• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Rikicin Cikin Gida Na Barazanar Mayar Da Hannun Agogo Baya A PDP

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
PDP Ta Yi Gangamin Wayar Da Kan Jama’a Kan Muhimmancin Katin Zabe A Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ga dukkan alamu sabon rikicin cikin gidan da ya kunno kai a babbar jam’iyyar adawa ta PDP sanadin zabo Gwamna Okowa a matsayin dan takarar mataimakin shugaban kasa a zaben 2023 na barazanar mayar da hannun agogo baya a jam’iyyar.

Dama dai ana ganin tun da aka tsayar da Alhaji Atiku Abubakar a matsayin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar ta PDP a babban zaben 2023, tsuguno ba ta kare ba a cikin jam’iyyar, musamman ganin cewa yankin kudancin Nijeriya ya so a ba shi takara amma hakan bai yiwu ba.

  • Atiku Ya Nesanta Kansa Daga Rikicin Cikin Gida Na PDP A Ekiti

Wasu na ganin kamar ma jam’iyyar za ta iya samun koma-baya ganin yadda wasu jiga-jigan jam’iyyar ciki har da gwamnoni suke yunkurin sauya sheka.

Hakan bai kara fitowa fili ba sai bayan da Atiku Abubakar ya tsayar da Ifeanyi Okowa a matsayin wanda zai tsaya mataimakinsa.

Hakan ya ta da kura tare da haifar da sabani tsakanin manyan jiga-jigan jam’iyyar, yayin da wasu suka fara kiraye-kirayen a tunbuke shugaban PDP na kasa, Dakta Iyorchia Ayu.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Batun gaskiya sabon rikicin na neman mai da hannun agogo baya a jam’iyyar PDP, inda shi kansa Atiku ya ce PDP ba za ta tarwatse ba, za su dauki matakin shawo kan duk wadanda ke ganin an yi musu ba daidai ba.

Alamu sun nuna ba abin da ke tafiya daidai a jam’iyyar, domin kuwa gwamnoni biyu rak cikin 13 ne suka halarci wurin da kwamitin gudanarwa na jam’iyyar ya kaddamar da tawagar yakin neman zaben gwamnan Jihar Osun.

Akwai rade-radin da ke yawo cewa Atiku na shan maganganu daga gwamnoni na ya ajiye Okowa tare da musanya shi da Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike.

Haka zalika, magoya bayan Wike su ma suna ci gaba da nuna bukatar a sanya Wike idan dai ana son zaman lafiya a cikin jam’iyyar.

Ko a cikin makon nan ma Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya ce zai je gaban gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike ya roke shi domin ya ci gaba da zama a jam’iyyar, saboda ana tunanin zai bar jam’iyyar.

Shugaban kwamitin Walid Jibrin ne ya bayyana haka, kwanaki uku bayan da Wike ya watsa wa wata tawagar da aka tura masa kasa a ido, ranar Alhamis a Turkiyya.

Wannan rikici dai ya kawo wata babbar baraka ga PDP da kuma Atiku daidai lokacin da ake kokarin fara shirin yakin neman zaben 2023.

Rikicin ya kara muni a ranar Laraba, yayin da manyan makusantan Wike biyu, Gwamna Samuel Ortom na Jihar Benuwe da tsohon Gwamnan Jihar Ekiti, Ayodele Fayose suka fito suka ce ba za su goyi bayan takarar Atiku ba.

Yayin da Ortom ya ce har yanzu zuciyarsa ba ta kwanta da goyon bayan Atiku Abubakar ba, Fayose kuwa cewa ya yi Wike ba zai goyi bayan Atiku ba.

An dai tura masa tsohon ministan harkokin ‘yan sanda, Adamu Waziri domin ya gana da shi, amma ya ki yarda ya gan shi.

Duk da yake ‘yan kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP sun rabu dangane da aniyar kwamitin na ziyartar Wike don rarrashinsa, wanda shugaban kwamitin ya ce idan ta kama su durkusa masa ne za su yi. Alhaji Adamu Maina Waziri dan kwamitin amintattun ne, wanda ya ce ba ya goyon bayan haka.

