• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Kabilanci: An Gudanar Da Taron Yafe Wa Juna A Jihar Filato

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Rikicin Kabilanci: An Gudanar Da Taron Yafe Wa Juna A Jihar Filato
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Filato ta jagoranci wani gagarumin taro a birnin Jos domin yafe wa juna da kuma sasanta al’ummar jihar da rikicin kabilanci da Addini ya raba kawunansu.

Wannan biki ya gudana ne a karkashin jagorancin gwamnan jihar, Simon Bako Lalong wanda ya samu halartar Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar II da Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero da shugaban mabiya darikar Katolika na Nijeriya, Arch Bishop John Onayekan da ya samu wakilcin Arch Bishop Ignatius Kaigama.

  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Kai Zuciya Nesa Game Da Batun Kumbon Farar Hula Da Ta Harbo
  • Zan Tabbatar Da An Ci Gajiyar Man Fetur A Yankin Bauchi Da Gombe Muddin Aka Zabe Ni – Atiku

Yayin gudanar da jawabinsa, gwamna Lalong wanda ya bayyana farin cikinsa da yadda jama’a suka amsa kiran da ya musu, ya ce sun yi nasarar kafa ginshikin zaman lafiya da adalci da mutunta juna da kuma karbar baki.

Lalong, ya ce da taimakon sarakunan gargajiya da limaman Addinai da shugabannin al’umma, gwamnatinsa ta yi aiki tukuru wajen sake fasalin jihar da kuma hada kan jama’a.

Gwamnan, ya ce kokarin da suka yi, ya taimaka wajen kawar da tsoro da rashin amincewa juna da kuma kyamar da ake samu a tsakanin jama’ar jihar da suka fito daga kabilu daban-daban

Labarai Masu Nasaba

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

Lalong ya bukaci jama’ar Jihar Filato da su rungumi shirin yafe wa juna da kuma hadin kai, yayin da shi ma ya nemi gafarar jama’ar da suke zaton ya saba musu.

Yayin jawabinsa, Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Saad Abubakar, ya jinjina wa gwamnatin Jihar Filato saboda jajircewar da ta yi wajen ganin ta tabbatar da dorewar zaman lafiya, musamman ganin yadda zaman lafiya da walwala ke dawowa a tsakanin al’umma.

Sarkin Musulmin ya ce babu dalilin da zai sa bayan an kwashe shekaru aru-aru ana zaman lafiya a Jihar, a ce kuma yanzu wasu ‘yan tsiraru za su hana zaman lafiya, yayin da ya gargadi jama’a da su daina barin bata gari suna tunzira su domin tashin hankali ba.

A nashi jawabin, Arch Bishop Ignatius Kaigama, shugaban mabiya darikar Katolika ya bayyana farin cikinsa cewar kokarin da suka yi a Filato na tabbatar da zaman lafiya ya kankama, sakamakon rawar da gwamnatin jihar ta taka.

Shugaban sarakunan Jihar Filato, Gbong Gwom Jos, Jacob Gyang Buba, ya bayyana taron a matsayin mai dimbin tarihi, saboda yadda ya tabbatar da aniyar Gwamna Lalong na janyo hankalin jama’ar jihar domin watsi da matsalolin da aka samu a baya dan rungumar zaman lafiya.

Cikin wadanda suka halarci bikin har da tsofaffin gwamnonin Jihar, Janar Lawrence Onoja mai ritaya da Sir Fidelis Tapgun.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Jihar FilatoJosLalongRikicin KabilanciSarkin KanoSarkin MusulmiTaron Yafiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotun Koli Ta Dakatar Da Daina Amfani Da Tsofaffin Kudi Na Wucin Gadi

Next Post

2023: Mun Fara Horas Da Ma’aikatan Wucin-gadi Miliyan 1.2 – INEC

Related

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

2 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

3 hours ago
UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

11 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

17 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

22 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

1 day ago
Next Post
2023: Mun Fara Horas Da Ma’aikatan Wucin-gadi Miliyan 1.2 – INEC

2023: Mun Fara Horas Da Ma'aikatan Wucin-gadi Miliyan 1.2 - INEC

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.