• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Tsari: Alhazan Nijeriya Zasu Daina Daɗewa A Saudiyya

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Sabon Tsari: Alhazan Nijeriya Zasu Daina Daɗewa A Saudiyya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Alhazai ta Nijeriya NAHCON, ta aiwatar da wani sabon tsari da nufin rage yawan lokutan da alhazan Nijeriya ke yi a ƙasar Saudiyya a lokacin aikin Hajji. Shugaban hukumar Malam Jalal Arabi ne ya bayyana hakan, da yake jawabi jim kaɗan bayan isar sa filin jirgin saman Yarima Mohammed Bin Abdulaziz da ke birnin Madina, ya ce hukumar ta samu nasarar kammala jigilar alhazan Najeriya ɗari bisa ɗari zuwa Madina.

Arabi ya kara da cewa, cimma wannan buri na iya taimakawa wajen takaita zaman alhazan Najeriya baki daya, waɗanda a tarihi suke shafe tsawon lokaci a ƙasar Saudiyya, inda suke yi ta kai-kawo, yayin da aka kwashe alhazan wasu ƙasashe cikin gaggawa.

  • Hajjin Bana: Saudiyya Ta Ba NAHCON Izinin Buɗe Asibitoci Biyu A Kasar
  • Hajjin 2024: Wani Alhaji Dan Nijeriya Daga Jihar Kebbi Ya Rasu A Makkah

Arabi ya yabawa fadar shugaban ƙasa, da majalisar dokokin ƙasar, da kuma jiragen dakon fasinja bisa goyon baya da haɗin kai, wanda ke da matuƙar muhimmanci wajen samun nasarar aikin hajjin.

NAHCON ta tabbatar da cewa dukkan maniyyatan Najeriya sun kasance a ƙasar Saudiyya sa’o’i 72 kafin rufe sararin samaniyar Saudiyyar, lamarin da ya tabbata ta hanyar haɗin gwuiwar masu ruwa da tsaki na gwamnati da masu zaman kansu.

Hukumar ta NAHCON ta kuma tanadi cikakken tsarin ciyar da alhazai da kula da lafiyar alhazai a lokacin aikin hajji daga ranar 13 ga watan Yuni.

Labarai Masu Nasaba

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Arabi ya bayyana cewa hukumar ta isa Makkah domin tantancewa tare da magance duk wata matsala da aka samu dangane da masu ba da hidima, yana mai jaddada cewa ba za su yi sakaci da Alhazan Najeriya ba balle su wulakanta ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HajjMadinaMakkahNAHCON
ShareTweetSendShare
Previous Post

UNAOC Ya Yi Maraba Da Kudurin Da Sin Ta Gabatar Na Ayyana Ranar Tattaunawa Tsakanin Mabambantan Al’ummomi Ta Duniya

Next Post

Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ta Kai Yuan Triliyan 3.8 Daga Janairu Zuwa Afrilu

Related

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

2 hours ago
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

14 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

16 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

18 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

21 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

23 hours ago
Next Post
Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ta Kai Yuan Triliyan 3.8 Daga Janairu Zuwa Afrilu

Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ta Kai Yuan Triliyan 3.8 Daga Janairu Zuwa Afrilu

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.