Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home Uncategorized

Sanata Ya Raba Kayan Asibiti Na Milliyoyin Naira A Kebbi Ta Arewa

by Muhammad
February 23, 2021
in Uncategorized
1 min read
Asibiti
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Jamil Gulma Birnin,

A cikin shirin sa na inganta lafiyar al’umma a mazabarsa ta gundumar Kebbi ta Arewa Sanata Dokta Yahaya Abdullahi shugaban masu rinjaye a majalisar dattawa ya raba kayan aikin asibiti na milliyoyin nairori a kananan asibitoci.

samndaads

Alhaji Abubakar Musa Argungu wanda shi ne ya wakilci Sanata Dokta Yahaya Abdullahi a wajen bukin rabon kayan ya bayyana samun wakilci irin na Sanata shi ne burin kowace al’umma saboda ba kansa ya je azurtawa ko dimama kujera ya je yi a majalisar dattawa ba ya je ne don wakiltar al’ummarsa kuma ba shakka ya isarda wakilci saboda tun tarihin siyasa a iya sanin sa ba a taba samun irin wannan wakilcin ba.

Ya yi kira ga jami’an da aka hannantawa wadannan kayan da su ji tsoron Allah su yi amfani da su yadda ya kamata kada su bi wadansu hanyoyi da bai kamata ba saboda idan ana yin haka da kayan ba su iso hannunsu ba.

Kayan dai sun hada da gadaje da katifu, tebura da kujeri, kayan awo dabam-daban, injinan wuta, Firjin, Babura, kabot-kabot, kujerin ofis, bokitai da kayan tsaftace asibiti da dai sauransu.

Taron dai ya sami halartar yansiyasa, ma’aikatan hukumar lafiya a matakin farko na kasa da jiha, shugabannin sashen lafiya daga kananan hukumomin Argungu, Augie Arewa, Dandi, Bagudo da Suru.

SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnatin Kano Ta Samar Asibiti A Kwalejin Kimiyya

Next Post

Garkuwa Da Mutane: Gwamnan Neja Ya Karbi Fasinjojin NSTA 53

RelatedPosts

Mukabalar

Mukabalar Malamai: Ina Son Gwamnan Kano Ya Fara Ba Ni Damar Ganawa – Sheikh Kasiyuni

by Muhammad
3 days ago
0

Daga Mustapha Ibrahim, “Ganin yadda Gwamnan Jihar Kano, Dr. Abdullahi...

Billiri

Yadda Rikicin Billiri Kan Zaben Sabon Sarki Ya Ta’azzara

by Muhammad
4 days ago
0

Gwamnan Gombe Ya Ziyarci Garin Don Duba Asarar Da Aka...

2023: Har Yanzu Ba Mu Ayyana Dan Takarar Shugaban Kasa Ba, Inji PDP

2023: Har Yanzu Ba Mu Ayyana Dan Takarar Shugaban Kasa Ba, Inji PDP

by Sulaiman Ibrahim
1 week ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim Jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ta karyata...

Next Post

Garkuwa Da Mutane: Gwamnan Neja Ya Karbi Fasinjojin NSTA 53

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version