• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samar Wa Sarakuna Hurumi A Tsarin Mulki Zai Kyautata Ci Gaban Kasa –Sarkin Misau

by Bello Hamza
3 years ago
in Rahotonni
0
Samar Wa Sarakuna Hurumi A Tsarin Mulki Zai Kyautata Ci Gaban Kasa –Sarkin Misau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

ALHAJI AHMED SULEIMAN mni shi ne Sarkin Misau da ke jihar Bauchi a hirarsa da wakilinmu KHALID IDRIS DOYA a makon jiya, bayan kammala bikin ba shi sandar mulki da Gwamna Bala Muhammad na Jihar Bauchi ya yi a matsayin sarkin masarautar Misau na 11 da aka yi a ranar Lahadi 13 ga watan Nuwamban 2022, ya bayyana cewar samar da hurumi ga sarakuna a cikin kundin tsarin mulkin kasa zai taimaka sosai wajen kyautata cigaban kasar nan ta fuskoki daban-daban.

Duk a cikin hirar, Sarkin ya ayyana wani buri da shirye-shirye ta cikin wata gidauniya da ya fito da ita, wanda ya ce ko waddan kawai Allah ya cika masa buri shi kan ya yi nasara kuma Alhamdullahi. Ga dai hirar:

 

Ran mai martaba ya dade, a lokacin bikin mika maka sanda, gwamnan Bauchi ya yi kira ga majalisar kasa da ta samar da wani hurumi wa Sarakuna a tsarin mulkin Nijeriya yaya kuka ga wannan kiran?
Bismillahir Rahmanin Rahim. Muna godiya wa Allah madaukakin Sarki da ya ba mu sarari mu yi magana a kan wannan batun. Wannan batu ne mai muhimmanci, mecece ma’anar abin da nake nufi? Nan ana rantsar da Sarakuna a kan tsaren mulki amma ba su cikin shi din. Rantsuwar da aka ba mu muka yi ana cewa za mu bi umarnin tsarin mulki din Nijeriya, kundun mulkin kasa gabaki daya. Amma kuma ba mu ciki, don haka gaskiya akwai matsala a ciki. Kuma ina tabbatar maku cewa majalisar sarakuna ta kasa gabadaya sun kafa kwamiti har an je majalisar dattawa a kan wannan batun, muna dai rokon Allah ya sa a duba wannan al’amarin a kuma yi abin da ya dace. Ba za ka ce mutum kana son ya yi amfani ba, kuma ka ce ba ya da wani amfani ba duk a lokaci guda.

Wanne alfanu ake ganin wannan abin zai yi idan aka samu nasarar hakan?
Zai bai wa kowa damar ya yi amfani da mukamin da Allah ya ba shi domin a kawo zaman lafiya da cigaba a wannan kasar.

Labarai Masu Nasaba

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

Wasu na ganin ko ba a yi wannan ba, ku Sarakuna ayyukan da kuke yi ma sun isheku na sasanta tsakanin jama’a, zamantakewa da bada shawarwari kusan wadannan ayyukan da kuke yi kamar ma baku ma da lokacin kanku?
Eh fadi ake yi, in ka samu tushe, ya zamana kana da tushen yin magana to ya fi alkairi. Wannan kam ai fada ake yi, za ka iya kiran talaka ya ce ai shi ba abin da aka masa kuma haka yake, tun da ba kada wani hurumi a cikin dokokin kasar nan.

Ya mai martaba zai kamanta rayuwarsa a baya da baya kan kujera da yanzu lokacin da yake sarki, kuma mene ne bambancin aikin sarauta da aikin gwamnati ganin cewa ka goge da dadewa a bangaren aikin gwamnati?
Alhamdullahi wannan abu ne wanda na yi bayaninsa a lokacin da Allah (Subhanahu Wata’ala) ya sa aka bani ‘Sanda’, banbancin shi ne yanzu al’ummar gaba daya suna kallonka ne kai kadai, da kana aikin gwamnati, kana karkashin wani ne sai abin da aka fada ko shawarar da za ka bayar, amma yanzu duk batun na wajenka, karshen maganar ta zo wajenka. Saboda haka wannan nauyin yana da muhimmanci yana da kuma ban tsoro, sai dai muna rokon Allah ya bamu ikon cinye wannan jarabawar.

Mai martaba ya ce ba abin da yake so kamar ya ga cewa ya bar wani abu da koda bayan baya nan a tuna da shi, ko me kake nufi da wannan?
Babu wani da baya son tarihi, babu wanda zai so a manta da tarihinsa, in ka san amfanin tarihi to maganar da nake yi kenan. A tarihince a san ka yi abu kaza ka yi abu kaza, wannan ne zai sa ba za a taba mantawa da kai ba.

Yanzu akwai wasu ayyukan da Sarki yake son ya maida hankali wajen ganin ya cimma su a nan gaba a masarautar shi?
Babba ma kuwa, manya-manya ma kuwa. Amma alhamudllahi duk sun dunkula ne yanzu a kan wata gidauniya da muka saka ta raya kasar Misau wato ‘MEDEP’ a takaice, wannan gidauniyar tana da sassa har guda goma, kama daga wasa, kiwon lafiya, batun anfanin, ilimi da dai sauransu. In da a ce zan samu wannan gidauniyar ta zauna da gindinta ni Alhamdullahi na samu biyan bukatata.

