• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

by Abubakar Sulaiman
6 hours ago
in Nishadi
0
Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ɗaya daga cikin matasan jarumai a Masana’antar Kannywood, wanda a yanzu haka ludayinsu yake kan dawo, Baba Sadiƙ ko kuma Auwal Labarina, ya bayyana cewa; samun kuɗi ya fi samun daukaka matuƙar wahala a masana’antarsu ta shirya fina-finan Hausa. 

Sadiƙ, a wata hira da ya yi da jarumar Kannywood, Hadiza Gabon a cikin shirinta mai suna ‘Gabon’s Room Talk Show’, ya bayyana cewa; akwai lokacin da ya tafi karɓo lambar yabo ta gwarzon jarumi mai tasowa, amma a kafa ya dawo gida riƙe da lambar yabon, sakamakon rashin abin hawa a wancan lokaci.

“A lokacin da na fito a cikin shiri mai dogon zango na Kwana Casa’in, na samu kyautar lambar yabo ta gwarzon jarumi mai tasowa, wanda na je na karɓa, amma bayan na fito daga wajen taron, sakamakon rashin abin hawa; a ƙarshe da ƙafa na taka har zuwa gidanmu”, in ji Sadiƙ. 

  • Shirin Bunƙasa Ilmi A Kano: Yadda Gwamnatin Abba Gida-gida Ta Tura Dalibai 1001 Karatu Kasashen Waje
  • Kasar Sin Da Namibia Sun Sha Alwashin Daukaka Hadin Gwiwarsu Na Cin Moriyar Juna

Ya ƙara da cewa, yanzu ya fi mayar da hankali a kan abubuwan da yake ɗorawa a shafukansa na sada zumunta, musamman ‘Facebook’, da ake biyan sa maƙudan kudaɗe.

Sadiƙ ya ci gaba da cewa, samun daukaka babu kuɗi matsala ce babba, domin kuwa idan ka samu daukaka, ba kowace irin sana’a za ka iya yi ba; domin duk abin da ka yi, idanun mutane yana kanka, ni a lokacin da nake harkokina kafin na samu wannan daukaka, daukar hoto na ke yi; sannan kuma ina tuƙa Adaidaita Sahu, amma bayan na samu daukaka an fara sani na, sai na ji ba zan iya ci gaba da wadannan sana’o’i ba, duk da cewa kuma ba ni da kuɗi, amma sai naji a raina cewa; ba zan iya ci gaba da yin su ba, kamar yadda ya bayyana.

Labarai Masu Nasaba

Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Auwalu Labarina, wanda ke cikin matasa jarumai da tauraruwarsu ke haskawa a Masana’antar Kannywood, ya fito a manyan fina-finai da dama da suka hada da darasi, Kwana Casa’in, Gidan Sarauta da kuma shirin nan na Labarina, ya kuma samu kyautuka da dama da suka danganci wannan sana’a tasa ta fim a lokuta daban-daban. Kazalika, ya yi nuni da cewa; yanzu mafi akasarin mutane, ba sa son abin da zai taimaka musu; kawai dai sun fi mayar da hankali wajen sharholiya iri-iri.

da yake amsa tambaya a kan me yasa ya fi mayar da hankali wajen ɗora bidiyo, musamman na jarumai mata a Masana’antar Kannywood a shafukansa na sada zumunta, musamman kuma ‘Facebook’? Sai Baba Sadiƙ ya ce; ba komai ba ne ya jawo haka illa tsarin biyan kuɗi (Monetization) da kamfanin ‘Facebook’ ya fito da shi, domin yanzu na zage damtse ina neman kuɗi, ba tare da wasa ba, kafin yanzu ina ɗora bidiyon shawarwarin da za su taimaki al’ummarmu, amma kuma su mutanen da ke kallo sai na ga kamar ba su da ra’ayin ire-iren wadannan abubuwa da nake ɗorawa a shafin nawa.

Bayan daukar tsawon lokaci ina yin wadannan bidiyoyi na shawarwari, sai na yanke shawarar yin watsi da shi na koma ɗora bidiyoyina tare da abokan aikina ƴan fim, musamman idan muka haɗu a lokeshan na daukar fim, daga wannan lokaci ne sai na ga yawan ‘likes’ da ‘comments’ ɗin da mutane suke yi a shafi nawa ya ƙaru sosai, sannan adadin mutanen da ke ziyartar shafin shi ma ya ƙaru, sai kuma ga shi ina samun dalar Amurka fiye da 300 a duk lokacin da na ɗora ire-iren wadannan bidiyoyi nawa a shafin, sai kawai na ci gaba da yin hakan.

daga wancan lokacin da na fara ɗora bidiyoyi nawa tare da jarumai mata ƴan fim da sauran sanannun mata, na kan samu aƙalla Naira Miliyan biyar zuwa 10 a duk wata daga abin da ‘Facebook’ ke biya na, don haka yanzu na gane cewa; talauci ne matsalata a lokacin baya, kuma Alhamdulillahi yanzu na fara samun sauƙin wannan matsala a halin yanzu da hanyoyin samu suka ƙara buɗe min, in ji shi.

daga ƙarshe, Baba Sadiƙ ya ce; kamata ya yi a ce matasa su mayar da hankali wajen abubuwan da za su taimake su a rayuwarsu, ba su tsaya suna faɗin aibin wani ko yaba burgewar wani ba, yanzu matasa da dama su kan ɓata lokacin su wajen aibata wani idan ya yi kuskure, ko kuma yabon wanda bai ma san suna yi ba, ba komai ne ke jawo irin haka ba; illa rashin aiki da mafi yawancin matasa ke fama da shi, a maimakon ka tsaya cewa; Rarara ya sai sabuwar mota ko kuma Hadiza Gabon ta yi ‘Slimming’ gara ka je ka nemi abin da za ka rufa wa kanka asiri, kamar yadda ya shawarci matasa.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kannywood
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

Next Post

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

Related

Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami
Nishadi

Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

10 hours ago
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa
Nishadi

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

1 week ago
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa
Nishadi

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

3 weeks ago
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau
Nishadi

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

4 weeks ago
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

4 weeks ago
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda
Nishadi

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

1 month ago
Next Post
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da 'Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

LABARAI MASU NASABA

Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

August 3, 2025
Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

August 3, 2025
Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

August 3, 2025
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

August 3, 2025
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

August 3, 2025
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

August 3, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

August 3, 2025
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

August 3, 2025
Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

August 3, 2025
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

August 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.