• English
  • Business News
Sunday, July 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

…Yadda Daura Ke Haramar Tarbar Buhari – Alhaji Saleh

by El-Zaharadeen Umar and Bello Hamza
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Kasa Da Wata Biyu Ya Bar Mulki, Shin Ko Buhari Ya Cika Wa ‘Yan Nijeriya Alkawarin Da Ya Yi Mu Su?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A daidai lokacin da Abuja ke shirye-shirye yin bankwana da Shugaban kasa Muhammad Buhjari a yayin da wa’adin mulkinsa da ya shafe shekara 8 yana jagorantar Nijeriya ke cika, su kuwa al’umma Jiharsa ta Katsina musamman garin haihuwarsa ta Daura sun dukufa cikin shirin ganin sun yi wa dan nasu gaggrumar tarba tare da shirya gangami na al’ummar jihar don nuna godiyarsu ga Allah da ya bashi ikon kammala wa’adin mulkinsa lafiya.

A cewar, wani jigo a yankin, wannan wata baiwa ce da ya kamata su gode wa Allah, suna kuma godiya ga al’ummar Nijeriya a bisa goyon baya da suka ba dan nasu har ya samu wannan nasarar.

  • Da Dumi-Dumi: Wanda Ya Assasa Bankin FCMB, Subomi Ya Rasu Ya Na Da Shekara 89
  • EFCC Na Binciken Gwamnan Zamfara Kan Almundahanar Biliyan 70

Tun a kwanan baya, mai martaba Sarkin Daura, Alhaji Umar Faruk Umar ya sanar da cewa, masarautar za ta shirya wa Shugaba Buhari gagarumin hawan daba domin yi masa lale marhabin da dawowa gida.

Alhaji Muhammad Saleh, shi ne shugaban kungiyar “Concern People Forum” da ke masarautar Daura wadanda suke jagorantar shirye-shiryen gangamin tarbar shugaban kasa Muhammad Buhari a ranar 29 da watan Mayu na wannan shekara da wa’adin mulkinsa ke karewa.

Ya tattauna da LEADERSHIP Hausa game da shirye-shiryen da suke yi wanda ya ce suna sa ran manyan mutane za su shiga cikin lamarin domin karrama Shugaba Buhari a mahaifarsa kamar yadda ya kamata.

Labarai Masu Nasaba

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

A cewar Muhammad Saleh, yanzu haka sun fara samun gudunmawa daga mai martaba Sarkin Daura, Alhaji Umar Faruk Umar domin ci gaba da shriye-shirye, haka kuma shi ma shugaban jam’iyyar APC na Jihar Katsina ya ba da tasa gudunmawar, kuma suna sa ran cewa wasu ma na kan hanya.

Ga yadda hirar ta kasance:

Ya ake ciki dangane da batun shirye-shiryen da kuke yi  na tarbar Shugaban Kasa Muhammad Buhari da ke kammala wa’adin mulkinsa a ranar 29 ga watan Mayu?

Gaskiya muna nan muna ci gaba da shirye-shiryen tarbar mai girma shugaban Kasa idan Allah ya kaimu wa’adin mulkinsa ya kare a ranar 29 ga watan Mayu na wannan shekara ta 2023 a nan garin Daura idan Allah ya yarda.

Kamar dame-dame kuka shirya domin tarbarsa?

Muna son dai, mu tarbe shi, a ga jama’a sun tarbe shi ya dawo gida cikin farin ciki da walwala, shi ne muke shirya cewa za mu yi riguna da huluna wadanda za mu ba matasa su sanya, sannan za mu yi manyan alluna na sawa a kan titi na nuna murnar shugaban kasa ya dawo gida lafiya, ya gama aikinsa na shekara takwas, haka kuma za mu yi amfani da motoci wajen wannan tarba, za mu sanya mawaka da makada da za su kawata wannan tarba.

Kamar mutum nawa kuke sa ran za ku gayyata domin wannan biki na tarbar shugaban kasa?

