• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rushewar Gini: Wike Ya Umarci A Cafko Mamallakin Ginin Cikin Gaggawa

byKhalid Idris Doya
2 years ago
Wike

Biyo bayan rushewar wani gini mai hawa biyu a kan babban hanyar layin Legas da ke gundumar Garki II a Abuja wajajen karfe 11:45 na daren ranar Laraba, ministan birnin tarayya, Nyesom Wike, ya bada umarnin a gaggauta kamo wanda ya mallaki ginin da ya rushe din. 

Wike, wanda ya bada umarnin a lokacin da ya ziyarci wurin da lamarin ya faru da safiyar ranar Alhamis, ya jinjina da aikin ceto da aka ake yi a ginin, ya kuma ce, rushewar ginin abun takaici ne da suka wayi gari da shi.

  • FIFA Ta Fara Bincike Kan Sumbata Da Rubiales Ya Yi Wa ‘Yar Wasan Spain
  • Xi Jinping: Za Kara Karfin Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Ya ce: “Ba abun da muka tsammaci faruwarsa ba ne. Bar na yaba wa hukumomi, musamman NEMA da FEMA bisa kasancewa da suka yi a nan domin taimakonmu wajen ceton rayuwa a kalla 32. Abun bakin ciki da takaici mun rasa mutum biyu daga cikinsu.

“Ina fatan babban sakatare zai tabbatar an samar da kudaden da za a biya jinyar wadanda aka ceto, don kar mu sake rasa wani mutum kuma, sannan, wannan zai faru ne cikin gaggawa.

“Na biyu, wadannan abubuwan ne fa muke ta fada, ba wanda ya san hakan zai faru, kazalika, lokacin da gwamnati ta ce za ta dauki mataki kan gine-ginen da aka yi ba bisa ka’ida ba, ba za a yi hakan don wani mutum daya ko don ni ba ne, a’a za a yi ne don mu dukka kuma don komai su tafi daidai,” ya shaida.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Ministan FCT din ya nuna bacin ransa kan yadda hukumar kula da birnin tarayya (FCTA) ta dauki tsawon lokaci ba tare da ta zauna da mazauna kauyen Garki ba, ya ce, cikin gaggawa ya na son a zauna da mutanen kauyen domin fito musu da tsarin da gwamnati take son yi a wannan yankin.

“Idan gwamnati ta ce ga tsarin gini kaza da take son a yi, ba wai don a musguna ma wani ba ne, sam, illa domin a kare lafiyar kowa da kowa ne. An shirya birane domin dakile faruwar irin wannan. Abun takaici ka ga gine-gine ba tare da amincewar yin ginin ba. Na umarci a nemo tare kamo mamallakin wannan gini. Ya na da matukar muhimmanci.

“Babu shakka gwamnati za ta amshi ragamar wannan yankin kuma a tabbatar ba abun da ya sake faruwa. Ina rokon dukkanin mutanen wannan yankin da su ba mu hadin kai domin kyautata rayuwar kowa. Babu wanda ya zo nan domin ya ce ina son wane, ba na son wa ne.”

Daga karshe dai ya jajanta ma iyalan wadanda suka rasa rayukansu tare da addu’ar Allah zai bai wa wadanda suka jikkata lafiya.

Shi ma da yake jawabi, daraktan sanya ido kan harkokin bunkasawa ta hukumar FCTA, Muktar Galadima, ya ce za su cigaba da sanya ido domin tabbatar da jama’a su tashi a wuraren da ba amince a yi gini a cikinsu ba musamman wuraren da suke kan hanyar ruwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba
Labarai

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Next Post
Xi Ya Yi Nuni Ga Ikon BRICS Na Juya Akalar Harkokin Duniya Zuwa Hanya Mai Bullewa

Xi Ya Yi Nuni Ga Ikon BRICS Na Juya Akalar Harkokin Duniya Zuwa Hanya Mai Bullewa

LABARAI MASU NASABA

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version