ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Uku Bayan Rufe Makarantu A Adamawa

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
6 months ago
Adamawa

Bayan kasa da awanni 24 da gwamnatin Jihar Adamawa ta rufe makarantun kwana, ‘yansanda sun kama masu satar mutane uku a jihar.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar a Adamawa, SP Suleiman Nguroje, ya fitar a ranar Lahadi, ya bayyana cewa kamun ya biyo bayan korafi da aka samu a ranar 19 ga Nuwamba, 2025, daga wani mazaunin wani kauye a Karamar Hukumar Song, cewa a ranar 18 ga Nuwamba, 2025, ya samu kiran waya ta barazana daga wani da ba a san ko waye ba.

  • Dogaro Da Noman Gargajiya Kadai Ba Zai Iya Wadatar Da  Nijeriya Ba – Farfesa Rabi’u
  • Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka

A cewar sanarwar, mai kiran waya ya nemi a biya shi Naira miliyan 2 ko kuma a yi garkuwa da shi har ma da yiwuwar a kashe shi.

ADVERTISEMENT

“Bayan karbar korafin, kwamishinan ‘yansanda, Dankombo Morris, ya umurci Mataimakin Kwamishinan ‘Yansanda na Sashen Bincike na Jiha, Yola, da ya gudanar da bincike tare da tabbatar da kama masu laifin,” in ji shi.

Mutanen da aka kama su ne Ahmadu Alhaji Halilu, mai shekara 24; Adamu Buba Balejo, mai shekara 21; da Hassan Alhaji Liman, duk maza daga Gundumar Malabu a Karamar Hukumar Fufore.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi

NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano

“Yayin binciken, wadannan mutum uku sun amsa laifinsu. An kuma samu katin SIM da aka yi amfani da shi wajen aikata laifin, wanda za a dauka a matsayin hujja.”

Kwamandan ‘yansanda, wanda ya yaba wa jami’an da suka shiga aikin, ya tabbatar da jajircewar rundunar wajen ganowa da kama, da gurfanar da masu laifi a fadin jihar.

Gwamnatin Jihar Adamawa ta rufe dukkan makarantun kwana na gwamnati da masu zaman kansu a jihar a ranar Asabar.

A cikin wata sanarwa da kwamishinan Ilimi da Ci gaban Dan’Adam, Dr Umar Pella, ya sanyawa hannu, an bayyana cewa matakin Fintiri na rufe makarantun kwana yana nufin kauce wa faruwar irin sace dalibai da aka yi a Jihohin Neja da Kebbi.

“Dangane da kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta a yanzu, musamman abin da ya faru da dalibai a Jihohin Neja da Kebbi, an lura da takaici cewa makasudin masu laifi su ne makarantun sakandire na kwana.

“Idan aka yi la’akari da wannan mummunan yanayi a kasar, Mai Girma Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Fintiri, ya umarce ni da in rufe dukkan makarantun kwana a fadin jihar, ko makarantu na gwamnati ne ko masu zaman kansu.”

Ya kara da cewa, “Dukansu su kasance makarantun jeka da ka dawo a halin yanzu. Saboda haka, ta wannan wasika, dukkan shugabanni da masu mallakar makarantu na gwamnati da na masu zaman kansu su mayar da dalibansu jeka ka dawo.”

Adamawa
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya
Adamawa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

MASU ALAKA

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi

June 1, 2026
NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
Tsaro

NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano

May 31, 2026
Yadda Muka Kashe Masu Garkuwa 4 Da Suke Shirin Kai Hari Kan Attajirai A Legas —CP
Tsaro

Yadda Muka Kashe Masu Garkuwa 4 Da Suke Shirin Kai Hari Kan Attajirai A Legas —CP

May 31, 2026
Next Post
Barau Ya Gargaɗi Gwamna Abba Kan Siyasantar Da Batun Tsaro A Kano

Barau Ya Gargaɗi Gwamna Abba Kan Siyasantar Da Batun Tsaro A Kano

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.