ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikici Ya Barke Kan Zaben Kananan Hukumomin Jihar Neja

by Muhammad Awwal Umar
4 years ago
Rikici

Tun bayan da hukumar zabe ta Jihar Neja (NSIEC) ta fitar da jadawalin zabukan kananan hukumomin Neja aka fara tayar da jijiyoyin wuya tsakanin gamayyar jam’iyyun siyasa da majalisar dokokin jihar. 

Kamar yadda hukumar zaben NSIEC ta fitar jadawalin zaben zai kasance ne farkon watan Nuwanba, wata uku kafin babban zaben 2023.

  • Shugaba Buhari Zai Kawo Karshen Rashin Tsaro A Nijeriya -Buratai
  • Ziyarar Babbar jami’ar Lithuania A Taiwan Shirme Ne

Wanda jadawalin zaben bai yi wa wasu ‘yan siyasa dadi ba, inda aka rika shirya taruka kan kiran gwamnatin jiha ta janye kudurinta na zaben a daidai wannan lokacin.

ADVERTISEMENT

Dan majalisar jiha mai wakiltar karamar hukumar Bosso, Hon. Malik Madawaki Bosso ya gabatar da kuduri ga majalisar, inda ya nemi majalisar da dakatar da hukumar zaben ta jiha kan zaben bisa wasu dalilan doka.

Da yake bayyana matsayar majalisar, shugaban majalisar dokokin jihar, Rt. Hon. Abdullahi Bawa Wuse, ya nemi gwamnatin jiha da ta dakatar da hukumar zaben na kudurin gudanar da zaben wanda ya zo daidai da sashe na ashirin (20) na dokar zaben kananan hukumomi na shekarar 2002 da sashe na ashirin da tara (29) (1) na dokar zabe na 2022.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Kudurin da dan majalisar Madawaki ya gabatar ya ce wa’adin shugabannin kananan hukumomi zai kare ne ranar 12 ga watan Disambar wannan shekarar.

Dan majalisar ya ce jadawalin zaben da hukumar zaben ta jiha ta fitar domin fara shirye-shiryen zaben kananan hukumomi a jihar, wanda ta tsara zaben fitar da gwani zai kasance tsakanin ranar 20 zuwa 27 ga watan Agusta, inda kuma ta ce za a gudanar da zaben ranar 5 ga watan Nuwamba ya saba wa dokar zaben jiha.

Ya kara da cewar tsakanin ranar 27 ga watan Agusta zuwa 5 ga watan Nuwamba kwana 35 ne, ya ce dokar ta tanadi cewa tsakanin zaben fid da gwani da babban zabe kwanaki dari da tamanin (180) ne.

Dan majalisar ya ce dokar da ta samar da matsayin kananan hukumomi na 2002, ita ce ta haifar da dokokin zaben 2022 da majalisar dokokin jiha ta gabatar kuma ya zama dokar zabe kananan hukumomi a Jihar Neja da wadda aka gabatar a shekarar 2002 da ta 2001.

Madaki ya ce sashi na ashirin (20) na dokokin zaben kananan hukumomi na 2002, ya bayyana za a samar da shugabannin kananan hukumomi ne bisa tsarin zabe da kuma tabbatar da cewar an bi tsarin doka kamar yadda sashi na sha tara (19) ya tanada.

Ya kara da cewar sashi na 29 sakin layi na daya na dokar zabe 2002, ya ce ba wata jam’iyyar siyasa za ta shiga zabe kasa da kwanaki 180 tsakanin zaben fid da gwani da babban zabe, sai sun mayar wa hukumar zabe sunayen wadanda suka samu nasarar zaben fid da gwani.

Ya ce a bayyana take cewar NSIEC za ta gudanar da zaben ba bisa doka ba idan ta ci gaba da shirya yunkurin gudanar da zaben a wannan lokacin kamar yadda ta fitar da jadawalin zaben.

Da yake amsa tambayoyin manema labarai, shugaban gamayyar jam’iyyun siyasa sha takwas “IPAC” da ke yunkurin shiga zaben, Malam Muhammad Bello Maikujeri, ya ce ‘muna nan kan matsayanmu na shiga zaben kamar yadda NSIEC ta fitar jadawalin zaben.’

Ya ci gaba da cewa majalisar ce ta yi sabon kudurin da ya bai wa shugabannin kananan hukumomi wa’adin shekaru uku kan karagar mulki, sanin kowa ne shugabannin kananan hukumomi na yin wa’adin shekaru biyu ne, amma bayan wannan dokar kotu ta tabbatar wa shugabannin kananan hukumomi wa’adin shekaru ukun, kuma wa’adin mulkinsu zai kare ne a ranar 12 ga watan Disamba.

Ya ce, “Saboda haka daga ranar 12 ga watan Disamba dole ne su sauka, amma ita majalisar dokokin jiha da ke tayar da jijiyoyin wuya ta manta cewa ita ce ta yi dokar, kuma a sabon dokar da muke amfani da shi da ya bai wa shugabannin kananan hukumomi wa’adin shekaru uku, ba ta bayyana gwamnatin rikon kwarya ba. “Idan ta natsu da kyau, hukumar zabe ta NSIEC ta yi abin da ya dace, domin ba zababbiyar gwamnatin karamar hukuma da za ta mika mulki hannun wani kantoma ko rikon kwarya bisa yadda suka tsara dokar.

“Saboda haka, wannan ba hurumin majalisar dokokin jiha ba ne, kotu ce kawai za ta iya warware abin da sabon dokar ya kunsa.

Mu IPAC, mun gamsu kuma mun amince jam’iyyu su ci gaba da shirye-shiryen zaben kananan hukumomi, domin muna magana ne a kan doka ba ra’ayin wani ba.

“Dokar zaben Jihar Neja ba ta samar da wani sashen rikon kwarya ko mika mulki ga wani a karamar hukuma ba, sai dai zababben shugaba. A yau mun ziyarci shugaban hukumar zabe ta Jiha Neja (NSIEC), Alhaji Aminu Baba domin bayyana masa matsayin IPAC a kan wannan takaddamar, mun tsaya ne a kan shiga zabe, kuma mun umurci sauran jam’iyyu su ci gaba da shirye-shiryen fuskar zaben kananan hukumomi na ranar 5 ga watan Nuwamba kamar yadda jadawalin NSIEC ta tsara.

Rikici
Muhammad Awwal Umar
+ postsBio
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Yadda Mayar Da Gonaki Fulotai Ke Tsananta Karancin Abinci
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Gwamnatoci Sun Fara Daukar Matakan Dakile Yunwa
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Neja Za Ta Gyara Makarantun Rugagen Fulani
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Ba Mu Hana Sulhu Da ‘Yan Ta’adda Ba, Amma A Bar Jami’an Tsaro Su Yi Aikinsu – Bosso

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Ko Makiyan Buhari Sun San Aikin Da Ya Yi Yafi Na Gwamnatocin Baya -Minista

Ko Makiyan Buhari Sun San Aikin Da Ya Yi Yafi Na Gwamnatocin Baya -Minista

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.