ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta Hanyar Tinkarar Wannan Muhimmin Batu Ne Kawai Za A Iya Inganta Dangantakar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

by CGTN Hausa
2 years ago
Amurka

A ran 26 ga wata ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya jaddada a ganawarsa da sakataren harkokin wajen kasar Amurka Antony Blinken da ke ziyara a kasar cewa, kamata ya yi kasashen biyu su kasance abokan hulda, maimakon abokan gaba, su taimaki juna cimma nasara, maimakon cutar da juna, su nemi cimma matsaya guda da ajiye bambance-bambance, maimakon shiga muguwar gasa, da kuma fada da cikawa, maimakon yin magana da baki biyu.  

Me ya sa Amurka a ko da yaushe take furta kalma amma sai ta aikata sabanin abin da ta furta? Li Haidong, shehun malami a jami’ar ilmin harkokin wajen kasar Sin, ya bayyana cewa, yin magana da baki biyu, wata babbar cuta ce ta gwamnatin Amurka a lokacin tafiyar da dangantakar dake tsakaninta da kasar Sin. Ban da wannan kuma, bana shekarar zabe ce a Amurka, sha’anin siyasa na cikin gida a Amurka ya kara ta’azzara, kana sauye-sauyen da suka shafi alkiblar manufofin kasar Sin sun karu, dukkansu sun yi tasiri kan manufofin gwamnatin Amurka game da yadda take mu’amala da kasar Sin. Idan an yi tunani mai zurfi kuma, an gano cewa, Amurka na bukatar yin hadin gwiwa da kasar Sin yayin da kuma take yunkurin dalike ci gaban kasar Sin, lamarin da ke nuna cewa, wasu mutanen Amurka suna da gajeren tunani, da yin kuskuren daukar kasar Sin a matsayin “babbar abokiyar hamayyarta bisa manyan tsare-tsare”, da kuma babban rashin fahimtar manufar bunkasuwar kasar Sin.

  • Binciken CGTN: Ba Karfin Samar Da Kayayyaki Na Kasar Sin Ba Ne Ya Wuce Kima, Sai Dai “Kariya Irin Na Amurka”
  • Dalilin Da Ya Sa Duniya Ke Bukatar Karfin Sin Na Samar Da Hajoji Masu Alaka Da Makamashi Mai Tsafta

An lura da cewa, yayin da aka yi mu’amala tsakanin manyan jami’an Sin da Amurka a cikin ‘yan shekarun nan, an tattauna batun fahimtar manyan tsare-tsare. A yayin ziyarar ta Blinken a wannan karo, bangaren Sin ya jaddada cewa, kasar Sin kasa ce mai ra’ayin gurguzu da ke bin hanyar samun ci gaba cikin lumana. Kuma ba ta dauke da tunanin hamayya ko yakin cacar baka, dukkan wadannan ba dabi’un kasar Sin ba ne. Wadannan kalamai sun aike da sako karara cewa, manufar ci gaban kasar Sin ita ce samar da ingantacciyar rayuwa ga jama’arta, ba wai ta maye gurbin Amurka ba. Bugu da kari, kasar Sin a ko da yaushe tana kallon dangantakar dake tsakaninta da Amurka bisa ma’aunin kiyaye tushen jin dadin jama’ar kasashen biyu, da kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya, kana tana tsayawa tsayin daka wajen mutunta juna, zaman tare cikin lumana, da hadin gwiwar samun nasara tare. (Yahaya)

ADVERTISEMENT

 

 

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Amurka
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Tinubu

Tinubu Zai Kaddamar Da Motoci 2,700 Masu Amfani Da Iskar Gas A Watan Mayu

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.