ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Bukatar Sake Farfado Da Kiwon Tarwada A Nijeriya

by Abubakar Abba
2 years ago
Nijeriya

A kullum, bukatar kifin Tarwada kara karuwa yake a Nijeriya, duba da irin muhimmancin da yake da shi wajen gina jikin Dan Adam tare kuma da kara bunkasa tattalin arzikin wannan kasa.

Sai dai, akwai kalubale wajen kiwon Tarwadar, koda-yake amfani da dabarun kimiyyar zamani da kasuwanci, za su taimaka wajen samar da makoma mai dorewa a wannan fanni tare damammaki masu yawan gaske ga masu yin kiwon ta.

  • Ta Hanyar Tinkarar Wannan Muhimmin Batu Ne Kawai Za A Iya Inganta Dangantakar Dake Tsakanin Sin Da Amurka
  • Hajjin Bana: NAHCON Ta Ba Jihohi Wa’adin Mika Sunaye Maniyyata

Har ila yau, a Nijeriya an jima ana kiwon Tarwada a gargajiyance, wanda akasarin masu yin wannan kiwo; masu karamin karfi ne, sannan ba sa iya samun kayan kiwo na zamanin tare da dabarun kiwon, don samun kasuwar da ta dace.

ADVERTISEMENT

Hakan ya yi sanadiyyar samun karancin Tarwadar da kuma rashin samun kudaden shiga masu yawa, rashin sarrafa ta yadda ya dace da kuma rashin samar da kayan aikin adana ta, wanda hakan kan jawo wa masu sana’ar yin asara a wasu lokutan.

Duk da wadannan kalubale, har yanzu fannin na samar da damammaki da suka hada da raguwar talauci, samar da ayyukan yi da kuma kara samar da wadataccen abinci a fadin wannan kasa.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Baya ga kasancewar Nijeriya a matsayin kasa mafi yawan al’umma a Afirka, ta kuma kasance kan gaba a duniya wajen samar da wannan kifi na Tarwada, wanda aka kiyasta cewa; tana iya samar da Tarwada tan miliyan daya a shekarar 2021, wanda kudinta ya kai kimanin dala biliyan 2.6.

Haka zalika, a Nijeriya akwai matakai da dama da ake bi na kiwonta, domin samun wadatacciyar riba da suka hada da; kiwonta, sarrafa ta, kasuwancinta da yin amfani da ita da sauran makamantansu.

Don haka, kowane mataki daya daga cikin wadannan matakai, na da irin nasa kalubalen da kuma damammaki.

Bisa wani bincike da aka yi karkashin aikin kiwon Kifi na ‘FISH4ACP’, wanda ma’aikatar aikin noma da raya karkara ta gudanar ya nuna cewa, Nijeriya na da akalla masu samar da Tarwada kimanin 285,000, inda kananan masu kiwon suka doshi kashi 60 cikin 100.

Bisa hadaka a tsakanin hukumar abinci ta duniya (FAO) da ma’aikatar noma da raya karkara ta yi a kwanakin baya, sun kaddamar da wanzar da kashin farko na bunkasa kiwon Tarwada; don samun gwaggwabar riba a Nijeriya.

A yanzu haka, Nahiyar Turai (EU), da kuma ma’aiktar bunkasa tattalin arziki ne ke tallafa wa wannan aiki na ‘Fish4ACP’ a Nijeriya.

Kazalika, wannan wani shiri ne wanda kungiyar Afirka da jihohin da ke bakin teku (OCAPS), suka kirkiro da shi domin bayar da nasu goyon bayan wajen samar da wadataccen abinci mai gina jiki, kara habaka tattalin arziki da samar da ayyukan yi, samar da damar kasuwanci da zuba jari da kuma karfafa yin gasa a wannan fanni.

A nasa jawabin yayin kaddamar da shirin a Abuja, wakilin hukumar FAO a Nijeriya; Fred Kafeero ya bayyana cewa, aikin zai taimaka wajen farfado da fannin kiwon Tarwada a Nijeriya tare da samar da abinci da kuma habaka tattalin arzikin ‘ya’yan wannan kasa baki-daya.

Kafeero ya kara da cewa, Nijeriya na da matukar muhimmanci da dabaru a cikin sauran kasashe, wajen bunkasa kiwon Tarwada da kuma habaka kiwonta, don samun riba mai yawan gaske.

Wata tawagar Nahiyar Turai (EU), ta kawo ziyara kasar nan domin taimaka wa da dabarun kiwonta, musamman domin lalubo da mafita kan kalubalen da masu sana’ar da kuma ‘yan kasuwa ke fuskanta a Nijeriya.

Frank Okafor ne ya jagoranci tawagar a wajen taron, wanda ya ce, kungiyar ta mayar da hankali ne domin taimaka wa Nijeriya da sauran kasashen da ke Afirka, don samun damar cimma muradunsu ta hanyar taimaka wa da kudade tare da samar da dabarun cin nasara a wannan fanni na kiwonta a dukkanin fadin Afirka.

Shi kuwa Babban Sakatare a Mai’aikatar Aikin Noma da Raya Karkara, Dakta Ernest Umakhihe cewa ya yi, ma’aikatar ta mayar da hankali ne, don habaka kiwonta wanda ake sa ran za a kara samar da yawanta, domin samun wadatuwa da ta kai kimanin tan 250,000, don cimma bukatar da ake da ita a kasar tare da rage dogaron da ake da shi na shigo da ita daga kasashen ketare.

Bugu da kari, kara fafado da wannan fannin a Nijeriya, abu ne da ke bukatar hada karfi da karfe a tsakanin gwamnati, masu ruwa da tsaki, masu kiwonta, masu yin bincike da kuma masana’antu masu zaman kansu.

Kazalika, yin amfai da dabarun da suka kamata da kuma samar da dauki ga fannin, masana’antar kiwonta za ta iya bayar da gudunmawa wajen kara habakawa tare da bunkasa tattalin arzikin Nijeriya.

 

Nijeriya
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Jihar Oyo Na Horar Da Malaman Gona Domin Samun Wadatar Abinci

Jihar Oyo Na Horar Da Malaman Gona Domin Samun Wadatar Abinci

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.