ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

…Yadda Daura Ke Haramar Tarbar Buhari – Alhaji Saleh

by El-Zaharadeen Umar and Bello Hamza
3 years ago
Buhari

A daidai lokacin da Abuja ke shirye-shirye yin bankwana da Shugaban kasa Muhammad Buhjari a yayin da wa’adin mulkinsa da ya shafe shekara 8 yana jagorantar Nijeriya ke cika, su kuwa al’umma Jiharsa ta Katsina musamman garin haihuwarsa ta Daura sun dukufa cikin shirin ganin sun yi wa dan nasu gaggrumar tarba tare da shirya gangami na al’ummar jihar don nuna godiyarsu ga Allah da ya bashi ikon kammala wa’adin mulkinsa lafiya.

A cewar, wani jigo a yankin, wannan wata baiwa ce da ya kamata su gode wa Allah, suna kuma godiya ga al’ummar Nijeriya a bisa goyon baya da suka ba dan nasu har ya samu wannan nasarar.

  • Da Dumi-Dumi: Wanda Ya Assasa Bankin FCMB, Subomi Ya Rasu Ya Na Da Shekara 89
  • EFCC Na Binciken Gwamnan Zamfara Kan Almundahanar Biliyan 70

Tun a kwanan baya, mai martaba Sarkin Daura, Alhaji Umar Faruk Umar ya sanar da cewa, masarautar za ta shirya wa Shugaba Buhari gagarumin hawan daba domin yi masa lale marhabin da dawowa gida.

ADVERTISEMENT

Alhaji Muhammad Saleh, shi ne shugaban kungiyar “Concern People Forum” da ke masarautar Daura wadanda suke jagorantar shirye-shiryen gangamin tarbar shugaban kasa Muhammad Buhari a ranar 29 da watan Mayu na wannan shekara da wa’adin mulkinsa ke karewa.

Ya tattauna da LEADERSHIP Hausa game da shirye-shiryen da suke yi wanda ya ce suna sa ran manyan mutane za su shiga cikin lamarin domin karrama Shugaba Buhari a mahaifarsa kamar yadda ya kamata.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

A cewar Muhammad Saleh, yanzu haka sun fara samun gudunmawa daga mai martaba Sarkin Daura, Alhaji Umar Faruk Umar domin ci gaba da shriye-shirye, haka kuma shi ma shugaban jam’iyyar APC na Jihar Katsina ya ba da tasa gudunmawar, kuma suna sa ran cewa wasu ma na kan hanya.

Ga yadda hirar ta kasance:

Ya ake ciki dangane da batun shirye-shiryen da kuke yi  na tarbar Shugaban Kasa Muhammad Buhari da ke kammala wa’adin mulkinsa a ranar 29 ga watan Mayu?

Gaskiya muna nan muna ci gaba da shirye-shiryen tarbar mai girma shugaban Kasa idan Allah ya kaimu wa’adin mulkinsa ya kare a ranar 29 ga watan Mayu na wannan shekara ta 2023 a nan garin Daura idan Allah ya yarda.

Kamar dame-dame kuka shirya domin tarbarsa?

Muna son dai, mu tarbe shi, a ga jama’a sun tarbe shi ya dawo gida cikin farin ciki da walwala, shi ne muke shirya cewa za mu yi riguna da huluna wadanda za mu ba matasa su sanya, sannan za mu yi manyan alluna na sawa a kan titi na nuna murnar shugaban kasa ya dawo gida lafiya, ya gama aikinsa na shekara takwas, haka kuma za mu yi amfani da motoci wajen wannan tarba, za mu sanya mawaka da makada da za su kawata wannan tarba.

Kamar mutum nawa kuke sa ran za ku gayyata domin wannan biki na tarbar shugaban kasa?

Muna sa ran kowace karamar hukumar da ke cikin masarautar Daura za mu gayyaci akalla motoci goma da za su dauko jama’a zuwa tarbar shugaban kasa, kuma muna tsammanin kowace mota za ta dauko mutum 10.

Ya batun sanya manyan mutane cikin wannan hidima ta tarbar shugaban kasa?

Gaskiya, mun sanya manyan mutane daga masarautar Daura musamman wadanda ke son su ga an yi wannan hidima, yanzu haka akwai wasu dattawa da suke tattaunawa a kan wannan muhimmin batu na tarbar shugaban, kuma ni ma zan hadu da su domin tattaunawa ta yadda za a kara kawata wannan hidima a samu nasara, kamar uban kasa mai martaba Sarkin Daura ya shigo cikin wannan lamari, sai kuma ita kungiyarmu ta “Concern People Forum” ta shiga sosai, mai martaba Sarkin mun sanar da shi, kuma ya goyi bayan mu, har ya ba mu gudunmawa ta naira miliyan daya, ya ce mu je mu ci gaba da shirye-shirye shi ma yana da nashi shirin na yin Daba.

Kamar me ya bambamta wannan tsari naku da kuma na ita masarautar Daura tun da ita ma za ta shirya tarba ga shugaban kasa Muhammad Buhari?

Abin da ya bambamnta namu da kuma na masarauta shi ne, masarauta za ta shirya hawan Daba inda za a hau dawakai da hakimai da sauransu, mu kuma za mu tarbo shi ne da motoci a ya yin da wasu kuma a kasa za su rika takawa.

Ka yi maganar Sarkin Daura ya ba ku gudunmawa ta Naira miliyan daya, ga shi wannan taro yana bukatar kudi, yaya kuka tsara yadda za ku samu kudaden da za ku gudanar da wannan tarba cikin nasara?

Yanzu dai maganar da ake yi shi ne, mai martaba ya fara ba da gudunmawa, sai kuma shugaban jam’iyyar APC na jihar Katsina, Alhaji Sani Aliyu (JB) shi ma ya ba mu gudunmawa, ya zuwa yanzu wadannan gudunmawa guda biyu kadai suka shigo hannunmu, duk da cewa mun raba takardun neman gudunmawa muna kuma jiran amsa daga wadanda muka tura wa, daidai abin da muka samu da shi ne zamu yi amfani, idan mun samu kudi da yawa taro zai kawatar, idan kuma kadan aka samu za mu yi abin da ya sauwaka.

Shin me kuke fatan nunawa ga duniya ta hanyar wannan tarba da za ku shirya wa shugaban kasa ta dawo gida bayan kammala wa’adin mulkinsa?

Muna son duniya ta san cewa har yanzu dai mutanen kasar Daura suna son dansu, dansu ya je ya yi aiki, ya dawo sun tarbe shi, daman abin da ya kamata kenan, idan mutum ya bar gida zai dawo, to al’ummarsa su fito kwansu da kwarkwata su nuna jin dadi da dawowarsa, su nuna murna tun da ya yi wannan aiki ya gama lafiya.

Buhari
El-Zaharadeen Umar
+ posts Bio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Batun Kammala Aikin Gina Gidaje 250 Na “Renewed Hope” Ya Bar Baya Da Kura A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yusuf Buhari Ya Halarci Zaɓen Fidda Gwani Na Sanatan Shiyyar Daura
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mace Ta Doke Namiji A Zaɓen Fidda Gwani Na Majalisar Tarayya A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Gayyato Jakadun Kasashen Waje 17 Ya Kara Wa Bukukuwan Sallah Armashi A Katsina
Buhari
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Gwamntin Tarayya Da Ta Ogun Sun Fara Yi Wa Dabbobi Allurar Riga-kafin Cuttutuka

Gwamntin Tarayya Da Ta Ogun Sun Fara Yi Wa Dabbobi Allurar Riga-kafin Cuttutuka

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.