Khalid Idris Doya">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Sabuwar Zanga-zangar #EndSARS Ta Barke A Osun, Legas Da Ibadan

by Khalid Idris Doya
December 8, 2020
in LABARAI
2 min read
#EndSARS
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Rahotonnin da su ka zo ma na a jiya na bayyana yadda wasu matasa su ka sake fitowa zanga-zangar #EndSARS a jihohin Legas, Osun da kuma Ibadan, inda su ke bayyana bukatunsu mabambanta.

Wasu matasa a ranar Litinin da su ke da alaka da kungiyar #EndSARS Moverment sun sake fitowa kan titi domin gudanar da zanga-zangar zargin rashin kyakkyawar shugabanci a Osogbo babban birnin jihar Osun.

samndaads

Masu zanga-zangar da suka fara haduwa a kan layin Ogo-Oluwa daga baya sun yi jerin gwano zuwa majalisar dokokin jihar Osun da ke kusa da sakatariyar jihar a Abere.

Matasan, wadanda suka samu jagorancin Emmanuel Adebisi, su na masu bukatar kyakkyawar shugabanci, bukatar neman a sake wadanda aka kama yayin zanga-zangar EndSARS da aka gudanar a kwanakin baya wanda ya juya zuwa tashin-tashi.

Kakakin majalisar dokokin jihar Osun, Hon. Timothy Owoeye ya shaida wa masu zanga-zangar da su kasance masu hakuri su kara wa gwamnati uzuri domin ta samu damar sauraron dukkanin bukatunsu.

Matasan wadanda suka dace kan cewa sun fito ne domin neman kyakkyawar shugabanci, sun sha alwashin cewa ba zanga-zanga ce ta tashin hankali ba, sun fito ne cikin lumana domin neman a biya musu bukatunsu, kana sun nuni da cewa basu da alaka da siyasa.

Har-ila-yau, dukka a jiyan, masu zanga-zangar EndSARS sun sun kuma fito kan tituna a jihar Legas da Ibadan babban birnin jihar Oyo.

Masu zanga-zangar wadanda suka koma kan gadar Lekki Toll Plaza inda aka zargi sojoji da bude wa masu zanga-zangar wuta a kwanakin baya.

Jami’an ‘yan sanda da soji sun kasance a yayin zanga-zangar domin tabbatar da masu yinta basu karya doka da oda ba.

Sai dai a bangaren jami’an tsaro, ‘yan sanda sun yi gargadin cewa dukkanin dukkanin wani da ya kara fitowa zanga-zangar nan duk abun da ya sameshi shine ya jawo wa kansa.

SendShareTweetShare
Previous Post

Limamin Masallacin Juma’ar Gesse Ya Tsine Wa Wanda Ya Zuba Ruwan Kashi A Masallaci

Next Post

Zulum Ya Kwashe Yini Ya Na Rabon Tallafi A Garuruwan Gwoza

RelatedPosts

Man Fetur

Kudirin Dokar Man Fetur Zai Bai Wa Nijeriya Damar Cin Gajiyar Albarkatunsa – Majalisar Dattawa

by Khalid Idris Doya
2 hours ago
0

Daga Muhammad Maitela, Shugaban majalisar dattawa, Sanata Ahmad Ibrahim Lawan...

Jobe

Ma’aikata Da ’Yan Fansho Ke Wawashe Rabin Kudin Katsina, Cewar Kwamishina Jobe

by Khalid Idris Doya
2 hours ago
0

Daga Sagir Abubukar, Kwamishinan Kasafin Kudi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki...

Rasuwar

Ana Cigaba Da Jimamin Rasuwar Mai Shari’ a Rabiu Danlami A Kano

by Khalid Idris Doya
2 hours ago
0

Daga Haruna Akarada, Ana cigaba da gudanar da ta’aziyya ta...

Next Post
Garuruwan Gwoza

Zulum Ya Kwashe Yini Ya Na Rabon Tallafi A Garuruwan Gwoza

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version