• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Arsenal Ta Barar Da Damarta Ta Lashe Firimiya?

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
Arsenal

Magoya bayan kungiyar kwallon kafa ta Arsenal dai ba su ji dadin sakamakon wasansu da kungiyar kwallon kafa ta Aston Billa ba sai dai har yanzu magoya bayan suna da yakinin Arsenal din za ta iya lashe gasar har yanzu.

A ranar Lahadi ne dai kungiyar kwallon kafa ta Arsenal ta barar da damar hawa kan teburin Premier League, bayan da ta yi rashin nasara 2-0 a hannun Aston Billa a filin wasa na Emirates. Aston Billa, karkashin tsohon kociyan Arsenal, Unai Emery ta doke

  • Amurka Na Fakewa Da Guzuma Domin Harbin Karsana
  • Sharhi: Kokarin Fahimtar Yanayin Tattalin Arzikin Sin Ta Bangarorin Ayyuka Guda 3

Arsenal gida da waje kenan a bana, bayan cin 1-0 ranar 9 ga  Disambar 2023 a filin wasa na Billa Park.

An kuma ci Arsenal kwallayen biyu dab da za a tashi ta hannun Leon Bailey a minti na 84 da Ollie Watkins saura minti uku a busa tashi kuma da wannan sakamakon Arsenal mai maki 71 iri daya da na Liberpool ta ukun teburi, Manchester City tana da maki 73 ta dayan teburi da tazarar maki biyu tsakaninsu.

Sai dai tun a ranar Asabar Manchester City ta dura 5-1 a ragar Luton Town a filin wasa na Etihad a ranar Crystal Palace ta ci Liberpool 1-0 a filin wasa na Anfield a karawar mako na 33. Wannan shi ne karon farko da aka ci kungiyar Arsenal a 2024 cikin wasa

LABARAI MASU NASABA

Iwobi Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Firimiya

Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba

11 a Premier League, wadda ta tashi ba ci da Manchester City, sannan ta lashe sauran wasannin gaba daya.

Rabon da Arsenal ta dauki gasar Premier League tun kakar wasa ta 2003 zuwa 2004 mai 13 jimilla, tun daga nan ba ta sake lashe kofin ba hakan ya sa magoya bayan kungiyar suke yunwar lashe gasar.

Kungiyar Arsenal ta kare kakar bara ba tare da daukar kofi ba, bayan da Manchester City ta sha gaban Arsenal a Premier daga karshe-karshen gasar sannan hakan ya bai wa Manchester City damar lashe kofi uku ciki har da na FA Cup da kuma KofinZakarun Turai karon farko a tarihi.

Saura wasanni shida da Arsenal za ta buga nan gaba, ciki har da karawa da Chelsea da Tottenham da kuma Manchester United, inda ake tunanin za ta iya sake barar da maki.

Wasannin da suke gaban Arsenal a Premier League:

20 ga Afirilu – Wolbes ( Molineud) 23 ga Afirilu – Chelsea (Emirates) 28 ga Afirilu – Tottenham (Tottenham Stadium) 4 ga Mayu – Bournemouth (Emirates) 12 ga Mayu- Manchester United (Old Trafford) 19 ga Mayu – Eberton (Emirate) Tasirin Magoya Baya

Bayan da kungiyar kwallon kafa ta Aston Billa ta zura kwallo ta biyu a ragar Arsenal a filin wasa na Fly Emirates, magoya bayan kungiyar Arsenal sun dinga ficewa daga filin tun kafin alkalin wasa ya tashi daga wasan wanda hakan koma baya ne ga kokarin kungiyar na lashe gasar firimiya. Tsohon dan wasan Arsenal, Ian Right, ya soki matakin magoya bayan na ficewa daga filin tun kafin a tashi inda yace kwata-kwata bai kamata ba kuma hakan zai karyarwa da ‘yan wasa gwiwa. Right ya bayar da misali da magoya bayan kungiyar kwallon kafa ta Manchester United da ba sa fita har sai alkalin wasa ya tashi daga wasa saboda suna ganin indai har ba a tashi ba tabbas ‘yan wasan kungiyar za su iya faranta musu rai ta hanyar zura kwallo a raga.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Iwobi Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Firimiya
Wasanni

Iwobi Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Firimiya

October 18, 2025
Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba
Wasanni

Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba

October 18, 2025
Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa
Wasanni

Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

October 16, 2025
Next Post
Sin Ta Nuna Rashin Gamsuwa Da Barazanar Da Amurka Ta Yi Na Kara Haraji Kan Karafa Da Gorar Ruwa Dake Shiga Kasar Daga Kasar Sin

Sin Ta Nuna Rashin Gamsuwa Da Barazanar Da Amurka Ta Yi Na Kara Haraji Kan Karafa Da Gorar Ruwa Dake Shiga Kasar Daga Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.