• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin CBN Ya Umurci Bankuna Su Ba Da Tsafaffin Kudi?

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Shin CBN Ya Umurci Bankuna Su Ba Da Tsafaffin Kudi?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban bankin Nijeriya (CBN) ya bayyana ce bai bayar da wani sabon umarni ga bankunan kasuwanci ba kan hukuncin da kotun koli ta yanke a ranar Juma’ar da ta gabata na bayar da umarnin a rika amfani da tsofaffin takardun naira tare da sabbi har zuwa ranar 31 ga watan Disamba.

Kwamitin alkalai na mutane bakwai karkashin jagorancin mai shari’a Inyang Okoro, ya bayyana lamarin a matsayin wanda ya saba wa kundin tsarin mulkin kasa, umarnin da Shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya bai wa CBN na sake sauya fasalin naira tare da cire tsofaffin takardun kudi na naira 200, 500 da 1,000, ba tare da tuntubar jihohi ba, majalisar zartarwa ta kasa, majalisar jihohi da sauran masu ruwa da tsaki.

  • Zabe: CBN Ya Musanta Shirin Katse Hada-Hadar Kudi Ta Intanet 

Daily Trust ta ruwaito cewa an samu rudani a tsakanin bankunan kasuwanci da ‘yan kasuwa biyo bayan rashin bayar da umarnin da CBN bai yi ba na karbar tsofaffin takardun kudi na naira 500 da 1000. Kakakin babban bankin na CBN, Isa Abdulmumin ya bayyana cewa CBN bai fitar da wata sanarwa a hukumance ba kan wannan batu.

Sai dai wani babban jami’in bankin da ya zanta da Daily Trust ya ce: “Tsoho da kuma sababbin takardun kudi duk doka ta amince da su, kuma a halin yanzu bankuna suna ba da su ga kwastomomi. Ka da ‘yan Nijeriya su yi watsi da kudi ko tsoho ko sabo.”
Akwai karin bankunan kasuwanci a fadin kasar nan za su fara raba tsofaffin takardun kudi na naira 500 da 1000 ga kwastomominsu.

Hakan na zuwa ne sa’o’i 24 bayan da Bankin GTB ya fara raba tsofaffin takardun kudi a rassansa a fadin kasar a ranar Litinin.
Binciken da wakilinmu ya yi a Legas ya nuna cewa bankuna sun fara bayar da tsofaffin takardun kudi na naira ga kwastomomi a na’urar ATM daban-daban da kuma kan kantuna.

Labarai Masu Nasaba

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Reshen bankin Zenith da ke garin Festac ya biya tsofaffin takardun kudi ga abokan ciniki a kan kantuna. Haka kuma na’urorin ATM da ke rassan bankin UBA a kusa da gadar Agege-Pen Cinema da GTB da ke unguwar Ikeja a Legas, su ma suna raba tsofaffin takardun kudi.

Binciken ya kuma nuna cewa bankin WEMA ya umurci rassansa da su fara raba tsofaffin takardun kudi na naira 500 da 1000 a fadin kasar nan.

Har ila yau, wani jami’in bankin Zenith wanda ya so a sakaya sunansa ya ce reshen da suke sun sami umarnin fara raba tsofaffin takardun kudi ga abokan cinikinmu. Wani ma’aikacin bankin Zenith, Barista Dike Amadi ya ce, “An biya ni tsohuwar kudi na naira 500 a yammacin yau a wani reshen bankin Zenith da ke Fatakwal.”

Haka shi ma wani abokin ciniki mai suna Aina Dipo, ya ce, “Yanzu ana bayar da tsofaffin takardun kudi na naira 500 da 1000 a Osogbo, Jihar Osun.”
Bincike da aka yi a bankin First Bank da Polaris da kuma bankin Unity, ya nuna cewa tsohon naira 200 ne kawai suke rabawa kamar yadda CBN ya umarta.

Wani manajan bankin First Bank da ke Kano ya ce, “Ba mu samu wani daftari daga CBN ba na karbar tsofaffin takardun kudi, kuma shi ya sa hakan bai gudana ba kamar yadda muke magana a halin yanzu.”

‘Yan Kasuwa Suna Kin Amsar Tsafaffin Kudi
Sai dai kuma an sake samun wani sabon salo a rikicin, inda manyan kantuna da gidajen mai da direbobin bas na ‘yan kasuwa a wasu sassan Legas ke kin amincewa da tsofaffin takardun kudi.

Olaiya Simileoluwa, wani mazaunin Legas ya ce, “Akwai rudani a cikin wannan lamari. Kotun koli ta ce tsofaffin takardun naira za su ci gaba da aiki har zuwa watan Disamba, bankuna sun fara rarraba tsofaffin takardun kudi, amma kuma direbobin bas, manyan kantuna, gidajen mai, da sauran su ba sa karbar tsofaffin kudin. An dai jefa kasar nan cikin babban rudani. ”

Hakazalika, Kate Hensley Haziel wadda ita ma da ke zaune a Legas ta ce, “Ina ganin bayan hukuncin kotun koli, tsofaffin naira 500 da 1000 za su ci gaba da zama kudi bisa tsarin doka har zuwa Disamba 2023. Akwai bukatar CBN ya yi magana da ‘yan Nijeriya. Mutane da yawa har yanzu suna cikin rudani game da ko za su karbi tsoffin kudin ko kuma a’a. ”

‘Shugaba Buhari Ya Bukaci CBN Ya Martaba Hukuncin Kotun Koli’
Wani masani kan harkokin kudi, Gbolade Idakolo, ya ce ya kamata Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya umarci gwamnan CBN da martaba hukuncin kotun koli.

“Tsarin sake fasalin naira ya durkusar da tattalin arzikin kasa da sama da tiriliyan guda a cikin harkokin kasuwanci. Yawancin kananan masana’antu sun rufe shagunansu saboda mu’amalarsu da tsabar kudi kai-tsaye.

“Tsarin ya kara wahalhalu ga al’ummar da ke cikin damuwa, kuma hukuncin kotun koli zai kasance babban taimako ne ga mutanen kasar nan,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ra’ayoyinku A Kan Umarnin Kotun Koli Na A Ci Gaba Da Karbar Tsofaffin Kudi

Next Post

An Fara Gwagwarmayar Neman Shugabancin Majalisun Kasa

Related

Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…
Manyan Labarai

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

14 minutes ago
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

10 hours ago
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano
Labarai

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

11 hours ago
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta
Labarai

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

13 hours ago
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

13 hours ago
EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi
Labarai

EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi

14 hours ago
Next Post
majalisar kasa

An Fara Gwagwarmayar Neman Shugabancin Majalisun Kasa

LABARAI MASU NASABA

Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.