• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Kabilanci: An Gudanar Da Taron Yafe Wa Juna A Jihar Filato

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Rikicin Kabilanci: An Gudanar Da Taron Yafe Wa Juna A Jihar Filato
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Filato ta jagoranci wani gagarumin taro a birnin Jos domin yafe wa juna da kuma sasanta al’ummar jihar da rikicin kabilanci da Addini ya raba kawunansu.

Wannan biki ya gudana ne a karkashin jagorancin gwamnan jihar, Simon Bako Lalong wanda ya samu halartar Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar II da Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero da shugaban mabiya darikar Katolika na Nijeriya, Arch Bishop John Onayekan da ya samu wakilcin Arch Bishop Ignatius Kaigama.

  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Kai Zuciya Nesa Game Da Batun Kumbon Farar Hula Da Ta Harbo
  • Zan Tabbatar Da An Ci Gajiyar Man Fetur A Yankin Bauchi Da Gombe Muddin Aka Zabe Ni – Atiku

Yayin gudanar da jawabinsa, gwamna Lalong wanda ya bayyana farin cikinsa da yadda jama’a suka amsa kiran da ya musu, ya ce sun yi nasarar kafa ginshikin zaman lafiya da adalci da mutunta juna da kuma karbar baki.

Lalong, ya ce da taimakon sarakunan gargajiya da limaman Addinai da shugabannin al’umma, gwamnatinsa ta yi aiki tukuru wajen sake fasalin jihar da kuma hada kan jama’a.

Gwamnan, ya ce kokarin da suka yi, ya taimaka wajen kawar da tsoro da rashin amincewa juna da kuma kyamar da ake samu a tsakanin jama’ar jihar da suka fito daga kabilu daban-daban

Labarai Masu Nasaba

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

Lalong ya bukaci jama’ar Jihar Filato da su rungumi shirin yafe wa juna da kuma hadin kai, yayin da shi ma ya nemi gafarar jama’ar da suke zaton ya saba musu.

Yayin jawabinsa, Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Saad Abubakar, ya jinjina wa gwamnatin Jihar Filato saboda jajircewar da ta yi wajen ganin ta tabbatar da dorewar zaman lafiya, musamman ganin yadda zaman lafiya da walwala ke dawowa a tsakanin al’umma.

Sarkin Musulmin ya ce babu dalilin da zai sa bayan an kwashe shekaru aru-aru ana zaman lafiya a Jihar, a ce kuma yanzu wasu ‘yan tsiraru za su hana zaman lafiya, yayin da ya gargadi jama’a da su daina barin bata gari suna tunzira su domin tashin hankali ba.

A nashi jawabin, Arch Bishop Ignatius Kaigama, shugaban mabiya darikar Katolika ya bayyana farin cikinsa cewar kokarin da suka yi a Filato na tabbatar da zaman lafiya ya kankama, sakamakon rawar da gwamnatin jihar ta taka.

Shugaban sarakunan Jihar Filato, Gbong Gwom Jos, Jacob Gyang Buba, ya bayyana taron a matsayin mai dimbin tarihi, saboda yadda ya tabbatar da aniyar Gwamna Lalong na janyo hankalin jama’ar jihar domin watsi da matsalolin da aka samu a baya dan rungumar zaman lafiya.

Cikin wadanda suka halarci bikin har da tsofaffin gwamnonin Jihar, Janar Lawrence Onoja mai ritaya da Sir Fidelis Tapgun.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Jihar FilatoJosLalongRikicin KabilanciSarkin KanoSarkin MusulmiTaron Yafiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotun Koli Ta Dakatar Da Daina Amfani Da Tsofaffin Kudi Na Wucin Gadi

Next Post

2023: Mun Fara Horas Da Ma’aikatan Wucin-gadi Miliyan 1.2 – INEC

Related

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

3 hours ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

7 hours ago
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

11 hours ago
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

11 hours ago
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

12 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

15 hours ago
Next Post
2023: Mun Fara Horas Da Ma’aikatan Wucin-gadi Miliyan 1.2 – INEC

2023: Mun Fara Horas Da Ma'aikatan Wucin-gadi Miliyan 1.2 - INEC

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.