• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikita-rikitar Da Ta Biyo Bayan Mutuwar Mawaki Mohbad

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Nishadi
0
Rikita-rikitar Da Ta Biyo Bayan Mutuwar Mawaki Mohbad
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mutuwar shahararren mawaki Ilerioluwa Aloba, wanda aka fi sani da Mohbad it ace maganar da aka shafe kusan makonni biyu ana tattauna ta a shafukan sada zumunta a fadin kasar nan baki daya.

Mawakin mai shekaru 27 ya rasu ne a ranar 12 ga watan Satumba cikin wani yanayi mai cike da rudani da ya janyo ce-ce-ku-ce a tsakanin abokan sana’ar sa a jihar Legas.

  • A Shirye Sin Take Ta Inganta Hadin Gwiwa Da UNESCO Domin Samar Da Ci Gaba Da Zaman Lafiya A Duniya
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Asirce: Sa-in-sa Ta Kaure Tsakanin Gwamnatin Tarayya Da Ta Zamfara

Sai dai wani abu mai kama da zargi da rudani shi ne kwana daya bayan rasuwarsa aka yi jana’izarsa, wani abu da shi ma ya janyo ka-ce-na-ce saboda abune wanda ba’a saba gani ba kasancewar sa ba musilmi ba ne kuma akanyi bukuku musamman idan wani ya mutu a cikin kabilar da aka haife shi.

Amma kuma a ranar Alhamis ‘yan sanda suka tono gawar Mohbad domin gudanar da bincike bayan da aka yi ta samun korafe-korafe har daga mawaka abokansa.

Itama gwamnatin jihar Legas karkashin mulkin Babajide Sanwo-Olu, ta bayar  da umurni a hukunta duk wanda ya taka wata rawa da ta kai ga mutuwar mawakin.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

Ya yinda rundunar  ‘yan sandan jihar Legas  ta ce ta kammala bincike kan gawar mawaki Ilerioluwa Aloba, wanda aka fi sani da Mohbad kuma a cewar rundunar, ta kammala binciken cikin nasara.

Dubban mutane ne suka yi zanga-zanga a sassan kasar nan musamman ma dai a jihar Legas da makwabtan jihohi domin nuna fushinsu kan yadda mawakin na Afrobeat ya mutu cikin wani yanayi mai cike da alamar tambaya.

A birnin Legas, an yi wani taro na zaman jimami a ranar Alhamis din satin da ya gabata inda aka ga matasa suna tattaki suna kiran da a bi wa mawakin kadinsa.

Rahotanni sun ce fitattun mawaka irinsu Dabido, Zlatan da Falz sun halarci taron zaman jimamin duk da cewa hukumomi sun gudanar da bincike kan gawar Mohbad.

Mohbad ya rasu ne bayan da aka garzaya da shi wani asibiti bisa wani rashin lafiya da ba a sani ba sai dai bayanai sun yi nuni da cewa, an yi wa mawakin wata allura a lokacin da aka kai shi asibitin inda daga nan kuma sai rai ya yi halinsa.

Mohbad, wanda a da mawaki ne karkashin kamfanin Malians na fitccen mawaki Naira Marley, ya fito idon duniya da wakokinsa irinsu ‘Ponmo, Peace, Ask About Me’ da sauransu.

A bara ne ya kuma fice daga kamfanin bisa wasu dalilai da har yanzu ba a fayyace ba sai dai daman hakan baya rasa nasaba da irin rikice-rikice da ake yawan samu a tsakanin masu irin wannan sana’ar Itama kungiyar nan ta kare muradun yarabawa da OPC ta bukaci gwamnati da jami’an tsaro akan suyi iya yinsu domin ganin an yiwa marigayi Mohbad adalci.

Kungiyar tace da ace marigayi Mohbad ya bayyana halin firgici da tashin hankalin da yake ciki ga kungiyar da tuni ba a kai ga haka ba kuma za su dauki matakin kare shi daga masu yi masa barazana ga rayuwa.

Kungiyar OPC dai ta bukaci rundunar ‘yan sanda ta kasa da jami’an hukumar tsaro ta farin kaya DSS da suyi kokarin gano wadanda suka kashe mawakin domin a hukunta su.

Wani tsohon faifan bidiyo na Bella Shmurda yana cewa Mohbad yana fama da matsalar tabin hankali kwanan nan ya sake kunno kai a yanar gizo mintuna bayan mutuwar mawakin.

Bayanai kan musabbabin mutuwarsa da kuma inda ya rasu yana ci gaba da zayyana har lokacin da ake hada wannan rahoto.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Xi Ya Jinjinawa Jaruman Kasar Da Suka Kwanta Dama A Ranar Shahidan Kasar Sin

Next Post

AU Ta Yi Kira Da Kara Zurfafa Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Afirka Da Sin

Related

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu
Nishadi

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

7 days ago
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 
Nishadi

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

2 weeks ago
Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani
Nishadi

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

3 weeks ago
Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa
Nishadi

Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa

3 weeks ago
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro
Nishadi

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

4 weeks ago
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage
Nishadi

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

4 weeks ago
Next Post
AU Ta Yi Kira Da Kara Zurfafa Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Afirka Da Sin

AU Ta Yi Kira Da Kara Zurfafa Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Afirka Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.