• English
  • Business News
Thursday, July 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rusau: Kotu Ta Ci Tarar Gwamnatin Kano Naira Miliyan 2

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Rusau: Kungiyoyi Sun Bukaci A Hana Gwamnan Kano Shiga Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata Babbar Kotun Tarayya ta bai wa Gwamnatin Kano umarnin biyan tarar naira miliyan biyu saboda yunkurin rushe wasu gine-gine.

Kotun dai ta umarci Gwamnatin Kano da ta biya wasu mutum biyu naira miliyan daya-daya saboda yunkurin rushe gine-ginensu a Unguwar Salanta da ke jihar.

  • Halin ‘Yan Siyasa Na Ba Sarakuna Mamaki – Sarkin Zazzau
  • Masana : Darussa Daga Shirin Kawar Da Talauci Na Kasar Sin Na Da Muhimmanci Ga Afrika

Alkalin da ya jagoranci zaman kotun a yau Juma’a, Mai Shari’a Simon Amobeda, ya ce Gwamnatin Kanon ta sauka daga kan layi ta daidai saboda shafa wa gine-gine fenti mai nuna alamar rusau kan zargin an yi su ne ba bisa ka’ida ba.

Mai Shari’a Simon ya kafa hujjar cewa, Gwamnatin ta saba wa sashe na 43 da 44 da ya bai wa wadanda abin ya shafa — Saminu Shehu Muhd da Tasiu Shehu Muhammad — ’yancin mallakar gine-gine kamar yadda Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya ya tanadar.

Jaridar Aminiya ta ruwaito cewa, gine-gine da lamarin ya shafa sun hada da fulotai masu lamba 41 da 43 da kuma 68 a Unguwar Salanta.

Labarai Masu Nasaba

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Kazalika, kotun ta riki cewa kutse da Gwamnatin Kanon ta yi a gine-ginen da misalin karfe 11 na daren ranar 14 ga watan Yunin 2023 ya saba wa tanadin Kundin Tsarin Mulkin na Kasa.

Kotun ta kuma bai wa Gwamnatin Kano umarnin sake fentin gine-ginen wanda Hukumar Tsara Birni ta Kano KNUPDA ta shafa wa alamar mai dauke jan fenti.

Da yake batu bayan hukuncin, Barista Bashir Ibrahim wanda ya shigar da kara a gaban kuliya, ya bayyana hukuncin da kotun ta yanke a matsayin abun yabawa saboda kare ’yanci da martabar bilAdama.

A nasa bangaren, Lauyan Gwamnatin Kano, Barista Musa Dahuru Muhad, ya ce za su yi nazari kan hukuncin da kotun ta yanke gabanin daukar matakin da ya dace.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: gwamnatikanoKotuRusauTara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masana : Darussa Daga Shirin Kawar Da Talauci Na Kasar Sin Na Da Muhimmanci Ga Afrika

Next Post

Marseille Ta Dauki Aubameyang Daga Chelsea

Related

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta
Labarai

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

42 minutes ago
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

57 minutes ago
EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi
Labarai

EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi

2 hours ago
Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya
Labarai

Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya

5 hours ago
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo

7 hours ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutum 22 Kan Zargin Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato

7 hours ago
Next Post
Marseille Ta Dauki Aubameyang Daga Chelsea

Marseille Ta Dauki Aubameyang Daga Chelsea

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

July 10, 2025
EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi

EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi

July 10, 2025
Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya

Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya

July 10, 2025
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo

July 10, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum 22 Kan Zargin Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato

July 10, 2025
Sauye-sauyen Tinubu Suna Taimaka Wa Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya — Minista

Sauye-sauyen Tinubu Suna Taimaka Wa Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya — Minista

July 10, 2025
Buhari Ba Mutum Ne Mai Son Abun Duniya Ba – Gowon

Buhari Ba Mutum Ne Mai Son Abun Duniya Ba – Gowon

July 10, 2025
Sojoji Sun Kai Hari Maɓoyar Boko Haram A Borno, Sun Kashe Wasu ‘Yan Ta’adda

Sojoji Sun Kai Hari Maɓoyar Boko Haram A Borno, Sun Kashe Wasu ‘Yan Ta’adda

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.