta Sana’ar Gwangwan A Jihar Borno

Related

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

3 days ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

4 days ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

6 days ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

2 weeks ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

2 weeks ago
Akwai Bukatar Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Jihar Legas Wajen Bunkasa Albarkatun Fatu
Rahotonni

Akwai Bukatar Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Jihar Legas Wajen Bunkasa Albarkatun Fatu

2 weeks ago
Next Post
Musabbabin Haramta Sana’ar Gwangwan A Jihar Borno

Musabbabin Haramta Sana'ar Gwangwan A Jihar Borno

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

Cutar Diphtheria Ta Kashe Yara 10 A Jihar Neja

September 11, 2025
DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

September 11, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

‘Yansanda Sun Cafke ‘Yan Fashi 3 A Kano, Sun Ƙwato Motar Sata

September 11, 2025
Ganawata Da Macron Ta Yi Amfani – Tinubu

Ganawata Da Macron Ta Yi Amfani – Tinubu

September 11, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Tinubu Ya Bayar Da Umarni Karya Farashin Kayan Abinci A Nijeriya

September 11, 2025
Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL

Mele Kyari Ya Bayyana A Ofishin EFCC Kan Zargin Badaƙalar Dala Biliyan 7.2

September 11, 2025
Amfani Da Karfin Tuwo Ba Zai Iya Kawo Zaman Lafiya A Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Amfani Da Karfin Tuwo Ba Zai Iya Kawo Zaman Lafiya A Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

September 10, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Mizanin Cinikayya Tare Da Sauran Mambobin BRICS

Kasar Sin Ta Fitar Da Mizanin Cinikayya Tare Da Sauran Mambobin BRICS

September 10, 2025
Mataimakin Shugaban Unilever: Mun Kudiri Aniyar Zama “Masu Tseren Gudun Fanfalaki” A Kasar Sin

Mataimakin Shugaban Unilever: Mun Kudiri Aniyar Zama “Masu Tseren Gudun Fanfalaki” A Kasar Sin

September 10, 2025
Shettima Ya Yaba Wa Uba Sani Kan Kafa Majalisar Ƙwarewa Ta Jihar Kaduna

Shettima Ya Yaba Wa Uba Sani Kan Kafa Majalisar Ƙwarewa Ta Jihar Kaduna

September 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.