• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi:Karya Fure Take Ba Ta ‘Ya’ya

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Sharhi:Karya Fure Take Ba Ta ‘Ya’ya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanakin baya, kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ba da rahoton yadda ma’aikatar tsaron kasar Amurka ta gudanar da wani aikin farfaganda a asirce a yayin barkewar annobar COVID-19. Bisa ga rahoton, Reuters ya gano wasu shafuka a kalla 300 da aka bude ta kafar sada zumunta na X (wato Twitter a baya), wadanda suka yi ta yada karairayi na shafa wa alluran rigakafi kirar kamfanin Sinovac na kasar Sin kashin kaji. Shafukan dai suna karkashin jagorancin sojojin kasar Amurka, kuma kusan an bude dukansu ne a shekarar 2020. An fi gudanar da aikin a kasar Philippines, baya ga wasu kasashe maso tasowa da ke tsakiyar Asiya da ma Gabas ta tsakiya ma da aikin ya shafa. 

Sakamakon wannan aikin, mutane kalilan ne suka karbi rigakafin a kasar Phlippines, wato daga cikin mutanen kasar miliyan 114, kimanin miliyan 2.1 ne kawai aka yi wa cikakkun rigakafin. Kakakin tsohon shugaban kasar ta Phlippines Harry Roque, ya bayyana ta kafar sada zumunta cewa, “Sama da ‘yan kasar dubu 60 suka halaka sakamakon annobar, wadanda ta yiwu su tsira da rayukansu idan da ba bu wannan mummunan aikin farfagandan da aka gudanar a kan rigakafi na Sinovac.”

  • Shugaba Xi Na Kasar Sin Ya Amsa Wasikar Da Mutanen Gundumar Jingning Suka Aika Masa
  • Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Murna Ga Makon Yin Cudanya Tsakanin Matasan Sin Da Amurka 

A hakika, rigakafin Sinovac rigakafi ne daya kacal da kasar Philippines ta iya samu a wancan lokaci. Bayan barkewar annobar, kasar Sin ta rungumi ra’ayin nan na “gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya”, inda ta yi kokarin samar da gudummawar kayayyakin kandagarkin cutar ga sassan kasa da kasa, ta kuma sanar da bai wa dukkanin kasashen duniya damar yin amfani da alluran rigakafin da ta hada idan ta kammala nazarinta, don tabbatar da kasashe masu tasowa sun iya samun rigakafin da suke bukata. A watan Faburairun shekarar 2021, rukunin farko na gudummawar alluran rigakafin da kasar Sin ta samar wa kasar Philippines ya isa birnin Manila, babban birnin kasar, wanda ya kasance allurai na farko da kasar ta samu tun bayan barkewar annobar. Sai dai a yayin da kasashe masu tasowa ke fama da matsalar karancin rigakafin, ita Amurka ta rika adana alluran da ta hada saboda manufar “fifikon kasar Amurka a kan sauran kasashen duniya” da ta aiwatar, matakin da ya bar dimbin rigakafin da dama suka lalace a banza, rigakafin da ka iya taimakawa wajen ceton dimbin rayukan al’umma.

Rahoton na Reuters ya jawo fushi daga bangarori daban daban. Mr. Harry Roque ya ce, idan Amurka ba ta son samar da rigakafinta ga Philippines, to, shi ke nan, amma me ya sa ta shafa kashin kaji ga rigakafin da sauran kasashe suka samar. A nata bangare, hukumar lafiya ta duniya WHO a martanin da ta yi, ta jaddada cewa, “rigakafin Sinovac yana da inganci, kuma yana iya magance nuna alamu masu tsanani, kai har mutuwa sakamakon cutar”. Hukumar ta kuma yi nuni da cewa, “Mai da rigakafi a matsayin makami na siyasa, zai iya haifar da mummunan sakamako.”

