Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home WASANNI

Ronaldo, Messi Da Neymar Za Su Sake Fafatawa

by Tayo Adelaja
September 24, 2017
in WASANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Hukumar kula da kwallon kafa ta duniya, FIFA, ta fitar sunayen wadanda za a zaba a matsayin fitattaun ’yan kwallo na duniya daga cikinsu, wadanda suka hada da Cristiano Ronaldo daga Real Madrid dan kasar Portugal da Lionel Messi daga Barcelona na Argentina da kuma Neymar daga Paris St-Germain dan kasar Brazil.

A shekarar da ta gabata dai Ronaldo ne ya lashe kyautar gwarzon dan wasan bayan da ya doke Messi da Neymar da kuma Antoine Griezmann na Atletico Madrid.

samndaads

Ronaldo ya taba lashe kyautar sau hudu, inda a bara ya lashe gasar cin kofin laliga da kuma kofin zakarun Turai da Real Madrid, sannan kuma shi ne yafi kowanne dan wasa zura kwallo a raga a gasar ta zakarun Turai da su ka lashe.

Messi, wanda ya fi kowa lashe kyautar, inda ya lashe ta sau biyar, da Neymar na kasar Brazil su ne abokan karawar Ronaldo bayan da su ka lashe kofin Copa del Rey na kasar ta Spaniya, sai dai yanzu Neymar ya bar kungiyar inda a yanzu ya ke taka leda a sabon kulob dinsa na PSG.

Kocin Chealsea Antonio Conte na iya lashe kofin gwarzon koci bayan da ya ja ragamar kungiyar har su ka kai da samun nasarar lashe kofin Premier a kakarsa ta farko a Stamford Bridge.

Yayin da shi ma Zidane zai iya lashe kyautar bayan da ya ja ragamar Real Madrid ta lashe gasar Laliga da kofin zakarun Turai.

Shi ma Alegri ya jagoranci jubentus ta lashe gasar Serie A, sannan kuma ya kai kungiyar wasan karshe na cin kofin zakarun Turai sai dai sun sha kasha da ci 4-1 a hannun Real Madrid.

An sake gabatar da mai rike da kofin fitacciyar ‘yar kwallon kafar  mata Carli Lloyd a matsayin wacce za ta lashe kofin na bana.

Lieke Martens wadda ta ci kwallo uku a wasan neman shiga gasar Euro 2017 a Netherland, da kuma ‘yar kwallon Benezuela Deyna Castellanos su ne abokan karawar Lloyd.

A ranar 23 ga watan Oktoba ne za a gabar da wadanda su ka yi nasara a dakin taro na Palladium da ke Landan.

SendShareTweetShare
Previous Post

Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya na gaisawa da Shugaba Amurka Donald Trump a birnin New York lokacin taron Majalisar Dinkin Duniya da ya gabata

Next Post

Zidane Ya Na Son Sanches A Real Madrid

RelatedPosts

Wane Ne Sabon Kociyan Chelsea, Thomas Tuchel?

Wane Ne Sabon Kociyan Chelsea, Thomas Tuchel?

by Sulaiman Ibrahim
2 hours ago
0

Chelsea ta nada tsohon kocin kungiyar kwallon kafa ta Paris...

Laporta Ya Zargi PSG Da Jefa Barcelona Rudani

Laporta Ya Zargi PSG Da Jefa Barcelona Rudani

by Sulaiman Ibrahim
2 hours ago
0

Dan takarar shugabancin kungiyar kwallon kafa ta Barcelona wanda shine...

Rashin Kudi Yana Neman Saka Real Madrid Hakura Da Mbappe

by Sulaiman Ibrahim
3 hours ago
0

kungiyar kwallon kafa ta Paris Saint German ta soma tuntubar...

Next Post

Zidane Ya Na Son Sanches A Real Madrid

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version