Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Iyaka: Buhari Ya Bukaci Al’ummu Su Hada Kai Da Hukumomin Jami’ar FUTO

by
2 years ago
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Shugaba Muhammadu Buhari, ya yi roko ga al’ummomin da suke kewaye da Jami’ar gwamnatin tarayya ta Kimiyya da Fasaha da ke Owerri (FUTO), da su bayar da cikakken hadin kai tare da shugabannin Jami’ar, yana mai cewa rikicin filaye da ya ki ci ya ki cinyewa a tsakanin Jami’ar da al’ummun  da suke kewaye da ita sam ba zai haifar da da mai ido ba ga bunkasar Jami’ar.

Buhari ya yi wannan jawabin ne a bukin saukan karatu na 32 da Jami’ar ta yi, ya nemi al’ummun da su dauki kasantuwar Jami’ar a tsakanin su a matsayin wata albarka a kusancin na su da hukumomin Jami’ar domin su taimaka wa fadada da ci gaban ta.

Shugaban kasan wanda karamin Minista a ma’aiakatar Ilimi, Emeka Nwajuba, ya wakilce shi cewa ya yi, ba wai gazawa ce a bangaren gwamnatin tarayya a kan matakin da ta dauka na kin karbe filayen da karfin tsiya, saboda ta hanyar kalal ne gwamnatin ta mallaki filayen, amma a maimakon hakan sai ta zabi hanyar sasantawa da lalama a matsayin hanyar warware rikicin.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Fille Kan Wani Dan Majalisa A Jihar Anambra

’Yan Bindigar Da Suka Sace Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Nasarawa Sun Sako Shi

Shugaban kasan ya ce, gwamnatin tarayya a karkashin hukumar kula da zaizayar kasa ta amince da farfado da duk wuraren da zaizayar kasar ta lalata a gefen kogin Otamiri da sassan gadar jami’ar, ya kara da cewa gidauniyar kula da ilimin manyan makarantu (TETFUND), ta bayar da aikin ginawa da kuma bincike a sassan.

Ya kuma bukaci hukumomin Jami’ar da su tabbatar da suna kulawa da yanda ayyukan suke tafiya, ya karfafa cewa, gwamnati ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen tabbatar da zaman lafiya da kuma ci gaban karatu ta hanyar kungiyoyi da sauran masu ruwa da tsaki ta yanda za a sami ingantaccen Ilimi.

Gwamnan Jihar ta Imo, Emeka Ihedioha, ya yaba wa Shugaban kasa Buhari, a kan irin goyon bayan da yake baiwa Jami’ar, sannan ya kwatanta Jami’ar a matsayin babbar cibiyar ilimin da suke tinkaho da ita.

 

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Yaki da Cin Hanci; Kungiyar MURIC Ta Yaba Wa Matakan Shugaba Buhari

Next Post

Tsarin Albashin IPPIS: Gwamnatin Tarayya Ba Za Ta Bi Umurnin Kotu Ba – ASUU

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Fille Kan Wani Dan Majalisa A Jihar Anambra

‘Yan Bindiga Sun Fille Kan Wani Dan Majalisa A Jihar Anambra

by Abubakar Abba
25 mins ago
0

...

’Yan Bindigar Da Suka Sace Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Nasarawa Sun Sako Shi

’Yan Bindigar Da Suka Sace Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Nasarawa Sun Sako Shi

by Leadership Hausa
2 hours ago
0

...

Wani Bene Ya Kuma Ruftawa Ya Danne Mutane A Legas

Wani Bene Ya Kuma Ruftawa Ya Danne Mutane A Legas

by Leadership Hausa
2 hours ago
0

...

 ‘Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 360 Da Sace 1,389 Cikin Watanni 3 A Kaduna

 ‘Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 360 Da Sace 1,389 Cikin Watanni 3 A Kaduna

by Muhammad Bashir
3 hours ago
0

...

Next Post
A Shirye Mu Ke Mu Tattauna Da Gwamnatin Tarayya –Kungiyar ASUU   

Tsarin Albashin IPPIS: Gwamnatin Tarayya Ba Za Ta Bi Umurnin Kotu Ba – ASUU

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: