• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Ci Gaban Sin Zai Samar Da Sabbin Damammaki Ga Kasashen Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
Kasashen duniya

A jiya Lahadi ne zaunannun mambobin ofishin siyasa na kwamitin tsakiya na JKS karo na 20, suka gana da ’yan jaridu na kasar Sin da na kasashen ketare.

A yayin taron, babban sakataren kwamitin kolin JKS Xi Jinping ya ba da jawabi, inda ya ce a halin yanzu, kasar Sin tana kan tafiyar da aka sanya a gaba, domin gina wata kasa mai tsarin gurguzu bisa dukkan fannoni cikin wannan sabon zamani, tana kuma dukufa domin cimma burinta a lokacin cika shekaru 100 da kafuwar Jamhuriyyar Jama’ar Kasar Sin, wato zuwa tsakiyar karnin nan, kuma kasar Sin za ta gina wata kasa mai karfi bisa tsarin gurguzu cikin wannan sabon zamani, wato wata kasa mai matsakacin wadata, da dimokuradiyya, da wayewar kai, da zaman daidaito, kuma mai kyau, ta yadda za ta tabbatar da farfadowar kasa baki daya, bisa salon ci gaba iri na kasar Sin cikin sabon zamani.

  • An Zartas Da Kuduri Kan “Gyararren Kundin Ka’idojin JKS”

Haka kuma, cikin jawabinsa, Xi ya bayyana babban aikin JKS, inda ya jaddada cewa, ya kamata a ci gaba da taimakawa jama’ar kasar wajen cimma burinsu na kyautata zaman rayuwa, yayin da ake gina wata kasa mai matsakacin wadata, wadda za ta kara samar da damammaki ga duniya baki daya.
Kaza lika, bayanin da ya yi game da “salon ci gaba iri na kasar Sin cikin sabon zamani” ya janyo hankulan masu sa ido na kasashen duniya.

A yayin babban taron wakilan JKS karo na 20, an ba da shawara kan yadda za a gina wata kasa mai tsarin gurguzu bisa dukkan fannoni cikin wannan sabon zamani, da kuma yadda za a inganta farfadowar kasar baki daya.

Idan aka kwatanta da salon ci gaba iri na yammacin kasashen duniya, wanda ya fi mai da hankali kan kudi, da kwashe albarkatun sauran kasashe, za a gane cewa, salon ci gaba iri na kasar Sin ya warware matsaloli da dama dake kan hanyar neman ci gaban bil Adama, da kuma samar da wata sabuwar hanyar neman ci gaba cikin sabon zamani ga dukkanin bil Adama.

LABARAI MASU NASABA

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Haka kuma, Xi Jinping ya jaddada cewa, za mu yi aiki da sauran al’ummomin kasashen duniya, domin ci gaba da gina al’umma mai makomar bai daya ga daukacin bil Adama, kuma, kasar Sin za ta kara bude kofa ga waje, domin samar da karin damammaki ga duniya.

Bugu da kari, sakamakon da aka cimma a yayin taron wakilan JKS karo na 20, da sanawar da shugaban kolin kasar Sin ya yi, sun kara fahimtar da jama’ar kasashen duniya kan wani muhimmin batu, wato, Jam’iyyar Kwaminis ta Kasar Sin, jam’iyya ce mai muhimmanci wajen tabbatar da gudanarwar harkokin kasa yadda ya kamata, kuma, muhimmiyar jam’iyya ce, wadda za ta tabbatar da ginawar wata kasa mai tsarin gurguzu bisa dukkan fannoni a sabon zamani, da kuma inganta farfadowar kasa bai daya. (Mai Fassarawa: Maryam Yang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya
Daga Birnin Sin

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103
Daga Birnin Sin

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Next Post
2023: Katsinawa Ku Kubutar Da Kanku Daga Rashin Iya Mulkin APC — Mustapha Inuwa

2023: Katsinawa Ku Kubutar Da Kanku Daga Rashin Iya Mulkin APC — Mustapha Inuwa

LABARAI MASU NASABA

gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.