Jamil Gulma">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Sanata Yahaya Abdullahi Ya Ja Kunnen Matasa Su Kasance Jakadu Nagari

by Jamil Gulma
December 9, 2020
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Sanata Yahaya Abdullahi
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Sanata mai wakiltar Kebbi ta Arewa kuma shugaban masu rinjaye a majalisar dattawa Sanata Dr Yahaya Abubakar Abdullahi ya ja kunnen matasa da su kasance jekadu nagari.

Wannan bayanin ya fito daga bakin mataimaki kan al’amurra na musamman Alhaji Ayuba Umar a garin Birnin Kebbi jiya Talata lokacin da tawagar wakilan Sanatan suka ziyarci matasa masu rubuta jarabawar shiga ayukan shige da fice, kashe gobara, gidan gyara halinka da kuma aikin tsaro na farinkaya da suka fito daga gundumar mazabar Kebbi ta Arewa da suka kumshi kananan hukumomin Argungu, Augie, Arewa, Dandi, Suru da kuma Bagudo.

samndaads

Alhaji Ayuba Umar ya ce maigirma Sanata yana yi musu fatar alheri da kuma ba su kwarin gwiwa wajen shiga gwagwarmayar neman kowane irin aiki idan aka nemi matasa su shiga.

Ya cigaba da cewa kamar yadda aka san yayan jihar Kebbi da jarunta a duk inda suka shiga a nan ma yana fatar ba za a bar su a haha ba kuma don Allah su zamo jekadu nagari musamman a wannan lokacin da kasar nan ke fama da matsalar tsaro.

Usman Lena daga karamar hukumar mulki ta Arewa a madadin sauran matasan ya yabawa Sanata Dr Yahaya Abubakar Abdullahi bisa a kulawarsa ga mutanen da ya ke wakilta wanda suna sane da irin kokarin da ya ke yi a duk lokacin da irin wannan ta taso, an yi daukar sojoji ya turo wakilansa, an yi daukar dalibai a makarantun gaba da sakandare musamman jami’o’i bayan ya raba fom-fom na sharefage ga matasa har wa yau ya turo wakilansa don bin dugin samun gurabun karatu ga daliban, ya aiko an koyawa matasa maza da maza sana’o’i don su dogara da kawunansu da dai sauran abubuwa da yawa saboda haka muna yi masa fatar alheri.

Ya yi kira ga yansiyasa musamman zababbu da su yi koyi da shi kada su ba su fafa gora sai ranar tafiya.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

INEC Za Ta Kammala Zaben Dan Majalisa Yau A Zamfara

Next Post

Nasarar Da Gwamna Ganduje Ya Samu Ta Al’ummar Kano Ce – Abubakar Zakari

RelatedPosts

Ingantaccen zabe

Aniyar Ganduje Ce Ta Haifar Da Ingantaccen Zabe A Kano – Yusif Ali

by Jamil Gulma
12 hours ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, An bayyana cewa, kyakkyawar aniyar Gwamna...

Kaduna

Sojoji Sun Yi Wa ‘Yan Bindiga Kwanton Bauna A Kaduna

by Jamil Gulma
12 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Sojojin da ke karkashin ‘Operation Thunder...

Farar Hula

Hankula Sun Tashi A Maiduguri Bayan Babbaka Sojan Da Ya Harbi Farar Hula Hudu

by Jamil Gulma
12 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Mutanen Maiduguri sun shiga tararrabi bayan...

Next Post
Abubakar Zakari

Nasarar Da Gwamna Ganduje Ya Samu Ta Al'ummar Kano Ce – Abubakar Zakari

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version