• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ribas: Ƙungiyar Ƙwadago Na Barazanar Shiga Yajin Aiki In Har Ba A Janye Dokar Ta-ɓaci Ba

by Abubakar Sulaiman
5 months ago
in Labarai
0
NLC Za Ta Yi Zama Kan Hana Wasu Ma’aikatan Kano Albashi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar kwadago ta yi gargadin cewa za a iya tilasta mata daukar matakan da za su iya kawo cikas ga ayyukan tattalin arzikin kasa nan, wanda ta yi barazanar shiga yajin aiki matukar ba a janye dokar ta-ɓaci a da kakaba a Jihar Ribas cikin gaggawa.

kungiyar ta dai fitar da barazanar ce a cikin wata sanarwa da shugabanta na Jihar Ribas, Aled Agwanwor da shugaban kungiyar ‘yan kasuwa ta jihar, TUC, Ikechukwu Onyefuru da shugaban majalisar tattaunawa ta hadin gwiwa (JNC), Chuku Emecheta.

  • ‘Yansanda Sun Hana Hawan Sallah A Kano Saboda Tsaro
  • Yadda Ake Fitar Da Zakkar Fidda Kai Da Sallar Idi

kungiyoyin kwadago sun nuna damuwarsu game da shari’a da tasirin tattalin arziki da kuma ayyana dokar ta-ɓaci ta Shugaba Bola Tinubu ya kakaba a Jihar Ribas.

Sun bayyana cewa ayyana dokar ta-vaci da kuma dakatar da zavavven gwamna, Siminalayi Fubara da mataimakiyarsa, Ngozi Odu da mambobin majalisar jihar a matsayin wanda ya sava dokan kundin tsarin mulkin Nijeriya.

Shugabannin kwadago sun dage cewa mutanen Jihar Ribas sun zavi wadannan jami’an ne cikin ‘yanci, kuma duk wani yunkuri na cire su da ya sava wa kundin tsarin mulki yana lalata dimokuraɗiyya.

Labarai Masu Nasaba

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

A cewar shugabannin Ƙwadago, dole ne a sauya irin wadannan lamari don kare mutuncin tsarin dimokuradiyya a Nijeriya.

Sun jaddada wahalar da dokar ta-ɓaci ta haifar wa ma’aikatan kananan hukumomi, da yawa daga cikinsu har yanzu ba su karɓi albashinsu ba.

Sanarwar ta lura cewa hana albashin ma’aikata ya jefa su cikin matsin tattalin arziki, musamman ma a irin wannan lokaci da ake samun tsadar rayuwa a cikin kasar nan.

Ƙungiyar Ƙwadago ta yi gargadin cewa dokar ta-vaci na iya haifar da mummunan sakamako na tattalin arziki, tana mai jaddada muhimmancin da Jihar Ribas ke da ita ga tattalin arzikin Nijeriya da yankin Neja Delta gaba daya.

Ta ce da ma can kasar nan ta riga ta fuskanci hauhawar farashi, raguwar darajar naira, tsadar musayar canji, rashin aikin yi da tsadar rayuwa, rashin kwanciyar hankali a Jihar Ribas na iya kara ta’azzara halin da ake ciki a duk fadin kasar nan.

Sanarwar ta kuma nuna cewa rashin tabbas na siyasa da dokar ta-ɓaci ta haifar ya kori masu saka hannun jari wadanda suka nuna sha’awar zuba hannun jari a tattalin arzikin jihar.

“Wannan asarar saka hannun jari yana lalata kudaden shiga na cikin gida na jihar (IGR), kuma zai yi tasiri na dogon lokaci a ci gaban tattalin arziki da kuma damar samar da ayyukan yi a yankin.

“Duk da cewa mun amince da bukatar kiyaye doka da oda, dole ne a aiwatar da irin wadannan matakai a cikin tsarin kundin tsarin mulkin Nijeriya.

Dakatar da zaɓaɓɓun jami’ai da lalata tsarin biyan albashin ma’aikata ya keta hakkoki dan’adam wanda zai iya ta’azzara rashin tsaro da kalubalen tattalin arziki.

“Ya kamata gwamnatin tarayya ta ba da fifiko ga tsaro da jin dadin ‘yan kasa a kan muradun siyasa.

“Duk wata hanyar mulki da ke sadaukar da jin dadin ma’aikata don ayyukan siyasa zai kara tashin hankali da rashin kwanciyar hankali ga al’umma,” in ji ƙungiyar ƙwadago.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dokar Ta-ɓaciƘungiyar ƘwadagoRibas
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwarewar Kasar Sin Da Ci Gabanta A Fannin Fasaha Na Da Muhimmanci Wajen Inganta Zamanantar Da Afirka

Next Post

Kasar Sin Za Ta Zage Damtsen Kawo Sauye-sauyen Zamani A Masana’antar Kananan Kayayyaki

Related

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya
Labarai

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

7 hours ago
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi
Labarai

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

8 hours ago
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa
Labarai

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

8 hours ago
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba
Labarai

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

9 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

12 hours ago
Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 
Labarai

Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

12 hours ago
Next Post
Kasar Sin Za Ta Zage Damtsen Kawo Sauye-sauyen Zamani A Masana’antar Kananan Kayayyaki

Kasar Sin Za Ta Zage Damtsen Kawo Sauye-sauyen Zamani A Masana’antar Kananan Kayayyaki

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.