• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rusau: Kotu Ta Ci Tarar Gwamnatin Kano Naira Miliyan 2

by Sadiq
2 years ago
Rusau

Wata Babbar Kotun Tarayya ta bai wa Gwamnatin Kano umarnin biyan tarar naira miliyan biyu saboda yunkurin rushe wasu gine-gine.

Kotun dai ta umarci Gwamnatin Kano da ta biya wasu mutum biyu naira miliyan daya-daya saboda yunkurin rushe gine-ginensu a Unguwar Salanta da ke jihar.

  • Halin ‘Yan Siyasa Na Ba Sarakuna Mamaki – Sarkin Zazzau
  • Masana : Darussa Daga Shirin Kawar Da Talauci Na Kasar Sin Na Da Muhimmanci Ga Afrika

Alkalin da ya jagoranci zaman kotun a yau Juma’a, Mai Shari’a Simon Amobeda, ya ce Gwamnatin Kanon ta sauka daga kan layi ta daidai saboda shafa wa gine-gine fenti mai nuna alamar rusau kan zargin an yi su ne ba bisa ka’ida ba.

Mai Shari’a Simon ya kafa hujjar cewa, Gwamnatin ta saba wa sashe na 43 da 44 da ya bai wa wadanda abin ya shafa — Saminu Shehu Muhd da Tasiu Shehu Muhammad — ’yancin mallakar gine-gine kamar yadda Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya ya tanadar.

Jaridar Aminiya ta ruwaito cewa, gine-gine da lamarin ya shafa sun hada da fulotai masu lamba 41 da 43 da kuma 68 a Unguwar Salanta.

LABARAI MASU NASABA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Kazalika, kotun ta riki cewa kutse da Gwamnatin Kanon ta yi a gine-ginen da misalin karfe 11 na daren ranar 14 ga watan Yunin 2023 ya saba wa tanadin Kundin Tsarin Mulkin na Kasa.

Kotun ta kuma bai wa Gwamnatin Kano umarnin sake fentin gine-ginen wanda Hukumar Tsara Birni ta Kano KNUPDA ta shafa wa alamar mai dauke jan fenti.

Da yake batu bayan hukuncin, Barista Bashir Ibrahim wanda ya shigar da kara a gaban kuliya, ya bayyana hukuncin da kotun ta yanke a matsayin abun yabawa saboda kare ’yanci da martabar bilAdama.

A nasa bangaren, Lauyan Gwamnatin Kano, Barista Musa Dahuru Muhad, ya ce za su yi nazari kan hukuncin da kotun ta yanke gabanin daukar matakin da ya dace.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna
Labarai

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga
Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra
Labarai

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Next Post
Marseille Ta Dauki Aubameyang Daga Chelsea

Marseille Ta Dauki Aubameyang Daga Chelsea

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025
Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

November 9, 2025
Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

November 9, 2025
Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

November 9, 2025
NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.