• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Bukatar Sake Farfado Da Kiwon Tarwada A Nijeriya

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
An Rufe Rabin Masana’antun Kiwon Kifi A Jihar Filato
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kullum, bukatar kifin Tarwada kara karuwa yake a Nijeriya, duba da irin muhimmancin da yake da shi wajen gina jikin Dan Adam tare kuma da kara bunkasa tattalin arzikin wannan kasa.

Sai dai, akwai kalubale wajen kiwon Tarwadar, koda-yake amfani da dabarun kimiyyar zamani da kasuwanci, za su taimaka wajen samar da makoma mai dorewa a wannan fanni tare damammaki masu yawan gaske ga masu yin kiwon ta.

  • Ta Hanyar Tinkarar Wannan Muhimmin Batu Ne Kawai Za A Iya Inganta Dangantakar Dake Tsakanin Sin Da Amurka
  • Hajjin Bana: NAHCON Ta Ba Jihohi Wa’adin Mika Sunaye Maniyyata

Har ila yau, a Nijeriya an jima ana kiwon Tarwada a gargajiyance, wanda akasarin masu yin wannan kiwo; masu karamin karfi ne, sannan ba sa iya samun kayan kiwo na zamanin tare da dabarun kiwon, don samun kasuwar da ta dace.

Hakan ya yi sanadiyyar samun karancin Tarwadar da kuma rashin samun kudaden shiga masu yawa, rashin sarrafa ta yadda ya dace da kuma rashin samar da kayan aikin adana ta, wanda hakan kan jawo wa masu sana’ar yin asara a wasu lokutan.

Duk da wadannan kalubale, har yanzu fannin na samar da damammaki da suka hada da raguwar talauci, samar da ayyukan yi da kuma kara samar da wadataccen abinci a fadin wannan kasa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

Baya ga kasancewar Nijeriya a matsayin kasa mafi yawan al’umma a Afirka, ta kuma kasance kan gaba a duniya wajen samar da wannan kifi na Tarwada, wanda aka kiyasta cewa; tana iya samar da Tarwada tan miliyan daya a shekarar 2021, wanda kudinta ya kai kimanin dala biliyan 2.6.

Haka zalika, a Nijeriya akwai matakai da dama da ake bi na kiwonta, domin samun wadatacciyar riba da suka hada da; kiwonta, sarrafa ta, kasuwancinta da yin amfani da ita da sauran makamantansu.

Don haka, kowane mataki daya daga cikin wadannan matakai, na da irin nasa kalubalen da kuma damammaki.

Bisa wani bincike da aka yi karkashin aikin kiwon Kifi na ‘FISH4ACP’, wanda ma’aikatar aikin noma da raya karkara ta gudanar ya nuna cewa, Nijeriya na da akalla masu samar da Tarwada kimanin 285,000, inda kananan masu kiwon suka doshi kashi 60 cikin 100.

Bisa hadaka a tsakanin hukumar abinci ta duniya (FAO) da ma’aikatar noma da raya karkara ta yi a kwanakin baya, sun kaddamar da wanzar da kashin farko na bunkasa kiwon Tarwada; don samun gwaggwabar riba a Nijeriya.

A yanzu haka, Nahiyar Turai (EU), da kuma ma’aiktar bunkasa tattalin arziki ne ke tallafa wa wannan aiki na ‘Fish4ACP’ a Nijeriya.

Kazalika, wannan wani shiri ne wanda kungiyar Afirka da jihohin da ke bakin teku (OCAPS), suka kirkiro da shi domin bayar da nasu goyon bayan wajen samar da wadataccen abinci mai gina jiki, kara habaka tattalin arziki da samar da ayyukan yi, samar da damar kasuwanci da zuba jari da kuma karfafa yin gasa a wannan fanni.

A nasa jawabin yayin kaddamar da shirin a Abuja, wakilin hukumar FAO a Nijeriya; Fred Kafeero ya bayyana cewa, aikin zai taimaka wajen farfado da fannin kiwon Tarwada a Nijeriya tare da samar da abinci da kuma habaka tattalin arzikin ‘ya’yan wannan kasa baki-daya.

Kafeero ya kara da cewa, Nijeriya na da matukar muhimmanci da dabaru a cikin sauran kasashe, wajen bunkasa kiwon Tarwada da kuma habaka kiwonta, don samun riba mai yawan gaske.

Wata tawagar Nahiyar Turai (EU), ta kawo ziyara kasar nan domin taimaka wa da dabarun kiwonta, musamman domin lalubo da mafita kan kalubalen da masu sana’ar da kuma ‘yan kasuwa ke fuskanta a Nijeriya.

Frank Okafor ne ya jagoranci tawagar a wajen taron, wanda ya ce, kungiyar ta mayar da hankali ne domin taimaka wa Nijeriya da sauran kasashen da ke Afirka, don samun damar cimma muradunsu ta hanyar taimaka wa da kudade tare da samar da dabarun cin nasara a wannan fanni na kiwonta a dukkanin fadin Afirka.

Shi kuwa Babban Sakatare a Mai’aikatar Aikin Noma da Raya Karkara, Dakta Ernest Umakhihe cewa ya yi, ma’aikatar ta mayar da hankali ne, don habaka kiwonta wanda ake sa ran za a kara samar da yawanta, domin samun wadatuwa da ta kai kimanin tan 250,000, don cimma bukatar da ake da ita a kasar tare da rage dogaron da ake da shi na shigo da ita daga kasashen ketare.

Bugu da kari, kara fafado da wannan fannin a Nijeriya, abu ne da ke bukatar hada karfi da karfe a tsakanin gwamnati, masu ruwa da tsaki, masu kiwonta, masu yin bincike da kuma masana’antu masu zaman kansu.

Kazalika, yin amfai da dabarun da suka kamata da kuma samar da dauki ga fannin, masana’antar kiwonta za ta iya bayar da gudunmawa wajen kara habakawa tare da bunkasa tattalin arzikin Nijeriya.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jihar Bauchi Ta Yi Fintikau Wajen Aiwatar Da Shirin Noma Na Bankin Duniya – Dr. Kabir

Next Post

Jihar Oyo Na Horar Da Malaman Gona Domin Samun Wadatar Abinci

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

4 days ago
Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

5 days ago
Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet
Noma Da Kiwo

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

5 days ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

6 days ago
Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma

2 weeks ago
Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja
Noma Da Kiwo

Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja

2 weeks ago
Next Post
Jihar Oyo Na Horar Da Malaman Gona Domin Samun Wadatar Abinci

Jihar Oyo Na Horar Da Malaman Gona Domin Samun Wadatar Abinci

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.