• English
  • Business News
Saturday, May 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Tashar Binciken Sararin Samaniya Ta Lasar Sin, Mallakar Kasar Sin Da Ma Duniya Baki Daya Ce

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sharhi: Tashar Binciken Sararin Samaniya Ta Lasar Sin, Mallakar Kasar Sin Da Ma Duniya Baki Daya Ce
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan nan, kumbon Shenzhou-14 dake dauke da ’yan sama jannati uku ya dawo doron duniya. Kafin wannan kuma, ’yan sama jannati na kumbon sun yi musayar aiki tare da takwarorinsu dake cikin kumbon Shenzhou-15, wanda aka harba ba da jimawa ba, daga nan kuma, tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin da ake kira “Tiangong”, ta shiga wani sabon mataki na fara gudanar da harkoki daban daban. Kafin wannan kuma, gwamnatin kasar Sin ta taba sanar da bude tashar ga dukkanin kasashe mambobin MDD.

An ce, tun daga shekarar 2016, kasar Sin ta tattara shirye-shiryen gwaji daga wajen kasashe mambobin MDD wadanda suke so su gudanar a tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin, kuma kawo yanzu akwai shirye-shirye 9 na kasashe 17, da suka hada da Switzerland, da Poland, da Jamus, da Italiya, da na wasu rukunoni 23 da aka sanya su cikin jerin shirye-shiryen gwajin kimiyya na farko da za a gudanar a tashar.

  • Kumbon Shenzhou-15 Na Kasar Sin Ya Hade Tashar Binciken Sararin Samaniyar Kasar

Darektar ofishin kula da harkokin sararin samaniya na MDD Simonetta Di Pippo, ta bayyana cewa, yadda kasar Sin ta bude kofar tasharta ta binciken sararin samaniya ya kasance wani muhimmin bangare na shawarar MDD ta “binciken sararin samaniya cikin hadin gwiwa”, kuma misali ne abun yabawa.

Sai dai idan an waiwayi baya, Amurka da sauran kasashen yamma sun yi kokarin kafa shingen hana harkokin binciken sararin samaniya da kasar Sin ta gudanar, har ma kasar Amurka ta kafa dokar hana hukumar NASA ta yi hadin gwiwa da kasar Sin, ta hana kasar Sin shiga tashar binciken sararin samaniya ta kasa da kasa. Amma hakan bai hana Sinawa kokarinsu na binciken sararin samaniya ba. Tun bayan da kasar Sin ta fara aiwatar da shirin harba kumbuna masu dauke da mutane a ranar 21 ga watan Satumban shekarar 1992, al’ummar Sinawa sun shafe tsawon shekaru 30 suna kokari bisa karfin kansu, har ma hakarsu ta cimma ruwa.

Ci gaban harkokin binciken sararin samaniya na kasar Sin, ba kawai ya shaida karfin kasar a wannan fanni ba, har ma ya sa kaimin ayyukan binciken sararin samaniya na dan Adam baki daya. Yadda kasa da kasa ke hada gwiwa wajen aiwatar da shirye-shirye a tashar bincike ta kasar Sin, zai taimaka wajen tara fasahohi a wannan fanni, da ma ciyar da harkokin binciken sararin samaniya na dan Adam gaba zuwa wani sabon matsayi.

Labarai Masu Nasaba

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

Tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin wadda ta bude kofarta ga kasa da kasa, za ta zama gida na ’yan Adam baki daya a sararin samaniya.

Kamar yadda babban mai tsara ayyukan harba kumbuna masu dauke da mutane na kasar Sin, mista Zhou Jianping ya ce, “Aikin da tashar Tiangong ta sanya gaba shi ne, ya zama dakin gwaji na kasar Sin a sararin samaniya, don tallafawa manazarta kimiyya wajen gudanar da nazari da bincike, don amfanin ’yan Adam baki daya.”

A watan Fabarairun bana, hukumar kula da harkokin sararin samaniya na kasar Amurka (NASA) ta sanar da cewa, tashar binciken sararin samaniya ta kasar za ta daina aiki a shekarar 2030, wadda daga baya za ta fado cikin tekun Pasifik. Ta haka, muna iya hasashen cewa, nan da shekaru 8 masu zuwa, tashar Tiangong ta kasar Sin za ta kasance tasha irinta daya kacal ta dan Adam, wadda kuma za ta dauki babban nauyin binciken sararin samaniya. Muna da imanin cewa, tashar za ta hada karfin kasa da kasa, don amfanin dan Adam baki daya, a kokarinta na binciken sararin samaniya. (Lubabatu)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zulum Ya Gabatar Da N234.8b A Matsayin Kasafin 2023 Ga Majalisar Dokokin Borno

Next Post

‘Yansanda Za Su Yi Binciken Harin Da Aka Kai Gidan Shugaban Kwamitin Yakin Zaben PDP A Ribas 

Related

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo
Daga Birnin Sin

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

9 hours ago
Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi
Daga Birnin Sin

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

10 hours ago
Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani
Daga Birnin Sin

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

11 hours ago
Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha
Daga Birnin Sin

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

11 hours ago
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu
Daga Birnin Sin

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

18 hours ago
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

20 hours ago
Next Post
‘Yansanda Za Su Yi Binciken Harin Da Aka Kai Gidan Shugaban Kwamitin Yakin Zaben PDP A Ribas 

'Yansanda Za Su Yi Binciken Harin Da Aka Kai Gidan Shugaban Kwamitin Yakin Zaben PDP A Ribas 

LABARAI MASU NASABA

Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

May 10, 2025
Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

May 9, 2025
Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

May 9, 2025
Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

May 9, 2025
Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

May 9, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.