Kwamishinan ‘yansandan Jihar Ribas, Okon Effiong, ya bayar da umarnin binciken harin da aka kai gidan shugaban kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Sanata Lee Maeba.
Talla
Effiong, a martaninsa a kan harin, ya ce, tuni ya umarci mataimakin kwamishinan ‘yansanda da ke kula da sashen gudanar da bincike (SCID) da ya yi cikakken bayani kan lamarin.
- Miji Ya Hallaka Matarsa A Kan Ruwan Sha A Legas
- Sahihanci Da Imani Da Goyon Baya Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa
Kwamishinan ya bayyana cewa, “Na bayar da umarnin a gudanar da bincike, inda kuma mataimakin kwamishinan na ‘yansanda da ke kula da sashen gudanar da bincike (SCID) zai yi karin haske a kan lamarin”.
Talla