• English
  • Business News
Monday, June 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sauyin Kudi: Gwamnonin APC Sun Bukaci Buhari Da CBN Su Mutunta Umarnin Kotun Koli

by Sulaiman and Abubakar Abba
2 years ago
in Siyasa
0
Sauyin Kudi: Gwamnonin APC Sun Bukaci Buhari Da CBN Su Mutunta Umarnin Kotun Koli
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar APC ta yi kira ga Babban Lauyan gwamnatin tarayya, SAN Abubakar Malami da gwamnan babban bankin Nijeriya CBN,  Godwin Emefiele, da su girmama umarnin kotun koli akan maganar sauya sabbin takardun kudade .  

 

Shugaban APC na kasa, sanata Abdullahi Adamu ya ce, wannan kiran na daya daga cikin matsayar da gwamonin APC da kwamitin zartarwa na jam’iyyar suka cimma a taron su na gaggawa da suka gudanar a jiya lahadi a Abuja.

  • ‘Rikicin Sauya Kudi’: Adamu Da Gwamnonin APC Sun Shiga Taron Gaggawa Na Sirri A Abuja

Adamu wanda ya shedawa manema labarai hakan jim kadan bayan kammala taron sirrin  ya kuma yi kira ga shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya sa baki acikin maganar don lalubo mafita akan matsalar da tsarin na sauya kudaden ta janyo.

 

Labarai Masu Nasaba

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

A hukuncin da kotun koli ta yanke, ta umarci CBN da gwamnatin tarayya da su dakatar da wa’adin ranar 10 ga watan Fabrairu na daina amfani da takardun kudaden naira 200, 500 da 1000 har sai kotun ta yanke hukunci a ranar 22 ga watan fabrairu 2023.

 

Sai dai, shugaban kasa Muhammadu Buhari a ranar 16 ga watan janairun 2023 ya sanar da cewa, naira 200 ce kawai za ta ci gaba da zama halartacciyar takardar kudi da za a ci gaba da amfani da ita har zuwa ranar 10 ga watan Afirilun 2023, inda kuma tsohuwar takardun kudi na naira 500 da naira 1000 suka zama tarihi a kasar.

 

Gwamonin Kaduna, Kogi, Jigawa, Yobe, Zamfara, Filato, Ekiti, Neja, Kebbi, Gombe, Lagos da kuma na Nasarawa ciki har da mataimakan gwamnonin Imo da Katsina, duk sun halarci zaman ganawar sirrin.

 

Dan takarar shugaban kasa a jamiyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu, shi ma ya halarci ganawar wacce aka shafe kimanin sa’o’i uku ana yi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

INEC Ta Gayyaci ‘Yan Takara Su Sake Rattaba Hannu Kan Zaman Lafiya Ranar Laraba

Next Post

ISWAP Sun Saki Likitan Da Suka Sace A Borno Bayan Kwashe Watanni 11 Suna Rike Da Shi

Related

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike
Siyasa

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

7 hours ago
Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya
Siyasa

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

3 days ago
‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027
Siyasa

‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027

1 week ago
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi
Labarai

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

2 weeks ago
PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe
Siyasa

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

2 weeks ago
Kyakkyawan Tunanin Kwankwaso Na Kafa Jami’ar Kimiyya Ta Wudil Ta Zama Alkairi Ga Al’umma – Alhaji Abdukadir
Ilimi

Kyakkyawan Tunanin Kwankwaso Na Kafa Jami’ar Kimiyya Ta Wudil Ta Zama Alkairi Ga Al’umma – Alhaji Abdukadir

2 weeks ago
Next Post
ISWAP Sun Saki Likitan Da Suka Sace A Borno Bayan Kwashe Watanni 11 Suna Rike Da Shi

ISWAP Sun Saki Likitan Da Suka Sace A Borno Bayan Kwashe Watanni 11 Suna Rike Da Shi

LABARAI MASU NASABA

Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

June 2, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

June 2, 2025
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

June 2, 2025
Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

June 2, 2025
Mataimakin shugaban kasa

Shettima: Shekaru Biyu Na Mataimaki, Jagora Mai Hangen Nesa Da Kawo Sauyi Nagari

June 2, 2025

Alƙalai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

June 2, 2025
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

June 2, 2025
Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

June 2, 2025
Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

June 2, 2025
Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

June 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.