• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Arsenal Ta Barar Da Damarta Ta Lashe Firimiya?

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
in Wasanni
0
Shin Arsenal Ta Barar Da Damarta Ta Lashe Firimiya?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Magoya bayan kungiyar kwallon kafa ta Arsenal dai ba su ji dadin sakamakon wasansu da kungiyar kwallon kafa ta Aston Billa ba sai dai har yanzu magoya bayan suna da yakinin Arsenal din za ta iya lashe gasar har yanzu.

A ranar Lahadi ne dai kungiyar kwallon kafa ta Arsenal ta barar da damar hawa kan teburin Premier League, bayan da ta yi rashin nasara 2-0 a hannun Aston Billa a filin wasa na Emirates. Aston Billa, karkashin tsohon kociyan Arsenal, Unai Emery ta doke

  • Amurka Na Fakewa Da Guzuma Domin Harbin Karsana
  • Sharhi: Kokarin Fahimtar Yanayin Tattalin Arzikin Sin Ta Bangarorin Ayyuka Guda 3

Arsenal gida da waje kenan a bana, bayan cin 1-0 ranar 9 ga  Disambar 2023 a filin wasa na Billa Park.

An kuma ci Arsenal kwallayen biyu dab da za a tashi ta hannun Leon Bailey a minti na 84 da Ollie Watkins saura minti uku a busa tashi kuma da wannan sakamakon Arsenal mai maki 71 iri daya da na Liberpool ta ukun teburi, Manchester City tana da maki 73 ta dayan teburi da tazarar maki biyu tsakaninsu.

Sai dai tun a ranar Asabar Manchester City ta dura 5-1 a ragar Luton Town a filin wasa na Etihad a ranar Crystal Palace ta ci Liberpool 1-0 a filin wasa na Anfield a karawar mako na 33. Wannan shi ne karon farko da aka ci kungiyar Arsenal a 2024 cikin wasa

Labarai Masu Nasaba

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

11 a Premier League, wadda ta tashi ba ci da Manchester City, sannan ta lashe sauran wasannin gaba daya.

Rabon da Arsenal ta dauki gasar Premier League tun kakar wasa ta 2003 zuwa 2004 mai 13 jimilla, tun daga nan ba ta sake lashe kofin ba hakan ya sa magoya bayan kungiyar suke yunwar lashe gasar.

Kungiyar Arsenal ta kare kakar bara ba tare da daukar kofi ba, bayan da Manchester City ta sha gaban Arsenal a Premier daga karshe-karshen gasar sannan hakan ya bai wa Manchester City damar lashe kofi uku ciki har da na FA Cup da kuma KofinZakarun Turai karon farko a tarihi.

Saura wasanni shida da Arsenal za ta buga nan gaba, ciki har da karawa da Chelsea da Tottenham da kuma Manchester United, inda ake tunanin za ta iya sake barar da maki.

Wasannin da suke gaban Arsenal a Premier League:

20 ga Afirilu – Wolbes ( Molineud) 23 ga Afirilu – Chelsea (Emirates) 28 ga Afirilu – Tottenham (Tottenham Stadium) 4 ga Mayu – Bournemouth (Emirates) 12 ga Mayu- Manchester United (Old Trafford) 19 ga Mayu – Eberton (Emirate) Tasirin Magoya Baya

Bayan da kungiyar kwallon kafa ta Aston Billa ta zura kwallo ta biyu a ragar Arsenal a filin wasa na Fly Emirates, magoya bayan kungiyar Arsenal sun dinga ficewa daga filin tun kafin alkalin wasa ya tashi daga wasan wanda hakan koma baya ne ga kokarin kungiyar na lashe gasar firimiya. Tsohon dan wasan Arsenal, Ian Right, ya soki matakin magoya bayan na ficewa daga filin tun kafin a tashi inda yace kwata-kwata bai kamata ba kuma hakan zai karyarwa da ‘yan wasa gwiwa. Right ya bayar da misali da magoya bayan kungiyar kwallon kafa ta Manchester United da ba sa fita har sai alkalin wasa ya tashi daga wasa saboda suna ganin indai har ba a tashi ba tabbas ‘yan wasan kungiyar za su iya faranta musu rai ta hanyar zura kwallo a raga.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Tsayawa Kan Goyon Bayan Falasdinu Don Zama Mamba A Hukumance A MDD

Next Post

Sin Ta Nuna Rashin Gamsuwa Da Barazanar Da Amurka Ta Yi Na Kara Haraji Kan Karafa Da Gorar Ruwa Dake Shiga Kasar Daga Kasar Sin

Related

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Wasanni

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

16 hours ago
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?
Wasanni

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

19 hours ago
Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr
Wasanni

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

3 days ago
Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi
Wasanni

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

4 days ago
Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford
Wasanni

Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford

5 days ago
Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona
Wasanni

Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona

6 days ago
Next Post
Sin Ta Nuna Rashin Gamsuwa Da Barazanar Da Amurka Ta Yi Na Kara Haraji Kan Karafa Da Gorar Ruwa Dake Shiga Kasar Daga Kasar Sin

Sin Ta Nuna Rashin Gamsuwa Da Barazanar Da Amurka Ta Yi Na Kara Haraji Kan Karafa Da Gorar Ruwa Dake Shiga Kasar Daga Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.