• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Sarautar Kano: Yadda Gwamnatin Abba Ta Sauya Alkibla

byYusuf Shuaibu and Abubakar Sulaiman
1 year ago
Sarauta

A wani lamari na sauya sabon salo dangane da rikicin sarautar Kano, Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya sake maido da masarautu uku daga cikin hudu da ya rushe.

A rana daya Majalisar Dokokin Kano ta gabatar da kudirin samar da dokar kirkirar masauratun masu daraja ta biyu, aka yi mata karatun da ya kamata, aka zartar da dokar, sannan aka kai wa gwamna kuma ya rattaba mata hannu da yammacin ranar Talata.

Bayan gwamna ya rattaba wa dokar hannu, nan take kuma ya amince da nadin sabbin sarakuna masu daraja ta biyu da suka hada da masarautun Gaya, Rano da Karaye. Gwamnan ya nada Alhaji Muhammad Mahraz Karaye, a matsayin Sarkin Karaye, wanda kafin nadinsa shi ne Hakimin Rogo.

Sai kuma Alhaji Muhammad Isa Umar, a matsayin Sarkin Rano, wanda kafin nadinsa shi ne Hakimin Bunkure, sannan kuma Alhaji Aliyu Ibrahim Abdulkadir Gaya, a matsayin Sarkin Gaya, wanda shi ne tsohon Sarkin Gaya.

Wannan mataki na gwamnatin Jihar Kano ya zama wani sabon salo, domin a lokacin da ake tsaka da ce-ce-ku-ce a gaban kotuna daban-daban kan rikicin masarautun na Kano, an ji yadda wasu kotunan suka tabbatar da dakatar da Sarki Muhammadu Sanusi II da kotunan gwamnatin tarraya suka zartar tare da cin tarar gwamnatin Kano na naira miliyon 10. Haka itama wata kotu a Jihar Kano karkashin Mai Shari’a Amina ta tabbatar da haramta wa Sarki Aminu Ado da sauran sarakuna uku ayyana kansu a matsayin sarakuna.

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Daular Borno Da Sarakunanta (3)

Tsofaffin Ɗaliban BUK Sun Yaba Wa Masarautar Hausawan Turai Kan Naɗa Ma’ajin Hausawan Turai

Ana tsaka da wannan danbarwa ne sai kuma a ranar Talata da ta gabta, bayan dawowar majalisar dokokin Jihar Kano daga hutun sama da kwanaki 40, inda majalisar ta fara da wani kudiri da aka bukaci samar da dokar kirkirar masauratu masu daraja ta biyu, aka kuma amince tare da mika kunshin dokar, inda gwamnan ya rattaba mata hannu a lokaci guda kuma ya amince tare da nada sabbin sarakuna uku masu daraja ta biyu wadda a wannan rana aka mika masu takardun kama aiki

Wannan sabon mataki na gwamnatin Kano kan sarkakkiyar da ta dabaibaye masarautun Kano na nuni da cewa ga dukkan alamu sarakuna biyu uwa daya uba daya, Alhaji Aminu Ado Bayero da dan’uwansa, Alhaji Nasiru Ado Bayero na alamta cewar an tsame su daga cikin jerin sarakunan da ake magana akansu, musamman Masarautar Bichi wadda babu ita baki daya daga cikin sabuwar dokar.

Shi dai tsohon sarkin Gaya mai daraja ta daya, wanda yanzu kuma aka sake mayar da shi a matsayin sarkin na Gaya, amma a wannan karon mai daraja ta biyu, Alhaji Aliyu Ibrahim Abdulkadir ya rabauta da sake darewa kan karagar sarautar ta Gaya, sakamakon matakin da ya dauka tun a lokacin da Gwamnatin Abba ta sanar da sauke su, inda shi kadai ne wanda ya fito fili ya karbi wancan kaddarar, kila hakan tasa gwamna ya sake aminta da nadisa a matsayin sabon Sarkin Gaya a wani salo na saka masa bisa karbar hukumcin da gwamnati ta yanke a kansu tun da farko.

Sai dai kuma wadannan sabbin sarakuna masu daraja ta biyu an sare masu fika-fikai, domin sarkin Gaya na da iko ne kawai da kananan hukumomi uku, wanda suka hada da Gaya, Ajingi da Albasu, shi kuma Sarkin Rano na da kananan hukumomin Rano, Kibiya da Bunkure, yayin da sarkin Karaye ke da iko da kananan hukumomin Karaye da Rogo, shi kuma Sarki Muhammadu Sanusi II sarki mai daraja ta daya kamar yadda sabuwar sokar ta nuna yana da kananan hukumomi 36 da suke karkashin ikonsa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tarihin Daular Borno Da Sarakunanta (3)
Masarautu

Tarihin Daular Borno Da Sarakunanta (3)

January 12, 2025
Alh. Hassan Baita Ubawaru (Ma'ajin Hausawan Turai)
Masarautu

Tsofaffin Ɗaliban BUK Sun Yaba Wa Masarautar Hausawan Turai Kan Naɗa Ma’ajin Hausawan Turai

July 31, 2024
Wakilin Gwale A Majalisar Kano Ya Zargi Magoya Bayan Sarki Aminu Da Cin Zarafinsa
Labarai

Wakilin Gwale A Majalisar Kano Ya Zargi Magoya Bayan Sarki Aminu Da Cin Zarafinsa

July 22, 2024
Next Post
GORON JUMA’A 19/07/2024

GORON JUMA'A 19/07/2024

LABARAI MASU NASABA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version