Wasu rahotanni da dama suna bayyana cewa shirun da Wike yake yi tun bayan zaben fitar da gwani, ya damalmala abubuwa ne a jam’iyyar PDP. Rashin jituwar Gwamna Wike da Atiku yana barka PDP a kudancin Nijeriya. Bugu da kari, Wike ya ki bari ya zauna da mutanen Atiku.

Bayanai na nuna cewa Atiku da Okowa na fuskantar barazana a jihohin irinsu Delta, Edo, Akwa Ibom, Bayelsa, Legas, Ogun, Ondo, Anambra da kuma Imo.

Amma a jihohin Ribas, Kuros Riba, Inugu, Abiya, Oyo da Ekiti, ‘ya ‘yan PDP ba su gamsu da Okowa ba. Masana suna ganin hakan zai iya kawo wa PDP cikas.

Amma akwai wata sanarwa daga Kungiyar Matasa ta Ohaneaze (OYC) sun ce Atiku ya ajiye Okowa a kan bukatar kanshi. Sanarwar mai dauke da sa hannun Shugaban, Mazi Nnabuike da Sakatare Kwamared Obinna Achionye sun ce duk wani yunkuri na canja Okowa zai janyo wasu abubuwa.

Kungiyar Inyamurai ta ce yankin kudu maso gabas ba zai taba yarda ya fadi gaba daya ba, tun da ya rasa haifar da dan takarar shugaban kasa a PDP ko a APC.

“Babu Bukatar sauya abin da muka yi tunanin PDP da APC za su kai tikitin takarar shugaban kasa ga yankin kudu maso gabas, amma hakan bai samu ba.
“Duk da wannan an riga an wuce da shi, abin da kadai ya rage mana shi ne zabin Gwamna Ifeanyi Okowa a matsayin abokin takarar Alhaji Atiku Abubakar, ta la’akari da cewa Okowa Inyamuri ne cikakke.

Idan kuwa aka koma cikin jam’iyyar PDP da mukaman da ke cikin jam’iyyar za a ga cewa ‘yan arewa ne suka mamaye manyan mukamai a cikinta. Zaben Atiku matsayin dan takara ya sa a yanzu PDP ta koma hannun ‘yan Arewa.

Atiku dai shi ne dan takarar shugaban kasa daga arewa maso gabas. Shugaban PDP, Iyorchia Ayu dan Arewa ta tsakiya ne. Shugaban dattawa na jam’iyyar, Walid Jibrin dan arewa maso gabas ne.

Mataimakin shugaban, Umar Damagum dan arewa ne, wanda shi ke bayan da umarni idan Ayu ba ya nan.

Yayin da Atiku ya kai wa Wike ziyara bayan kammala zaben fid da gwani, Wike ya tunatar da shi yarjejeniyar da ta ce idan dan arewa ne ya yi nasarar a zaben fid da gwani, to Iyorchia Ayu zai sauka daga shugabancin PDP.

Atiku ya shawarci Wike da cewa su bar wannan batun tukunna a tsakaninsu, ka da su fitar da shi har sai ya shawarci Ayu.
Idan dai ba a manta ba, irin wannan rikicin cikin gida na daga cikin musabbabin faduwar jam’iyyar PDP zabe a 2015.

Yanzu dai ya rage wa shugabannin jam’iyyar da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar su zauna su lalubo hanyar sulhunta ‘ya’yanta don kai wa ga gaci, idan ba haka kuwa suna ji suna gani zaben 2023 ya sake kucce masu a matakin kasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Gogaggen Dan Siyasa Ne, In Ji Ganduje

Next Post

Hukumar Da Ke Kula Da Gidajen Yarin Nijeriya Na Cigiyar Fursunoni 69 Da Suka Tsere Daga Kuje

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

2 weeks ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

2 weeks ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

2 weeks ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

3 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

3 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

3 weeks ago
Next Post
Hukumar Da Ke Kula Da Gidajen Yarin Nijeriya Na Cigiyar Fursunoni 69 Da Suka Tsere Daga Kuje

Hukumar Da Ke Kula Da Gidajen Yarin Nijeriya Na Cigiyar Fursunoni 69 Da Suka Tsere Daga Kuje

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.