• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Tashar Binciken Sararin Samaniya Ta Lasar Sin, Mallakar Kasar Sin Da Ma Duniya Baki Daya Ce

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sharhi: Tashar Binciken Sararin Samaniya Ta Lasar Sin, Mallakar Kasar Sin Da Ma Duniya Baki Daya Ce
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan nan, kumbon Shenzhou-14 dake dauke da ’yan sama jannati uku ya dawo doron duniya. Kafin wannan kuma, ’yan sama jannati na kumbon sun yi musayar aiki tare da takwarorinsu dake cikin kumbon Shenzhou-15, wanda aka harba ba da jimawa ba, daga nan kuma, tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin da ake kira “Tiangong”, ta shiga wani sabon mataki na fara gudanar da harkoki daban daban. Kafin wannan kuma, gwamnatin kasar Sin ta taba sanar da bude tashar ga dukkanin kasashe mambobin MDD.

An ce, tun daga shekarar 2016, kasar Sin ta tattara shirye-shiryen gwaji daga wajen kasashe mambobin MDD wadanda suke so su gudanar a tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin, kuma kawo yanzu akwai shirye-shirye 9 na kasashe 17, da suka hada da Switzerland, da Poland, da Jamus, da Italiya, da na wasu rukunoni 23 da aka sanya su cikin jerin shirye-shiryen gwajin kimiyya na farko da za a gudanar a tashar.

  • Kumbon Shenzhou-15 Na Kasar Sin Ya Hade Tashar Binciken Sararin Samaniyar Kasar

Darektar ofishin kula da harkokin sararin samaniya na MDD Simonetta Di Pippo, ta bayyana cewa, yadda kasar Sin ta bude kofar tasharta ta binciken sararin samaniya ya kasance wani muhimmin bangare na shawarar MDD ta “binciken sararin samaniya cikin hadin gwiwa”, kuma misali ne abun yabawa.

Sai dai idan an waiwayi baya, Amurka da sauran kasashen yamma sun yi kokarin kafa shingen hana harkokin binciken sararin samaniya da kasar Sin ta gudanar, har ma kasar Amurka ta kafa dokar hana hukumar NASA ta yi hadin gwiwa da kasar Sin, ta hana kasar Sin shiga tashar binciken sararin samaniya ta kasa da kasa. Amma hakan bai hana Sinawa kokarinsu na binciken sararin samaniya ba. Tun bayan da kasar Sin ta fara aiwatar da shirin harba kumbuna masu dauke da mutane a ranar 21 ga watan Satumban shekarar 1992, al’ummar Sinawa sun shafe tsawon shekaru 30 suna kokari bisa karfin kansu, har ma hakarsu ta cimma ruwa.

Ci gaban harkokin binciken sararin samaniya na kasar Sin, ba kawai ya shaida karfin kasar a wannan fanni ba, har ma ya sa kaimin ayyukan binciken sararin samaniya na dan Adam baki daya. Yadda kasa da kasa ke hada gwiwa wajen aiwatar da shirye-shirye a tashar bincike ta kasar Sin, zai taimaka wajen tara fasahohi a wannan fanni, da ma ciyar da harkokin binciken sararin samaniya na dan Adam gaba zuwa wani sabon matsayi.

Labarai Masu Nasaba

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin wadda ta bude kofarta ga kasa da kasa, za ta zama gida na ’yan Adam baki daya a sararin samaniya.

Kamar yadda babban mai tsara ayyukan harba kumbuna masu dauke da mutane na kasar Sin, mista Zhou Jianping ya ce, “Aikin da tashar Tiangong ta sanya gaba shi ne, ya zama dakin gwaji na kasar Sin a sararin samaniya, don tallafawa manazarta kimiyya wajen gudanar da nazari da bincike, don amfanin ’yan Adam baki daya.”

A watan Fabarairun bana, hukumar kula da harkokin sararin samaniya na kasar Amurka (NASA) ta sanar da cewa, tashar binciken sararin samaniya ta kasar za ta daina aiki a shekarar 2030, wadda daga baya za ta fado cikin tekun Pasifik. Ta haka, muna iya hasashen cewa, nan da shekaru 8 masu zuwa, tashar Tiangong ta kasar Sin za ta kasance tasha irinta daya kacal ta dan Adam, wadda kuma za ta dauki babban nauyin binciken sararin samaniya. Muna da imanin cewa, tashar za ta hada karfin kasa da kasa, don amfanin dan Adam baki daya, a kokarinta na binciken sararin samaniya. (Lubabatu)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zulum Ya Gabatar Da N234.8b A Matsayin Kasafin 2023 Ga Majalisar Dokokin Borno

Next Post

‘Yansanda Za Su Yi Binciken Harin Da Aka Kai Gidan Shugaban Kwamitin Yakin Zaben PDP A Ribas 

Related

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

58 minutes ago
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka
Daga Birnin Sin

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

2 hours ago
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya
Daga Birnin Sin

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

3 hours ago
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

4 hours ago
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

5 hours ago
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

7 hours ago
Next Post
‘Yansanda Za Su Yi Binciken Harin Da Aka Kai Gidan Shugaban Kwamitin Yakin Zaben PDP A Ribas 

'Yansanda Za Su Yi Binciken Harin Da Aka Kai Gidan Shugaban Kwamitin Yakin Zaben PDP A Ribas 

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.