• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikita-rikitar Da Ta Biyo Bayan Mutuwar Mawaki Mohbad

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Mohbad

Mutuwar shahararren mawaki Ilerioluwa Aloba, wanda aka fi sani da Mohbad it ace maganar da aka shafe kusan makonni biyu ana tattauna ta a shafukan sada zumunta a fadin kasar nan baki daya.

Mawakin mai shekaru 27 ya rasu ne a ranar 12 ga watan Satumba cikin wani yanayi mai cike da rudani da ya janyo ce-ce-ku-ce a tsakanin abokan sana’ar sa a jihar Legas.

  • A Shirye Sin Take Ta Inganta Hadin Gwiwa Da UNESCO Domin Samar Da Ci Gaba Da Zaman Lafiya A Duniya
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Asirce: Sa-in-sa Ta Kaure Tsakanin Gwamnatin Tarayya Da Ta Zamfara

Sai dai wani abu mai kama da zargi da rudani shi ne kwana daya bayan rasuwarsa aka yi jana’izarsa, wani abu da shi ma ya janyo ka-ce-na-ce saboda abune wanda ba’a saba gani ba kasancewar sa ba musilmi ba ne kuma akanyi bukuku musamman idan wani ya mutu a cikin kabilar da aka haife shi.

Amma kuma a ranar Alhamis ‘yan sanda suka tono gawar Mohbad domin gudanar da bincike bayan da aka yi ta samun korafe-korafe har daga mawaka abokansa.

Itama gwamnatin jihar Legas karkashin mulkin Babajide Sanwo-Olu, ta bayar  da umurni a hukunta duk wanda ya taka wata rawa da ta kai ga mutuwar mawakin.

LABARAI MASU NASABA

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

Ya yinda rundunar  ‘yan sandan jihar Legas  ta ce ta kammala bincike kan gawar mawaki Ilerioluwa Aloba, wanda aka fi sani da Mohbad kuma a cewar rundunar, ta kammala binciken cikin nasara.

Dubban mutane ne suka yi zanga-zanga a sassan kasar nan musamman ma dai a jihar Legas da makwabtan jihohi domin nuna fushinsu kan yadda mawakin na Afrobeat ya mutu cikin wani yanayi mai cike da alamar tambaya.

A birnin Legas, an yi wani taro na zaman jimami a ranar Alhamis din satin da ya gabata inda aka ga matasa suna tattaki suna kiran da a bi wa mawakin kadinsa.

Rahotanni sun ce fitattun mawaka irinsu Dabido, Zlatan da Falz sun halarci taron zaman jimamin duk da cewa hukumomi sun gudanar da bincike kan gawar Mohbad.

Mohbad ya rasu ne bayan da aka garzaya da shi wani asibiti bisa wani rashin lafiya da ba a sani ba sai dai bayanai sun yi nuni da cewa, an yi wa mawakin wata allura a lokacin da aka kai shi asibitin inda daga nan kuma sai rai ya yi halinsa.

Mohbad, wanda a da mawaki ne karkashin kamfanin Malians na fitccen mawaki Naira Marley, ya fito idon duniya da wakokinsa irinsu ‘Ponmo, Peace, Ask About Me’ da sauransu.

A bara ne ya kuma fice daga kamfanin bisa wasu dalilai da har yanzu ba a fayyace ba sai dai daman hakan baya rasa nasaba da irin rikice-rikice da ake yawan samu a tsakanin masu irin wannan sana’ar Itama kungiyar nan ta kare muradun yarabawa da OPC ta bukaci gwamnati da jami’an tsaro akan suyi iya yinsu domin ganin an yiwa marigayi Mohbad adalci.

Kungiyar tace da ace marigayi Mohbad ya bayyana halin firgici da tashin hankalin da yake ciki ga kungiyar da tuni ba a kai ga haka ba kuma za su dauki matakin kare shi daga masu yi masa barazana ga rayuwa.

Kungiyar OPC dai ta bukaci rundunar ‘yan sanda ta kasa da jami’an hukumar tsaro ta farin kaya DSS da suyi kokarin gano wadanda suka kashe mawakin domin a hukunta su.

Wani tsohon faifan bidiyo na Bella Shmurda yana cewa Mohbad yana fama da matsalar tabin hankali kwanan nan ya sake kunno kai a yanar gizo mintuna bayan mutuwar mawakin.

Bayanai kan musabbabin mutuwarsa da kuma inda ya rasu yana ci gaba da zayyana har lokacin da ake hada wannan rahoto.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala
Nishadi

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

November 8, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
Nishadi

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Mawaƙin Shekarar 2025, Skales

October 25, 2025
Next Post
AU Ta Yi Kira Da Kara Zurfafa Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Afirka Da Sin

AU Ta Yi Kira Da Kara Zurfafa Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Afirka Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

November 10, 2025
Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

November 10, 2025
Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Masu Zagaye Kusa Da Doron Kasa

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Masu Zagaye Kusa Da Doron Kasa

November 10, 2025
Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

November 10, 2025
Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Ci Gaba Da Bude Kofa Mai Zurfi A Sin

Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Ci Gaba Da Bude Kofa Mai Zurfi A Sin

November 10, 2025
Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump

Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump

November 10, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Zai Ziyarci Kasashen Guinea Da Saliyo

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Zai Ziyarci Kasashen Guinea Da Saliyo

November 10, 2025
FCT Ta Saka Ranar 1 Disamba Don Kammala Biyan Kudin Hajjin 2026 N7.7m

FCT Ta Saka Ranar 1 Disamba Don Kammala Biyan Kudin Hajjin 2026 N7.7m

November 10, 2025
Xi Ya Taya Ouattara Murnar Sake Lashe Zaben Shugaban Cote D’Ivoire

Xi Ya Taya Ouattara Murnar Sake Lashe Zaben Shugaban Cote D’Ivoire

November 10, 2025
Rundunar Sojin Sama Ta Kai Hari Kan ISWAP Da Ƴan Bindiga A Borno, Kwara Da Katsina

Rundunar Sojin Sama Ta Kai Hari Kan ISWAP Da Ƴan Bindiga A Borno, Kwara Da Katsina

November 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.