ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin CBN Ya Umurci Bankuna Su Ba Da Tsafaffin Kudi?

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
CBN

Babban bankin Nijeriya (CBN) ya bayyana ce bai bayar da wani sabon umarni ga bankunan kasuwanci ba kan hukuncin da kotun koli ta yanke a ranar Juma’ar da ta gabata na bayar da umarnin a rika amfani da tsofaffin takardun naira tare da sabbi har zuwa ranar 31 ga watan Disamba.

Kwamitin alkalai na mutane bakwai karkashin jagorancin mai shari’a Inyang Okoro, ya bayyana lamarin a matsayin wanda ya saba wa kundin tsarin mulkin kasa, umarnin da Shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya bai wa CBN na sake sauya fasalin naira tare da cire tsofaffin takardun kudi na naira 200, 500 da 1,000, ba tare da tuntubar jihohi ba, majalisar zartarwa ta kasa, majalisar jihohi da sauran masu ruwa da tsaki.

  • Zabe: CBN Ya Musanta Shirin Katse Hada-Hadar Kudi Ta Intanet 

Daily Trust ta ruwaito cewa an samu rudani a tsakanin bankunan kasuwanci da ‘yan kasuwa biyo bayan rashin bayar da umarnin da CBN bai yi ba na karbar tsofaffin takardun kudi na naira 500 da 1000. Kakakin babban bankin na CBN, Isa Abdulmumin ya bayyana cewa CBN bai fitar da wata sanarwa a hukumance ba kan wannan batu.

ADVERTISEMENT

Sai dai wani babban jami’in bankin da ya zanta da Daily Trust ya ce: “Tsoho da kuma sababbin takardun kudi duk doka ta amince da su, kuma a halin yanzu bankuna suna ba da su ga kwastomomi. Ka da ‘yan Nijeriya su yi watsi da kudi ko tsoho ko sabo.”
Akwai karin bankunan kasuwanci a fadin kasar nan za su fara raba tsofaffin takardun kudi na naira 500 da 1000 ga kwastomominsu.

Hakan na zuwa ne sa’o’i 24 bayan da Bankin GTB ya fara raba tsofaffin takardun kudi a rassansa a fadin kasar a ranar Litinin.
Binciken da wakilinmu ya yi a Legas ya nuna cewa bankuna sun fara bayar da tsofaffin takardun kudi na naira ga kwastomomi a na’urar ATM daban-daban da kuma kan kantuna.

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Reshen bankin Zenith da ke garin Festac ya biya tsofaffin takardun kudi ga abokan ciniki a kan kantuna. Haka kuma na’urorin ATM da ke rassan bankin UBA a kusa da gadar Agege-Pen Cinema da GTB da ke unguwar Ikeja a Legas, su ma suna raba tsofaffin takardun kudi.

Binciken ya kuma nuna cewa bankin WEMA ya umurci rassansa da su fara raba tsofaffin takardun kudi na naira 500 da 1000 a fadin kasar nan.

Har ila yau, wani jami’in bankin Zenith wanda ya so a sakaya sunansa ya ce reshen da suke sun sami umarnin fara raba tsofaffin takardun kudi ga abokan cinikinmu. Wani ma’aikacin bankin Zenith, Barista Dike Amadi ya ce, “An biya ni tsohuwar kudi na naira 500 a yammacin yau a wani reshen bankin Zenith da ke Fatakwal.”

Haka shi ma wani abokin ciniki mai suna Aina Dipo, ya ce, “Yanzu ana bayar da tsofaffin takardun kudi na naira 500 da 1000 a Osogbo, Jihar Osun.”
Bincike da aka yi a bankin First Bank da Polaris da kuma bankin Unity, ya nuna cewa tsohon naira 200 ne kawai suke rabawa kamar yadda CBN ya umarta.

Wani manajan bankin First Bank da ke Kano ya ce, “Ba mu samu wani daftari daga CBN ba na karbar tsofaffin takardun kudi, kuma shi ya sa hakan bai gudana ba kamar yadda muke magana a halin yanzu.”

‘Yan Kasuwa Suna Kin Amsar Tsafaffin Kudi
Sai dai kuma an sake samun wani sabon salo a rikicin, inda manyan kantuna da gidajen mai da direbobin bas na ‘yan kasuwa a wasu sassan Legas ke kin amincewa da tsofaffin takardun kudi.

Olaiya Simileoluwa, wani mazaunin Legas ya ce, “Akwai rudani a cikin wannan lamari. Kotun koli ta ce tsofaffin takardun naira za su ci gaba da aiki har zuwa watan Disamba, bankuna sun fara rarraba tsofaffin takardun kudi, amma kuma direbobin bas, manyan kantuna, gidajen mai, da sauran su ba sa karbar tsofaffin kudin. An dai jefa kasar nan cikin babban rudani. ”

Hakazalika, Kate Hensley Haziel wadda ita ma da ke zaune a Legas ta ce, “Ina ganin bayan hukuncin kotun koli, tsofaffin naira 500 da 1000 za su ci gaba da zama kudi bisa tsarin doka har zuwa Disamba 2023. Akwai bukatar CBN ya yi magana da ‘yan Nijeriya. Mutane da yawa har yanzu suna cikin rudani game da ko za su karbi tsoffin kudin ko kuma a’a. ”

‘Shugaba Buhari Ya Bukaci CBN Ya Martaba Hukuncin Kotun Koli’
Wani masani kan harkokin kudi, Gbolade Idakolo, ya ce ya kamata Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya umarci gwamnan CBN da martaba hukuncin kotun koli.

“Tsarin sake fasalin naira ya durkusar da tattalin arzikin kasa da sama da tiriliyan guda a cikin harkokin kasuwanci. Yawancin kananan masana’antu sun rufe shagunansu saboda mu’amalarsu da tsabar kudi kai-tsaye.

“Tsarin ya kara wahalhalu ga al’ummar da ke cikin damuwa, kuma hukuncin kotun koli zai kasance babban taimako ne ga mutanen kasar nan,” in ji shi.

CBN
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

MASU ALAKA

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Next Post
majalisar kasa

An Fara Gwagwarmayar Neman Shugabancin Majalisun Kasa

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.