ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Shugabancin Majalisar Legas: Ko Sulhunsu Zai Dore?

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
Legas

Yayin Da Obasa Ya Dawo, Mernda Ta Yi Murabus Bayan cece-kuce a tsakanin manyan masu ruwa da tsaki da kan rikicin shugabancin da ya turnike a majalisar dokokin Jihar Legas, Honorabul Mudashiru Obasa ya sake dawowa kan kujerarsa na shugabancin majalisar dokokin Jihar Legas.

Maido da shi cikin kan kurerar ya bayar da mamaki, bayan da Honorabul Mojisola Meranda ta yi murabus tare da komawa matsayinta na mataimakiyar shugabar majalisar, shi ne ya dau hankalin ‘yan Nijeriya wanda suka zuba ido su ga yadda abubuwan za su kasance a wannan zauren majalisa.

  • Matsalar Wuta Ta Jefa Wasu Sassan Nijeriya Cikin Duhu
  • Masana Kimiyya Na Sin Sun Gano Tsare-Tsaren Rayuwa A Muhallin Halittu Mafi Zurfi A Teku

Yanzu dai idanuwa sun karkata ga Obasa a daidai lokacin da ‘yan Nijeriya ke dakon ganin mataki na gaba na aiwatar da yarjejeniyar, yayin da rahotanni suka ce ana bukatar ya yi murabus daga ofis domin samar da hanyar da za a bi wajen ganin dan takara mai sassaucin ra’ayi ya fito a matsayin sabon shugaban majalisar.

ADVERTISEMENT

Majiyoyin sun shaida cewa, ya kamata a fito da sabon shugaban majalisar dokokin Legas nan da sa’o’i 48 masu zuwa, bisa yarjejeniyar da aka kulla da ta share fagen sauye-sauyen shugabanci da aka yi a ranar Litinin.

Rikicin shugabancin da ya dabaibaye majalisar dokokin Jihar Legas ya mayar da hannun agogon ‘yan majalisar jihar baya.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Rikicin ya fara ne tun bayan tsige Obasa a ranar 13 ga Janairu, 2025, a matsayin shugaban majalisar. ‘Yan majalisa 33 a zaman da aka yi a wannan rana suka tsige Obasa tare da ayyana tsohowar mataimakiyar shugaban majalisar, Merand a matsayin shugaban majalisar dokokin Jihar Legas.

Ko da yake ’yan majalisar sun yi nuni da cewa yana cin zarafin mukami da karkatar da kudade da kuma rashin da’a a matsayin wani bangare na dalilan tsige Obasa, matakin ya nuna asalin rikicin da ya barke a majalisar ta 10 a jihar.

‘Yan majalisar dai sun tsige Obasa ne a lokacin da yake kasar Amurka.

Bayan dawowarsa Legas a ranar 25 ga Janairu, 2025, ya kalubalanci cire shi.

Duk da tsoma bakin manyan jiga-jigan jam’iyyar APC, musamman tsofaffin gwamnonin jihohin Osun da Ogun, Cif Bisi Akande da Cif Olusegun Osoba, ba a warware rikicin shugabancin ba.

Ita ma majalisar ba da shawara kan harkokin mulki a jihar ta kasa shawo kan rikicin, inda wasu mambobin ke ganin cewa Shugaban kasa Bola Tinubu ne kadai zai iya shiga tsakani yadda ya kamata.

Sai dai duk da shiga tsakani da kwamitin sasantawa da Akande ya jagoranta da Tinubu ya shirya domin warware matsalar, da alama rikicin ya kara kamari. Kwamitin dai ya gana da ‘yan kungiyar GAC da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar a jihar da kuma ‘yan majalisar, duk da haka bai hakarsa ba ta cimma ruwa ba.

A ranar Alhamis da ta gabata ne Obasa, wanda bai halarci majalisar ba tun bayan tsige shi, ya koma harabar majalisar a wani mataki na ban mamaki.

Matakin dai ya sanya masu ruwa da tsaki a harkokin siyasa da sauran al’umma cikin kaduwa, yayin da sabon al’amarin ya kara jefa majalisar cikin rudani.

Duk da shigarsa ofishin, ‘yan majalisa 35 ne suka ki amincewa da Obasa, yayin da ‘yan majalisa hudu suka yi zaman da shi a wannan rana.

A zama na karshe da Meranda ta yi a matsayin shugaban, ta dage zaman majalisar tare da da’awar cewa ta zama shugaban majalisar dokokin Jihar Legas.

Yayin da take bayyana matakinta na yin murabus, Meranda ta ce ta yi hakan ne domin ceto majalisar daga rigingimu da abin kunya da bai kamata ba, tana mai jaddada cewa ta dauki matakin ne don karrama manyan shugabannin siyasa.

Ta yi alkawarin ba za ta rabu da tafarkin mutunci, adalci, rikon amana da hidimar mahaifinta Marigayi Cif Akanni Lawal Taoreed ba.

Legas
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Legas
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Hajjin 2025: Ba Zan Taba Bai Wa Tinubu Da ‘Yan Nijeriya Kunya Ba – Shugaban NAHCON

Hajjin 2025: Ba Zan Taba Bai Wa Tinubu Da ‘Yan Nijeriya Kunya Ba – Shugaban NAHCON

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.