Wannan gidauniyar za ta kawo sauye-sauyen da kake bukata kenan?
Insha Allahu, kuma ku taya mu da addu’a muma muna kai.

Ranka dade ko za ka mana karin haske kan wannan gidauniyar ta yaya za ta kasance kuma kai ne shugabanta, ganin cewa ka ce burinka na kanta?
Kwarai da gaske burina yana kai, amma ni zan ce kamar ni shugaba ne marar iko, amma akwai wadanda suke gudanar da ita, kuma kowani sashi yana da wanda yake shugantarsa. Misali, ilimi, sai muka dauko Farfesa Auwal Uba mukaddashin shugaban jami’ar Gadau sai yake kula da sha’anin da duk ya shafi ilimi, kama daga samun guraben karatu na yara da samun dukkanin agajin da suka shafi ilimi har taimakawa ga wadanda basu da hali wajen ganin an sama musu yadda za su yi karatun.
Sannan a bangaren kiwon lafiya, akwai Dakta Alkali wanda wata kila ka sanshi, ya matsayin Associate Professor ne yana asibitin kwararru da ke Bauchi to shi kuma yana kula da sashin lafiya. Haka duk sauran bangarorin muka yi domin ganin an samu nasara. In ka lura kafin a bani Sanda akwai gudunmawar da wannan gidauniyar ta bayar, ina tabbatar maka a kalla mutane 400 an duba lafiyarsu an basu magani a sanadin bada wannan sandar haka dabbobi da sauransu duk a sanadiyyar bada wannan sandar kawai. Don haka wannan gidauniyar tamu tana da fadi idan aka samu, ba wai muna yi mu cire aikin gwamnati ba ne, a’a muna yi ne don mu taimaka wa jama’anmu ne, mu taimaka a inda gwamnati ta dan kasa sai mu bada tamu gudunmawar.

Muna da masaniyar cewa duk a karkashin wannan gidauniyar an kaddamar da banki na al’umma, ta yaya za ta gudanar da aikinta za ta bayar da bashi da ruwa ne ko za ta bayar da bashi ba tare da ruwa ba kuma su waye za su mora masu karamin karfi?
Ina godiya da wannan tambayar taka, kuma ina son na jawo hankalin al’ummar karamar hukumar Misau da dukkanin wadanda suke da sha’awar kawo cigaba. Muhimmin abin da ake nufi shi ne wannan bankin ba na ruwa ba ne, shi ya sa aka kirashi ‘Ba riba a ciki- (Ba ruwa)’ za ka bada jarinka ko za ka je ka karbi bashi bisa abun da ka samu in riba ce ku ci ku raba da bankin tare in ma faduwa ce haka za ku raba tare. Shi ya sa aka ce wa bankin ‘Islamic Bank’ yana bin ka’idoji na addinin musulunci don haka babu zancen riba a ciki, kuma muna fatan yadda aka yi shi ya tabbata muna fatan ya zama alkairi ga kasar baki daya.

A zantawar da muka yi da al’ummar masarautar Misau kafin a baka sandar mulki, ka yi kokarin hada kan al’umma da wasu da suka samu sabani duk an sasantasu ko wane karin bayani za ka yi a kan wannan?
Ai abu mai sauki ne, tsintsiya daya bata shara. In ka hada kan jama’a kowa da irin baiwar da Allah ya yi masa sai ka ga an samu cigaba shi ne dalili kuma shi ne makasudi domin kasar tamu ba girma take da shi ba, idan muka hada kai za mu fi samun nasara, wannan dalilin ne ya sa muka dauki wannan matakin na sasanta kowa da hada kan kowa.

Duk abun da ake nema shi ne a kau da talauci ya zama kowa na zaune lafiya, yana da abun da zai ci da abun da zai yi ba tare da tashin hankali ba.

A wajen baka sandar girma an ga al’umma masu dumbin yawa don za a iya cewa hakan ya shiga cikin tarihin masarautar nan, ka ji dadi kuwa a ranka?
Alhamdullahi ba wanda zai ga jama’a irin wannan ba zai yi godiya wa Allah madaukakin sarki ba. Muna godiya wa kowa da kowa, mun kuma ji dadi da Allah ya maida kowa gidasa lafiya.
Mun gode.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dansanda Wakilin Nijeriya, Ne Akwai Bukatar Girmama Shi – Osinbajo

Next Post

Za A Yi Jana’izar Tsohon Shugaban Jami’ar ABU, Farfesa Abdullahi Mahdi Da Yammacin Ranar Asabar

Related

'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

2 days ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

1 week ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

1 week ago
Akwai Bukatar Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Jihar Legas Wajen Bunkasa Albarkatun Fatu
Rahotonni

Akwai Bukatar Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Jihar Legas Wajen Bunkasa Albarkatun Fatu

1 week ago
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya
Rahotonni

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

2 weeks ago
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari
Rahotonni

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

2 weeks ago
Next Post
Za A Yi Jana’izar Tsohon Shugaban Jami’ar ABU, Farfesa Abdullahi Mahdi Da Yammacin Ranar Asabar

Za A Yi Jana'izar Tsohon Shugaban Jami'ar ABU, Farfesa Abdullahi Mahdi Da Yammacin Ranar Asabar

LABARAI MASU NASABA

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

September 6, 2025
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

September 6, 2025
Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

September 6, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

September 6, 2025
Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

September 6, 2025
Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

September 6, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

September 6, 2025
Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

September 6, 2025
Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha

Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha

September 6, 2025
‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.