ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Saudiyya Ta Sake Sassauta Dokokin Ta’ammali Da Barasa A Cikin Kasar

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
3 weeks ago
Saudiyya

Saudiyya Arebiya ta fadada damar da mutane ke da ita na ciniki da kuma kwankwadar barasa ga mazauna kasar wadanda ba Musulmai, abin da ke nufin a yanzu an kara yawan shagunan hada-hadar barasar sabanin guda daya tal da ake da shi, wanda ke a birnin Riyadh fadar gwamnatii da aka samar tun farko domin jami’an Diplomasiyya.

Rahotanni sun ce cikin sirrin gwamnatin kasar Saudiyya ta yi aikin fadada shagunan musamman a unguwannin jami’an diplomasiyyar da ke zaune a birnin na Riyadh.

  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Uku Bayan Rufe Makarantu A Adamawa
  • Dogaro Da Noman Gargajiya Kadai Ba Zai Iya Wadatar Da  Nijeriya Ba – Farfesa Rabi’u

Ana ganin cewa wannan mataki baya rasa nasaba da yadda sannu hankali damar sha da kuma samun barasa cikin sauki ke bai wa ‘yan yawon bude ido kwarin gwiwar ziyartar kasar ta yankin Gulf mai tsauraran dokokin addinin Islama da suka haramta kusantar barasa.

ADVERTISEMENT

Mahukuntan Saudiyya dai na bukatar janyo hankalin baki ‘yan yawon bude ido akalla miliyan 150 nan da shekarar 2030, yayin da ake ganin yadda kasar ke ci gaba da zuba jari a bangarorin otel-otel da wuraren shakatawa.

Bayanai sun ce baya ga jami’an diplomasiyya, ma’aikata ‘yan kasashen ketare da ke aiki kuma suke samun albashin da ya kai SAR dubu 80 dai-dai da Dalar Amurka dubu 21 a wata na damar siya da kuma shan barasar amma bisa sanya idanun gwamnati.

LABARAI MASU NASABA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Rahotanni sun ce a yanzu al’ummar kasashen ketare mazauna Saudiyya da a baya ke da sassaucin sarrafa barasar ta gargajiya a gida su kuma sha abinsu amma ba tare da sayarwa ba, na da damar neman lasisin hukuma don fara cinikin barasar a hukumance.

Matakin na sassaucin sha da ta’ammali da barasar na a karkashin tsare-tsaren gwamnatin Saudiya na fasalta dokokinta don yin dai dai da zamani karkashin shirin BISION 2030 da Yarima mai jiran gado na Saudiyan ke jagoranta, wanda ya sahale bude gidajen kallo na Cinema da kuma bai wa mata damar tuki da ma bunkasa bangarorin nishadi da yawon bude ido.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Next Post
Hong Kong Ta Yi Jimamin Wadanda Gobara Ta Shafa Ta Hanyar Saukar Da Tutoci

Hong Kong Ta Yi Jimamin Wadanda Gobara Ta Shafa Ta Hanyar Saukar Da Tutoci

LABARAI MASU NASABA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.