Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Sakkwatawa Sun Jaddada Goyon Baya Ga Kwankwasiyya

by Tayo Adelaja
October 23, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto

Ɗaruruwan mabiya aƙidar Kwankwasiyya a Jihar Sakkwato sun fito ƙwai da gije suka gudanar da saukar Ƙur’ani Mai Tsalki da Addu’o’in Musamman domin tunawa da ranar zagoyowar haifuwar Jagoran Kwankwasiyya na Ƙasa.

samndaads

Kwankwasawan na Sakkwato a ɗaukacin Ƙananan Hukumomi 23 sun gudanar da addu’o’in musamman ne a ranar Asabar a gidan Jagoran Kwankwasiyya na Jihar Sakkwato, Honarabul Malami Muhammad Galadanci wanda aka fi sani da Bajare.

Bayan saukar Ƙur’ani malamai ɗaya bayan ɗaya sun gabatar da addu’o’in ƙarin yawaitar shekaru masu albarka, ingantacciyar lafiya da ƙarin ɗaukaka da nasara a dukkanin lamurran da Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya sanya a gaba.

A zantawarsa da manema labarai, Jagoran Kwankwasiyya na Sakkwato Honarabul Malami Bajare ya bayyana cewar ranar muhimmiyar rana ce ta musamman da suke murnar tunawa da ayyukan alhairin da Sanata Kwankwaso ya aiwatar a karan zubin siyasar sa.

Ɗan Majalisar na Jihar Sakkwato daga mazabar Sakkwato ta Arewa ta (1) ya bayyana cewar “Kwankwaso jagora ne nagari, ya aiwatar da muhimman ayyukan raya jiha da ci-gaban al’umma a kowane fanni, ya gina Kano da Kanawa, ya samu nasarar zama na biyu a zaɓen fitar da gwani na takarar shugabancin ƙasa a jam’iyyar APC.”

Ya ce “Yadda Sakkwatawa suka fito domin taya murna ga Sanata Kwankwaso ya nuna cewar lallai tsohon Gwamnan na Kano, cikakken ɗan siyasa ne wanda ya samu gagarumar karɓuwa a faɗin ƙasa bakiɗaya.”

Wasu daga cikin mahalarta taron, Muktar Mu’azu ‘Yarsakke da Shehu Muhammad Danchadi sun bayyana cewar mulkin gaskiya da adalci da Kwankwaso ya gudanar a Kano ne dalillin da yasa suka bi jirgin siyasar sa. “Muna tare da tafiyar Kwankwasiyya 100 bisa 100 a matakin jiha da ƙasa bakidaya.” Inji su.

Fitaccen matashin ɗan kasuwa kuma ɗaya daga cikin masu tallafawa tafiyar Kwankwasiyya, Alhaji Abdulrazak Rabi’u Razi na daga cikin dimbin jama’ar da suka hakarci taron irinsa na farko a Sakkwato.

 

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Yau Gwamnoni 17 Za Su Gudanar Da Babban Taro A Legas

Next Post

Rashin Lambar BVN: Gwamnati Ta Garƙame Asusun Mutane Miliyan 15

RelatedPosts

Shata Ya Shaida Ma Ni Zan Dade A Bisa Kan Karagar Mulki – Sarkin Ningi

Shata Ya Shaida Ma Ni Zan Dade A Bisa Kan Karagar Mulki – Sarkin Ningi

by Sulaiman Ibrahim
2 days ago
0

A ranar Talata 15/2/2021 da ta gabata wakilinmu, Dokta Aliyu...

Matasa Su Dage Da Neman Ilimi Da Koyon Sana’oin Hannu – Dakta Ibrahim Agege 

Matasa Su Dage Da Neman Ilimi Da Koyon Sana’oin Hannu – Dakta Ibrahim Agege 

by Sulaiman Ibrahim
4 days ago
0

Daga Yusuf Abdullahi Yakasai Legas Neman ilmi da koyon sana’oin...

Hajiya Ummi Muhammed Ta Zama Sarauniyar Matan Jihohin Yamma

Hajiya Ummi Muhammed Ta Zama Sarauniyar Matan Jihohin Yamma

by Sulaiman Ibrahim
4 days ago
0

Daga Yusuf Abdullahi Yakasai, Legas Koda- yaushe cancanta da rashinta...

Next Post

Rashin Lambar BVN: Gwamnati Ta Garƙame Asusun Mutane Miliyan 15

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version