ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Shugabancin Majalisar Legas: Ko Sulhunsu Zai Dore?

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
Legas

Yayin Da Obasa Ya Dawo, Mernda Ta Yi Murabus Bayan cece-kuce a tsakanin manyan masu ruwa da tsaki da kan rikicin shugabancin da ya turnike a majalisar dokokin Jihar Legas, Honorabul Mudashiru Obasa ya sake dawowa kan kujerarsa na shugabancin majalisar dokokin Jihar Legas.

Maido da shi cikin kan kurerar ya bayar da mamaki, bayan da Honorabul Mojisola Meranda ta yi murabus tare da komawa matsayinta na mataimakiyar shugabar majalisar, shi ne ya dau hankalin ‘yan Nijeriya wanda suka zuba ido su ga yadda abubuwan za su kasance a wannan zauren majalisa.

  • Matsalar Wuta Ta Jefa Wasu Sassan Nijeriya Cikin Duhu
  • Masana Kimiyya Na Sin Sun Gano Tsare-Tsaren Rayuwa A Muhallin Halittu Mafi Zurfi A Teku

Yanzu dai idanuwa sun karkata ga Obasa a daidai lokacin da ‘yan Nijeriya ke dakon ganin mataki na gaba na aiwatar da yarjejeniyar, yayin da rahotanni suka ce ana bukatar ya yi murabus daga ofis domin samar da hanyar da za a bi wajen ganin dan takara mai sassaucin ra’ayi ya fito a matsayin sabon shugaban majalisar.

ADVERTISEMENT

Majiyoyin sun shaida cewa, ya kamata a fito da sabon shugaban majalisar dokokin Legas nan da sa’o’i 48 masu zuwa, bisa yarjejeniyar da aka kulla da ta share fagen sauye-sauyen shugabanci da aka yi a ranar Litinin.

Rikicin shugabancin da ya dabaibaye majalisar dokokin Jihar Legas ya mayar da hannun agogon ‘yan majalisar jihar baya.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Rikicin ya fara ne tun bayan tsige Obasa a ranar 13 ga Janairu, 2025, a matsayin shugaban majalisar. ‘Yan majalisa 33 a zaman da aka yi a wannan rana suka tsige Obasa tare da ayyana tsohowar mataimakiyar shugaban majalisar, Merand a matsayin shugaban majalisar dokokin Jihar Legas.

Ko da yake ’yan majalisar sun yi nuni da cewa yana cin zarafin mukami da karkatar da kudade da kuma rashin da’a a matsayin wani bangare na dalilan tsige Obasa, matakin ya nuna asalin rikicin da ya barke a majalisar ta 10 a jihar.

‘Yan majalisar dai sun tsige Obasa ne a lokacin da yake kasar Amurka.

Bayan dawowarsa Legas a ranar 25 ga Janairu, 2025, ya kalubalanci cire shi.

Duk da tsoma bakin manyan jiga-jigan jam’iyyar APC, musamman tsofaffin gwamnonin jihohin Osun da Ogun, Cif Bisi Akande da Cif Olusegun Osoba, ba a warware rikicin shugabancin ba.

Ita ma majalisar ba da shawara kan harkokin mulki a jihar ta kasa shawo kan rikicin, inda wasu mambobin ke ganin cewa Shugaban kasa Bola Tinubu ne kadai zai iya shiga tsakani yadda ya kamata.

Sai dai duk da shiga tsakani da kwamitin sasantawa da Akande ya jagoranta da Tinubu ya shirya domin warware matsalar, da alama rikicin ya kara kamari. Kwamitin dai ya gana da ‘yan kungiyar GAC da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar a jihar da kuma ‘yan majalisar, duk da haka bai hakarsa ba ta cimma ruwa ba.

A ranar Alhamis da ta gabata ne Obasa, wanda bai halarci majalisar ba tun bayan tsige shi, ya koma harabar majalisar a wani mataki na ban mamaki.

Matakin dai ya sanya masu ruwa da tsaki a harkokin siyasa da sauran al’umma cikin kaduwa, yayin da sabon al’amarin ya kara jefa majalisar cikin rudani.

Duk da shigarsa ofishin, ‘yan majalisa 35 ne suka ki amincewa da Obasa, yayin da ‘yan majalisa hudu suka yi zaman da shi a wannan rana.

A zama na karshe da Meranda ta yi a matsayin shugaban, ta dage zaman majalisar tare da da’awar cewa ta zama shugaban majalisar dokokin Jihar Legas.

Yayin da take bayyana matakinta na yin murabus, Meranda ta ce ta yi hakan ne domin ceto majalisar daga rigingimu da abin kunya da bai kamata ba, tana mai jaddada cewa ta dauki matakin ne don karrama manyan shugabannin siyasa.

Ta yi alkawarin ba za ta rabu da tafarkin mutunci, adalci, rikon amana da hidimar mahaifinta Marigayi Cif Akanni Lawal Taoreed ba.

Legas
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Hajjin 2025: Ba Zan Taba Bai Wa Tinubu Da ‘Yan Nijeriya Kunya Ba – Shugaban NAHCON

Hajjin 2025: Ba Zan Taba Bai Wa Tinubu Da ‘Yan Nijeriya Kunya Ba – Shugaban NAHCON

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.