• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin CBN Ya Umurci Bankuna Su Ba Da Tsafaffin Kudi?

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Shin CBN Ya Umurci Bankuna Su Ba Da Tsafaffin Kudi?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban bankin Nijeriya (CBN) ya bayyana ce bai bayar da wani sabon umarni ga bankunan kasuwanci ba kan hukuncin da kotun koli ta yanke a ranar Juma’ar da ta gabata na bayar da umarnin a rika amfani da tsofaffin takardun naira tare da sabbi har zuwa ranar 31 ga watan Disamba.

Kwamitin alkalai na mutane bakwai karkashin jagorancin mai shari’a Inyang Okoro, ya bayyana lamarin a matsayin wanda ya saba wa kundin tsarin mulkin kasa, umarnin da Shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya bai wa CBN na sake sauya fasalin naira tare da cire tsofaffin takardun kudi na naira 200, 500 da 1,000, ba tare da tuntubar jihohi ba, majalisar zartarwa ta kasa, majalisar jihohi da sauran masu ruwa da tsaki.

  • Zabe: CBN Ya Musanta Shirin Katse Hada-Hadar Kudi Ta Intanet 

Daily Trust ta ruwaito cewa an samu rudani a tsakanin bankunan kasuwanci da ‘yan kasuwa biyo bayan rashin bayar da umarnin da CBN bai yi ba na karbar tsofaffin takardun kudi na naira 500 da 1000. Kakakin babban bankin na CBN, Isa Abdulmumin ya bayyana cewa CBN bai fitar da wata sanarwa a hukumance ba kan wannan batu.

Sai dai wani babban jami’in bankin da ya zanta da Daily Trust ya ce: “Tsoho da kuma sababbin takardun kudi duk doka ta amince da su, kuma a halin yanzu bankuna suna ba da su ga kwastomomi. Ka da ‘yan Nijeriya su yi watsi da kudi ko tsoho ko sabo.”
Akwai karin bankunan kasuwanci a fadin kasar nan za su fara raba tsofaffin takardun kudi na naira 500 da 1000 ga kwastomominsu.

Hakan na zuwa ne sa’o’i 24 bayan da Bankin GTB ya fara raba tsofaffin takardun kudi a rassansa a fadin kasar a ranar Litinin.
Binciken da wakilinmu ya yi a Legas ya nuna cewa bankuna sun fara bayar da tsofaffin takardun kudi na naira ga kwastomomi a na’urar ATM daban-daban da kuma kan kantuna.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Reshen bankin Zenith da ke garin Festac ya biya tsofaffin takardun kudi ga abokan ciniki a kan kantuna. Haka kuma na’urorin ATM da ke rassan bankin UBA a kusa da gadar Agege-Pen Cinema da GTB da ke unguwar Ikeja a Legas, su ma suna raba tsofaffin takardun kudi.

Binciken ya kuma nuna cewa bankin WEMA ya umurci rassansa da su fara raba tsofaffin takardun kudi na naira 500 da 1000 a fadin kasar nan.

Har ila yau, wani jami’in bankin Zenith wanda ya so a sakaya sunansa ya ce reshen da suke sun sami umarnin fara raba tsofaffin takardun kudi ga abokan cinikinmu. Wani ma’aikacin bankin Zenith, Barista Dike Amadi ya ce, “An biya ni tsohuwar kudi na naira 500 a yammacin yau a wani reshen bankin Zenith da ke Fatakwal.”

Haka shi ma wani abokin ciniki mai suna Aina Dipo, ya ce, “Yanzu ana bayar da tsofaffin takardun kudi na naira 500 da 1000 a Osogbo, Jihar Osun.”
Bincike da aka yi a bankin First Bank da Polaris da kuma bankin Unity, ya nuna cewa tsohon naira 200 ne kawai suke rabawa kamar yadda CBN ya umarta.

Wani manajan bankin First Bank da ke Kano ya ce, “Ba mu samu wani daftari daga CBN ba na karbar tsofaffin takardun kudi, kuma shi ya sa hakan bai gudana ba kamar yadda muke magana a halin yanzu.”

‘Yan Kasuwa Suna Kin Amsar Tsafaffin Kudi
Sai dai kuma an sake samun wani sabon salo a rikicin, inda manyan kantuna da gidajen mai da direbobin bas na ‘yan kasuwa a wasu sassan Legas ke kin amincewa da tsofaffin takardun kudi.

Olaiya Simileoluwa, wani mazaunin Legas ya ce, “Akwai rudani a cikin wannan lamari. Kotun koli ta ce tsofaffin takardun naira za su ci gaba da aiki har zuwa watan Disamba, bankuna sun fara rarraba tsofaffin takardun kudi, amma kuma direbobin bas, manyan kantuna, gidajen mai, da sauran su ba sa karbar tsofaffin kudin. An dai jefa kasar nan cikin babban rudani. ”

Hakazalika, Kate Hensley Haziel wadda ita ma da ke zaune a Legas ta ce, “Ina ganin bayan hukuncin kotun koli, tsofaffin naira 500 da 1000 za su ci gaba da zama kudi bisa tsarin doka har zuwa Disamba 2023. Akwai bukatar CBN ya yi magana da ‘yan Nijeriya. Mutane da yawa har yanzu suna cikin rudani game da ko za su karbi tsoffin kudin ko kuma a’a. ”

‘Shugaba Buhari Ya Bukaci CBN Ya Martaba Hukuncin Kotun Koli’
Wani masani kan harkokin kudi, Gbolade Idakolo, ya ce ya kamata Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya umarci gwamnan CBN da martaba hukuncin kotun koli.

“Tsarin sake fasalin naira ya durkusar da tattalin arzikin kasa da sama da tiriliyan guda a cikin harkokin kasuwanci. Yawancin kananan masana’antu sun rufe shagunansu saboda mu’amalarsu da tsabar kudi kai-tsaye.

“Tsarin ya kara wahalhalu ga al’ummar da ke cikin damuwa, kuma hukuncin kotun koli zai kasance babban taimako ne ga mutanen kasar nan,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ra’ayoyinku A Kan Umarnin Kotun Koli Na A Ci Gaba Da Karbar Tsofaffin Kudi

Next Post

An Fara Gwagwarmayar Neman Shugabancin Majalisun Kasa

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

5 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

6 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

7 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

12 hours ago
CBN
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

12 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

13 hours ago
Next Post
majalisar kasa

An Fara Gwagwarmayar Neman Shugabancin Majalisun Kasa

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.