ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta Hanyar Tinkarar Wannan Muhimmin Batu Ne Kawai Za A Iya Inganta Dangantakar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

by CGTN Hausa
2 years ago
Amurka

A ran 26 ga wata ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya jaddada a ganawarsa da sakataren harkokin wajen kasar Amurka Antony Blinken da ke ziyara a kasar cewa, kamata ya yi kasashen biyu su kasance abokan hulda, maimakon abokan gaba, su taimaki juna cimma nasara, maimakon cutar da juna, su nemi cimma matsaya guda da ajiye bambance-bambance, maimakon shiga muguwar gasa, da kuma fada da cikawa, maimakon yin magana da baki biyu.  

Me ya sa Amurka a ko da yaushe take furta kalma amma sai ta aikata sabanin abin da ta furta? Li Haidong, shehun malami a jami’ar ilmin harkokin wajen kasar Sin, ya bayyana cewa, yin magana da baki biyu, wata babbar cuta ce ta gwamnatin Amurka a lokacin tafiyar da dangantakar dake tsakaninta da kasar Sin. Ban da wannan kuma, bana shekarar zabe ce a Amurka, sha’anin siyasa na cikin gida a Amurka ya kara ta’azzara, kana sauye-sauyen da suka shafi alkiblar manufofin kasar Sin sun karu, dukkansu sun yi tasiri kan manufofin gwamnatin Amurka game da yadda take mu’amala da kasar Sin. Idan an yi tunani mai zurfi kuma, an gano cewa, Amurka na bukatar yin hadin gwiwa da kasar Sin yayin da kuma take yunkurin dalike ci gaban kasar Sin, lamarin da ke nuna cewa, wasu mutanen Amurka suna da gajeren tunani, da yin kuskuren daukar kasar Sin a matsayin “babbar abokiyar hamayyarta bisa manyan tsare-tsare”, da kuma babban rashin fahimtar manufar bunkasuwar kasar Sin.

  • Binciken CGTN: Ba Karfin Samar Da Kayayyaki Na Kasar Sin Ba Ne Ya Wuce Kima, Sai Dai “Kariya Irin Na Amurka”
  • Dalilin Da Ya Sa Duniya Ke Bukatar Karfin Sin Na Samar Da Hajoji Masu Alaka Da Makamashi Mai Tsafta

An lura da cewa, yayin da aka yi mu’amala tsakanin manyan jami’an Sin da Amurka a cikin ‘yan shekarun nan, an tattauna batun fahimtar manyan tsare-tsare. A yayin ziyarar ta Blinken a wannan karo, bangaren Sin ya jaddada cewa, kasar Sin kasa ce mai ra’ayin gurguzu da ke bin hanyar samun ci gaba cikin lumana. Kuma ba ta dauke da tunanin hamayya ko yakin cacar baka, dukkan wadannan ba dabi’un kasar Sin ba ne. Wadannan kalamai sun aike da sako karara cewa, manufar ci gaban kasar Sin ita ce samar da ingantacciyar rayuwa ga jama’arta, ba wai ta maye gurbin Amurka ba. Bugu da kari, kasar Sin a ko da yaushe tana kallon dangantakar dake tsakaninta da Amurka bisa ma’aunin kiyaye tushen jin dadin jama’ar kasashen biyu, da kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya, kana tana tsayawa tsayin daka wajen mutunta juna, zaman tare cikin lumana, da hadin gwiwar samun nasara tare. (Yahaya)

ADVERTISEMENT

 

 

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Amurka
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Tinubu

Tinubu Zai Kaddamar Da Motoci 2,700 Masu Amfani Da Iskar Gas A Watan Mayu

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.