ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Bukatar Sake Farfado Da Kiwon Tarwada A Nijeriya

by Abubakar Abba
2 years ago
Nijeriya

A kullum, bukatar kifin Tarwada kara karuwa yake a Nijeriya, duba da irin muhimmancin da yake da shi wajen gina jikin Dan Adam tare kuma da kara bunkasa tattalin arzikin wannan kasa.

Sai dai, akwai kalubale wajen kiwon Tarwadar, koda-yake amfani da dabarun kimiyyar zamani da kasuwanci, za su taimaka wajen samar da makoma mai dorewa a wannan fanni tare damammaki masu yawan gaske ga masu yin kiwon ta.

  • Ta Hanyar Tinkarar Wannan Muhimmin Batu Ne Kawai Za A Iya Inganta Dangantakar Dake Tsakanin Sin Da Amurka
  • Hajjin Bana: NAHCON Ta Ba Jihohi Wa’adin Mika Sunaye Maniyyata

Har ila yau, a Nijeriya an jima ana kiwon Tarwada a gargajiyance, wanda akasarin masu yin wannan kiwo; masu karamin karfi ne, sannan ba sa iya samun kayan kiwo na zamanin tare da dabarun kiwon, don samun kasuwar da ta dace.

ADVERTISEMENT

Hakan ya yi sanadiyyar samun karancin Tarwadar da kuma rashin samun kudaden shiga masu yawa, rashin sarrafa ta yadda ya dace da kuma rashin samar da kayan aikin adana ta, wanda hakan kan jawo wa masu sana’ar yin asara a wasu lokutan.

Duk da wadannan kalubale, har yanzu fannin na samar da damammaki da suka hada da raguwar talauci, samar da ayyukan yi da kuma kara samar da wadataccen abinci a fadin wannan kasa.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Baya ga kasancewar Nijeriya a matsayin kasa mafi yawan al’umma a Afirka, ta kuma kasance kan gaba a duniya wajen samar da wannan kifi na Tarwada, wanda aka kiyasta cewa; tana iya samar da Tarwada tan miliyan daya a shekarar 2021, wanda kudinta ya kai kimanin dala biliyan 2.6.

Haka zalika, a Nijeriya akwai matakai da dama da ake bi na kiwonta, domin samun wadatacciyar riba da suka hada da; kiwonta, sarrafa ta, kasuwancinta da yin amfani da ita da sauran makamantansu.

Don haka, kowane mataki daya daga cikin wadannan matakai, na da irin nasa kalubalen da kuma damammaki.

Bisa wani bincike da aka yi karkashin aikin kiwon Kifi na ‘FISH4ACP’, wanda ma’aikatar aikin noma da raya karkara ta gudanar ya nuna cewa, Nijeriya na da akalla masu samar da Tarwada kimanin 285,000, inda kananan masu kiwon suka doshi kashi 60 cikin 100.

Bisa hadaka a tsakanin hukumar abinci ta duniya (FAO) da ma’aikatar noma da raya karkara ta yi a kwanakin baya, sun kaddamar da wanzar da kashin farko na bunkasa kiwon Tarwada; don samun gwaggwabar riba a Nijeriya.

A yanzu haka, Nahiyar Turai (EU), da kuma ma’aiktar bunkasa tattalin arziki ne ke tallafa wa wannan aiki na ‘Fish4ACP’ a Nijeriya.

Kazalika, wannan wani shiri ne wanda kungiyar Afirka da jihohin da ke bakin teku (OCAPS), suka kirkiro da shi domin bayar da nasu goyon bayan wajen samar da wadataccen abinci mai gina jiki, kara habaka tattalin arziki da samar da ayyukan yi, samar da damar kasuwanci da zuba jari da kuma karfafa yin gasa a wannan fanni.

A nasa jawabin yayin kaddamar da shirin a Abuja, wakilin hukumar FAO a Nijeriya; Fred Kafeero ya bayyana cewa, aikin zai taimaka wajen farfado da fannin kiwon Tarwada a Nijeriya tare da samar da abinci da kuma habaka tattalin arzikin ‘ya’yan wannan kasa baki-daya.

Kafeero ya kara da cewa, Nijeriya na da matukar muhimmanci da dabaru a cikin sauran kasashe, wajen bunkasa kiwon Tarwada da kuma habaka kiwonta, don samun riba mai yawan gaske.

Wata tawagar Nahiyar Turai (EU), ta kawo ziyara kasar nan domin taimaka wa da dabarun kiwonta, musamman domin lalubo da mafita kan kalubalen da masu sana’ar da kuma ‘yan kasuwa ke fuskanta a Nijeriya.

Frank Okafor ne ya jagoranci tawagar a wajen taron, wanda ya ce, kungiyar ta mayar da hankali ne domin taimaka wa Nijeriya da sauran kasashen da ke Afirka, don samun damar cimma muradunsu ta hanyar taimaka wa da kudade tare da samar da dabarun cin nasara a wannan fanni na kiwonta a dukkanin fadin Afirka.

Shi kuwa Babban Sakatare a Mai’aikatar Aikin Noma da Raya Karkara, Dakta Ernest Umakhihe cewa ya yi, ma’aikatar ta mayar da hankali ne, don habaka kiwonta wanda ake sa ran za a kara samar da yawanta, domin samun wadatuwa da ta kai kimanin tan 250,000, don cimma bukatar da ake da ita a kasar tare da rage dogaron da ake da shi na shigo da ita daga kasashen ketare.

Bugu da kari, kara fafado da wannan fannin a Nijeriya, abu ne da ke bukatar hada karfi da karfe a tsakanin gwamnati, masu ruwa da tsaki, masu kiwonta, masu yin bincike da kuma masana’antu masu zaman kansu.

Kazalika, yin amfai da dabarun da suka kamata da kuma samar da dauki ga fannin, masana’antar kiwonta za ta iya bayar da gudunmawa wajen kara habakawa tare da bunkasa tattalin arzikin Nijeriya.

 

Nijeriya
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Jihar Oyo Na Horar Da Malaman Gona Domin Samun Wadatar Abinci

Jihar Oyo Na Horar Da Malaman Gona Domin Samun Wadatar Abinci

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.