Muna sa ran kowace karamar hukumar da ke cikin masarautar Daura za mu gayyaci akalla motoci goma da za su dauko jama’a zuwa tarbar shugaban kasa, kuma muna tsammanin kowace mota za ta dauko mutum 10.

Ya batun sanya manyan mutane cikin wannan hidima ta tarbar shugaban kasa?

Gaskiya, mun sanya manyan mutane daga masarautar Daura musamman wadanda ke son su ga an yi wannan hidima, yanzu haka akwai wasu dattawa da suke tattaunawa a kan wannan muhimmin batu na tarbar shugaban, kuma ni ma zan hadu da su domin tattaunawa ta yadda za a kara kawata wannan hidima a samu nasara, kamar uban kasa mai martaba Sarkin Daura ya shigo cikin wannan lamari, sai kuma ita kungiyarmu ta “Concern People Forum” ta shiga sosai, mai martaba Sarkin mun sanar da shi, kuma ya goyi bayan mu, har ya ba mu gudunmawa ta naira miliyan daya, ya ce mu je mu ci gaba da shirye-shirye shi ma yana da nashi shirin na yin Daba.

Kamar me ya bambamta wannan tsari naku da kuma na ita masarautar Daura tun da ita ma za ta shirya tarba ga shugaban kasa Muhammad Buhari?

Abin da ya bambamnta namu da kuma na masarauta shi ne, masarauta za ta shirya hawan Daba inda za a hau dawakai da hakimai da sauransu, mu kuma za mu tarbo shi ne da motoci a ya yin da wasu kuma a kasa za su rika takawa.

Ka yi maganar Sarkin Daura ya ba ku gudunmawa ta Naira miliyan daya, ga shi wannan taro yana bukatar kudi, yaya kuka tsara yadda za ku samu kudaden da za ku gudanar da wannan tarba cikin nasara?

Yanzu dai maganar da ake yi shi ne, mai martaba ya fara ba da gudunmawa, sai kuma shugaban jam’iyyar APC na jihar Katsina, Alhaji Sani Aliyu (JB) shi ma ya ba mu gudunmawa, ya zuwa yanzu wadannan gudunmawa guda biyu kadai suka shigo hannunmu, duk da cewa mun raba takardun neman gudunmawa muna kuma jiran amsa daga wadanda muka tura wa, daidai abin da muka samu da shi ne zamu yi amfani, idan mun samu kudi da yawa taro zai kawatar, idan kuma kadan aka samu za mu yi abin da ya sauwaka.

Shin me kuke fatan nunawa ga duniya ta hanyar wannan tarba da za ku shirya wa shugaban kasa ta dawo gida bayan kammala wa’adin mulkinsa?

Muna son duniya ta san cewa har yanzu dai mutanen kasar Daura suna son dansu, dansu ya je ya yi aiki, ya dawo sun tarbe shi, daman abin da ya kamata kenan, idan mutum ya bar gida zai dawo, to al’ummarsa su fito kwansu da kwarkwata su nuna jin dadi da dawowarsa, su nuna murna tun da ya yi wannan aiki ya gama lafiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariDauraSauka Daga MulkiTarba
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sharhi: Kasashen Duniya Za Su Gano Amsa In Sun Kwatanta Tarukan Koli Na Xi’an Da Hiroshima

Next Post

Gwamntin Tarayya Da Ta Ogun Sun Fara Yi Wa Dabbobi Allurar Riga-kafin Cuttutuka

Related

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC
Manyan Labarai

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

3 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

10 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

14 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

1 day ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

1 day ago
Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace
Manyan Labarai

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

2 days ago
Next Post
Gwamntin Tarayya Da Ta Ogun Sun Fara Yi Wa Dabbobi Allurar Riga-kafin Cuttutuka

Gwamntin Tarayya Da Ta Ogun Sun Fara Yi Wa Dabbobi Allurar Riga-kafin Cuttutuka

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

July 5, 2025
Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

July 5, 2025
‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

July 5, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

July 5, 2025
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

July 5, 2025
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

July 5, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

July 5, 2025
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

July 5, 2025
Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.