Abin hakan yake, yada karairayi zai iya haifar da babbar barazana ga lafiyar al’umma. Amma a zahiri dai, ba lafiyar al’umma ba ce ke jawo hankalin Amurka. Wani jami’in kasar Amurkan da ya sa hannu a aikin ya ce, “Ba ta fuskar mahangar lafiyar al’umma muke kallon batun ba, a’a, abin da ke jan hankalinmu shi ne ta yaya za mu jefa kasar Sin cikin halin kaka-nika-yi.” Rahoton na Reuters ya kara da cewa, dalilin da ya sa Amurka ta aiwatar da wannan aiki shi ne, sabo da tana jin tsoron tasirin matakin kasar Sin na rarraba rigakafinta ga kasashen duniya. Wani jami’in kasar da yake da hannu a aikin ya ce, “Ba mu kyauta ba wajen rarraba rigakafinmu ga kawayenmu, saboda haka abin da kawai muka iya yi shi ne mu shafa wa rigakafin kasar Sin bakin fenti.”

Labarai Masu Nasaba

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

A yayin da kasar Sin ke dada bunkasa, ita kuma Amurka ta yi kuskure har ta dauki kasar Sin a matsayin babbar abokiyar takarar ta ta farko, lamarin da ya sa ta dauki matakai na dakile kasar Sin daga dukkan fannoni, ciki har da fannin yada labarai. Ba kawai ta fannin rigakafin da kasar Sin ta samar ba, har ma da shawarar “ziri daya da hanya daya”, da ma motocin lantarki da kasar ke samarwa, wadanda ke samun karbuwa daga kasa da kasa.

In mun dauki misalin Afirka, Sin da kasashen Afirka suna ta inganta hadin gwiwarsu tare da cimma gaggaruman nasarori. Amma Amurka wadda ta dade tana nuna fin karfi a duniya ba ta ji dadin hakan ba, don haka ma muke ta kara karanta rahotanni da ke da alaka da batun “sabon salon mulkin mallaka”, da “tarkon bashi”, da “barazana daga kasar Sin” a rahotannin da kafofin yada labarai na kasashen yamma suke watsawa.

Tsohon sakataren harkokin wajen kasar Amurka Mike Pompeo ya taba bayyanawa a fili cewa, “Muna karya da yaudara da sata…Mun kuma samar da darasi na koyar da wannan.” Sau tari hakikanan abubuwan da suka faru sun shaida cewa, dabarar Amurka ce ta yada karairayi ta kafofin sada zumunta, a yunkurinta na shafa wa wasu kasashe kashin kaji.

Sai dai shafa bakin fenti ga sauran kasashe ba zai “sake daga martabar Amurka” ba, illa ya shaida yadda take nuna fin karfi da ma rashin amana. Kasa mai girma irin Amurka, kamata ya yi ta yi abin da ya dace. Me zai hana ta mai da hankali wajen gudanar da ayyuka masu ma’ana, da za su amfani kasashen Afirka da ma sauran kasashe masu tasowa, maimakon yada karairayi?

Jama’a, shawara a gare ku kuma ita ce, ku yi hankali a lokacin da ku ke karanta rahotannin da ke shafa wa kasar Sin bakin fenti. (Mai zane:Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaCOVID-19SINOVAC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kar Ku Damu Ba Wata Babbar Gobara Ba ce – Matatar Dangote 

Next Post

Majalisa Ta shiga Taron Gaggawa Kan Batun Saya Wa Shugaba Ƙasa Sabon Jirgi

Related

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

6 hours ago
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

2 days ago
Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba
Ra'ayi Riga

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

1 week ago
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

2 weeks ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

2 weeks ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

2 weeks ago
Next Post
Majalisa Ta shiga Taron Gaggawa Kan Batun Saya Wa Shugaba Ƙasa Sabon Jirgi

Majalisa Ta shiga Taron Gaggawa Kan Batun Saya Wa Shugaba Ƙasa Sabon Jirgi

LABARAI MASU NASABA

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.