• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Kasashen Duniya Za Su Gano Amsa In Sun Kwatanta Tarukan Koli Na Xi’an Da Hiroshima

by CMG Hausa
2 years ago
Hiroshima

A kwanakin nan, an gudanar da manyan tarukan koli guda biyu kusan a lokaci guda, wato taron kolin kasar Sin da kasashen da ke tsakiyar Asiya wanda aka gudanar a birnin Xi’an na kasar Sin, birnin dake zama mafarin hanyar siliki, da kuma taron kolin kungiyar G7, wanda aka gudanar a birnin Hiroshima, birni na farko a duniya da aka kai masa harin nukiliya, hakan nan kuma tarukan biyu sun bambanta sosai bisa la’akari da abubuwan da suke neman cimmawa.

Taron kolin kasar Sin da kasashen da ke tsakiyar Asiya wanda aka kammala shi ba da jimawa ba, ya mai da hankali a kan karfafa hadin gwiwa don tinkarar kalubale, kuma manufar taron shi ne karfafa hadin kai a maimakon yin fito na fito.

  • Shugabannin Kasashen Tsakiyar Asiya Sun Yi Alkawarin Kara Hadin Gwiwa Da Sin

Kamar dai yadda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana a jawabinsa cewa, duniya na fatan ganin tabbatar da kwanciyar hankali da ci gaba da jituwa da hadewa da juna a tsakiyar Asiya, ya kamata a gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya a tsakanin Sin da kasashen da ke tsakiyar Asiya, kuma ya kamata kasashen su tsaya kan taimakon juna da tabbatar da ci gaban juna da tsaronsu na bai daya da sada zumunta da juna daga zuriya zuwa zuriya.

Haka nan kuma ya shaida yadda kasar Sin ke cudanya da kasashen biyar din da ke tsakiyar Asiya bisa tushen zaman daidaito, kuma ba domin dakile wata kasa ba suke hulda da juna.

Taron na yini biyu ya cimma gagaruman nasarori, kuma babu shakka ya shaida ainihin ma’anar cudanyar kasa kasa, tare da kiyaye tsari da adalci a duniya.

LABARAI MASU NASABA

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

A daya bangare kuma, taron kolin G7 da har yanzu ke gudana a birnin Hiroshima, yana mai da hankali a kan haifar da rarrabuwar kawuna a tsakanin kasashen duniya, wato su kulla kawance don yin fito na fito da wasu kasashe. Kasar Japan mai masaukin baki tana amfani da damarta ta karbar bakuncin taron, don neman kulla kawance da sauran kasashen kungiyar, a yunkurin tinkarar abin da take kira wai “barazana daga Rasha da Sin da kuma Koriya ta arewa”, a sa’i daya kuma, tana neman goyon baya daga kawayen nan nata a kan batun zuba dagwalon ruwan nukiliya cikin tekun Pasifik. Ita kuma kasar Amurka ma burinta a bayyane ne, wato tana ci gaba da neman rura wutar rikicin Ukraine, tare da karfafa kawancenta da kasashen G7 wajen tinkarar kasar Sin. Da haka, muke iya gano cewa, manufar taron G7 shi ne su karfafa kawancensu don dakile sauran kasashe.

In mun kwatanta tarukan biyu, cikin sauki za mu gane cewa, tarukan biyu sun bambanta sosai daga dalilan gudanar da su da ma burin da ake neman cimmawa. Taron da aka gudanar a birnin Xi’an an gudanar da shi ne sabo da neman ci gaba na bai daya, don haka ma, abin da aka tattauna a gun taron shi ne ta yaya za a tabbatar da ci gaban kasashen.

A sa’i daya kuma, taron da aka gudanar a Hiroshima ya shaida yadda kasashen G7 suke da ra’ayin nan na samun ci gaba daga faduwar wani, don haka ma, sun fi mai da hankali a kan yadda za su kulla kawance da juna don yin fito na fito da wasu.

Daga Xi’an zuwa Hiroshima, tarukan biyu tamkar wani madubi ne dake haskakawa kasashen duniya, don gano amsa idan sun kwatanta su. (Lubabatu Lei)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
Daga Birnin Sin

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
Daga Birnin Sin

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Next Post
Kasa Da Wata Biyu Ya Bar Mulki, Shin Ko Buhari Ya Cika Wa ‘Yan Nijeriya Alkawarin Da Ya Yi Mu Su?

…Yadda Daura Ke Haramar Tarbar Buhari – Alhaji Saleh

LABARAI MASU NASABA

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.