ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Katsina: Sojoji Sun Ragargaje Su

by Abubakar Sulaiman
2 years ago
Katsina

Wani abu mai kama da sakaci da ya ɗaure kan al’umma da dama a Jihar Katsina shi ne, yadda ‘yan ta’adda suka yi wa wasu garuruwa ƙawanya suka yi masu kisan kare dangi a karamar hukumar Kankara ta Jihar Katsina.

Sai dai bayanan da suka biyo bayan wannan mummunan harin wuce gona da iri shi ne, irin yadda gwamnatin Jihar Katsina karkashin jagorancin Malam Dikko Umar Radda ta yi gum da bakinta a daidai lokacin da radadin kisan ke tafarfasa.

  • Tinubu Ya Ba Jama’an Tsaro Umarnin Kamo Ƴan Ta’addan Da Suka Kashe Mutane A Katsina
  • Za A Yi Sallah Babu Lantarki A Jahohin Kano, Jigawa, Katsina, Ma’aikatan KEDCO Sun Shiga Yajin Aiki

Ba tare da aune ba, sai dai ji aka yi tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takara shugaban kasa a zaben da ya gabata a karkashin jam’iyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar yana jajanta wa al’ummomin da abin ya shafa, ita kuwa gwamantin Ji-har Katsina ta yi shiru.

ADVERTISEMENT

Bullar wancan sanarwar tasa jikin jama’a da dama ya yi la’asar ganin cewa wani mutum daga nisan duniya ya fara nuna alhini kan wannan lamari, amma gwa-mantin Jihar Katsina tana nan gefe guda.

Alhaji Atiku ya ce ya yi mamakin yadda ‘yan bindiga ke da karfin halin kai wa ja-mi’an tsaro harin kwantan bauna har su kashe wasu daga ciki.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Yana mai Allah wadai da kuma tir da irin wannan lamarin da ke taruwa a Jihar Katsina da wasu jihohin arewacin Nijeriya tsawon lokaci abin ya ki karewa.

Kamar yadda rahotanni suka bayyana cewa an kashe fiye da mutane 50 a hare-haren wuce gona da iri da ‘yan bindiga suka kai ciki har da jami’an ‘yansanda hudu da kuma dakarun zaman lafiya na C-Watch guda biyu.

Rundunar ‘yansandan Jihar Katsina a ta bakin mai magana da yawunta, ASP Abu-bakar Aliyu ya yi taron manema labarai, inda ya bayyana yadda abin ya faru a bangaren jami’an tsaro. Ya ce an kashe jami’an ‘yansanda 4 da jami’an C-Watch 2 da Kuma mutane 20.

Ya kara da cewa lallai wannan harin abin takaici ne da bakin ciki, musamman irin yadda harin ya fi rutsawa da mata da kananan yara.

Kazalika, rundunar ‘yansanda ta ce tuni jami’an tsaro sun yi kawaye wajen da wannan lamari ya faru domin tabbatar da an kama wadannan suka yi wannan danyen aiki domin su girbi abin da suka shuka.

Sai dai kuma a cikin wani irin yanayi da sanyin jiki gwamantin Jihar Katsina ta fitar da sanarwa tana jajanta wa al’ummomin da wannan harin ya shafa a kauyen gidan Boka a karamar hukumar Kankara, inda ta ce an kashe mutane 26.

Sanarwar wanda mai taimaka wa gwamnan Jihar Katsina kan harkokin yada laba-rai, Ibrahim Kaula ya fitar, inda ya nuna takaici da wannan harin wuce gona da iri.

Sai dai sanarwar ta zo ne bayan da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya fitar da tashi wanda ake ganin kamar gwamantin Jihar Katsina ta yi fargar jaji.

Ibrahim ya ce gwamnatin Dikko Radda a shirye take wajen ganin ta kawo karshen wannan matsalar tsaro da ta-ki-ci-ta-ki cinyewa kuma ta kara nuna bukatar da ake da ita na ganin jama’a da su ci gaba da taimaka wa jami’an tsaro da bayanai sirri domin ganin an samu nasara

Gwamna Radda dai ya sha nanata cewa ba zai taba yin sulhu da ‘yan bindiga ba, sai dai idan ‘yan bindiga sun ajiye makamansu, sun rungumi zaman lafiya.

Yanzu dai Jihar Katsina ta kara komawa wani sansanin daukar rai, inda kullum sai an kashe jama’a ko an sace, ko an kone gari da sauran nau’in zalunci ba dare ba rana.

A wani hari na ramuwar gayya kuma, rundunar sojin saman Nijeriya ta kashe ‘yan bnidiga 29 tare da ceto wadanda suka yi garkuwa da su ciki har da diyar sarkin ga-rin Ruwan Godiya.

An samu nasarar ne a wani hari ta sama da aka kai a kusa da tsaunin Bakori da Yartsintsiya a karamar hukumar Kankara ta Jihar Katsina.

Wannan farmakin ya gudana ne a matsayin na mayar da martani ga harin baya-bayan nan da aka kai a karamar hukumar Kankara a ranar Lahadi, 9 ga watan Yunin 2024, ya kuma dakile ayyukan ta’addanci a yankin.

Rundunar sojin saman Nijeriya ta bayyana cewa za ta ci gaba da hada kai da so-jojin kasa da hukumomin leken asiri don ganowa tare da kawar da masu aika ta laifuka a yankin.

Katsina
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
  • Abubakar Sulaiman
    Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
  • Abubakar Sulaiman
    Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka
  • Abubakar Sulaiman
    Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

MASU ALAKA

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
Labarai

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya
Rahotonni

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
Jihohi Goma Mafi Arahar Abinci A Nijeriya

Jihohi Goma Mafi Arahar Abinci A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.