• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

by Abubakar Sulaiman
3 weeks ago
in Nishadi
0
Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ɗaya daga cikin matasan jarumai a Masana’antar Kannywood, wanda a yanzu haka ludayinsu yake kan dawo, Baba Sadiƙ ko kuma Auwal Labarina, ya bayyana cewa; samun kuɗi ya fi samun daukaka matuƙar wahala a masana’antarsu ta shirya fina-finan Hausa. 

Sadiƙ, a wata hira da ya yi da jarumar Kannywood, Hadiza Gabon a cikin shirinta mai suna ‘Gabon’s Room Talk Show’, ya bayyana cewa; akwai lokacin da ya tafi karɓo lambar yabo ta gwarzon jarumi mai tasowa, amma a kafa ya dawo gida riƙe da lambar yabon, sakamakon rashin abin hawa a wancan lokaci.

“A lokacin da na fito a cikin shiri mai dogon zango na Kwana Casa’in, na samu kyautar lambar yabo ta gwarzon jarumi mai tasowa, wanda na je na karɓa, amma bayan na fito daga wajen taron, sakamakon rashin abin hawa; a ƙarshe da ƙafa na taka har zuwa gidanmu”, in ji Sadiƙ. 

  • Shirin Bunƙasa Ilmi A Kano: Yadda Gwamnatin Abba Gida-gida Ta Tura Dalibai 1001 Karatu Kasashen Waje
  • Kasar Sin Da Namibia Sun Sha Alwashin Daukaka Hadin Gwiwarsu Na Cin Moriyar Juna

Ya ƙara da cewa, yanzu ya fi mayar da hankali a kan abubuwan da yake ɗorawa a shafukansa na sada zumunta, musamman ‘Facebook’, da ake biyan sa maƙudan kudaɗe.

Sadiƙ ya ci gaba da cewa, samun daukaka babu kuɗi matsala ce babba, domin kuwa idan ka samu daukaka, ba kowace irin sana’a za ka iya yi ba; domin duk abin da ka yi, idanun mutane yana kanka, ni a lokacin da nake harkokina kafin na samu wannan daukaka, daukar hoto na ke yi; sannan kuma ina tuƙa Adaidaita Sahu, amma bayan na samu daukaka an fara sani na, sai na ji ba zan iya ci gaba da wadannan sana’o’i ba, duk da cewa kuma ba ni da kuɗi, amma sai naji a raina cewa; ba zan iya ci gaba da yin su ba, kamar yadda ya bayyana.

Labarai Masu Nasaba

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

Auwalu Labarina, wanda ke cikin matasa jarumai da tauraruwarsu ke haskawa a Masana’antar Kannywood, ya fito a manyan fina-finai da dama da suka hada da darasi, Kwana Casa’in, Gidan Sarauta da kuma shirin nan na Labarina, ya kuma samu kyautuka da dama da suka danganci wannan sana’a tasa ta fim a lokuta daban-daban. Kazalika, ya yi nuni da cewa; yanzu mafi akasarin mutane, ba sa son abin da zai taimaka musu; kawai dai sun fi mayar da hankali wajen sharholiya iri-iri.

da yake amsa tambaya a kan me yasa ya fi mayar da hankali wajen ɗora bidiyo, musamman na jarumai mata a Masana’antar Kannywood a shafukansa na sada zumunta, musamman kuma ‘Facebook’? Sai Baba Sadiƙ ya ce; ba komai ba ne ya jawo haka illa tsarin biyan kuɗi (Monetization) da kamfanin ‘Facebook’ ya fito da shi, domin yanzu na zage damtse ina neman kuɗi, ba tare da wasa ba, kafin yanzu ina ɗora bidiyon shawarwarin da za su taimaki al’ummarmu, amma kuma su mutanen da ke kallo sai na ga kamar ba su da ra’ayin ire-iren wadannan abubuwa da nake ɗorawa a shafin nawa.

Bayan daukar tsawon lokaci ina yin wadannan bidiyoyi na shawarwari, sai na yanke shawarar yin watsi da shi na koma ɗora bidiyoyina tare da abokan aikina ƴan fim, musamman idan muka haɗu a lokeshan na daukar fim, daga wannan lokaci ne sai na ga yawan ‘likes’ da ‘comments’ ɗin da mutane suke yi a shafi nawa ya ƙaru sosai, sannan adadin mutanen da ke ziyartar shafin shi ma ya ƙaru, sai kuma ga shi ina samun dalar Amurka fiye da 300 a duk lokacin da na ɗora ire-iren wadannan bidiyoyi nawa a shafin, sai kawai na ci gaba da yin hakan.

daga wancan lokacin da na fara ɗora bidiyoyi nawa tare da jarumai mata ƴan fim da sauran sanannun mata, na kan samu aƙalla Naira Miliyan biyar zuwa 10 a duk wata daga abin da ‘Facebook’ ke biya na, don haka yanzu na gane cewa; talauci ne matsalata a lokacin baya, kuma Alhamdulillahi yanzu na fara samun sauƙin wannan matsala a halin yanzu da hanyoyin samu suka ƙara buɗe min, in ji shi.

daga ƙarshe, Baba Sadiƙ ya ce; kamata ya yi a ce matasa su mayar da hankali wajen abubuwan da za su taimake su a rayuwarsu, ba su tsaya suna faɗin aibin wani ko yaba burgewar wani ba, yanzu matasa da dama su kan ɓata lokacin su wajen aibata wani idan ya yi kuskure, ko kuma yabon wanda bai ma san suna yi ba, ba komai ne ke jawo irin haka ba; illa rashin aiki da mafi yawancin matasa ke fama da shi, a maimakon ka tsaya cewa; Rarara ya sai sabuwar mota ko kuma Hadiza Gabon ta yi ‘Slimming’ gara ka je ka nemi abin da za ka rufa wa kanka asiri, kamar yadda ya shawarci matasa.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kannywood
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

Next Post

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

Related

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah
Nishadi

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

2 days ago
Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya
Nishadi

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

1 week ago
Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu
Nishadi

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

2 weeks ago
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya
Nishadi

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

2 weeks ago
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna
Nishadi

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

2 weeks ago
Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami
Nishadi

Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

3 weeks ago
Next Post
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da 'Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

LABARAI MASU NASABA

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

August 25, 2025
Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.