ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin CBN Ya Umurci Bankuna Su Ba Da Tsafaffin Kudi?

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
CBN

Babban bankin Nijeriya (CBN) ya bayyana ce bai bayar da wani sabon umarni ga bankunan kasuwanci ba kan hukuncin da kotun koli ta yanke a ranar Juma’ar da ta gabata na bayar da umarnin a rika amfani da tsofaffin takardun naira tare da sabbi har zuwa ranar 31 ga watan Disamba.

Kwamitin alkalai na mutane bakwai karkashin jagorancin mai shari’a Inyang Okoro, ya bayyana lamarin a matsayin wanda ya saba wa kundin tsarin mulkin kasa, umarnin da Shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya bai wa CBN na sake sauya fasalin naira tare da cire tsofaffin takardun kudi na naira 200, 500 da 1,000, ba tare da tuntubar jihohi ba, majalisar zartarwa ta kasa, majalisar jihohi da sauran masu ruwa da tsaki.

  • Zabe: CBN Ya Musanta Shirin Katse Hada-Hadar Kudi Ta Intanet 

Daily Trust ta ruwaito cewa an samu rudani a tsakanin bankunan kasuwanci da ‘yan kasuwa biyo bayan rashin bayar da umarnin da CBN bai yi ba na karbar tsofaffin takardun kudi na naira 500 da 1000. Kakakin babban bankin na CBN, Isa Abdulmumin ya bayyana cewa CBN bai fitar da wata sanarwa a hukumance ba kan wannan batu.

ADVERTISEMENT

Sai dai wani babban jami’in bankin da ya zanta da Daily Trust ya ce: “Tsoho da kuma sababbin takardun kudi duk doka ta amince da su, kuma a halin yanzu bankuna suna ba da su ga kwastomomi. Ka da ‘yan Nijeriya su yi watsi da kudi ko tsoho ko sabo.”
Akwai karin bankunan kasuwanci a fadin kasar nan za su fara raba tsofaffin takardun kudi na naira 500 da 1000 ga kwastomominsu.

Hakan na zuwa ne sa’o’i 24 bayan da Bankin GTB ya fara raba tsofaffin takardun kudi a rassansa a fadin kasar a ranar Litinin.
Binciken da wakilinmu ya yi a Legas ya nuna cewa bankuna sun fara bayar da tsofaffin takardun kudi na naira ga kwastomomi a na’urar ATM daban-daban da kuma kan kantuna.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Reshen bankin Zenith da ke garin Festac ya biya tsofaffin takardun kudi ga abokan ciniki a kan kantuna. Haka kuma na’urorin ATM da ke rassan bankin UBA a kusa da gadar Agege-Pen Cinema da GTB da ke unguwar Ikeja a Legas, su ma suna raba tsofaffin takardun kudi.

Binciken ya kuma nuna cewa bankin WEMA ya umurci rassansa da su fara raba tsofaffin takardun kudi na naira 500 da 1000 a fadin kasar nan.

Har ila yau, wani jami’in bankin Zenith wanda ya so a sakaya sunansa ya ce reshen da suke sun sami umarnin fara raba tsofaffin takardun kudi ga abokan cinikinmu. Wani ma’aikacin bankin Zenith, Barista Dike Amadi ya ce, “An biya ni tsohuwar kudi na naira 500 a yammacin yau a wani reshen bankin Zenith da ke Fatakwal.”

Haka shi ma wani abokin ciniki mai suna Aina Dipo, ya ce, “Yanzu ana bayar da tsofaffin takardun kudi na naira 500 da 1000 a Osogbo, Jihar Osun.”
Bincike da aka yi a bankin First Bank da Polaris da kuma bankin Unity, ya nuna cewa tsohon naira 200 ne kawai suke rabawa kamar yadda CBN ya umarta.

Wani manajan bankin First Bank da ke Kano ya ce, “Ba mu samu wani daftari daga CBN ba na karbar tsofaffin takardun kudi, kuma shi ya sa hakan bai gudana ba kamar yadda muke magana a halin yanzu.”

‘Yan Kasuwa Suna Kin Amsar Tsafaffin Kudi
Sai dai kuma an sake samun wani sabon salo a rikicin, inda manyan kantuna da gidajen mai da direbobin bas na ‘yan kasuwa a wasu sassan Legas ke kin amincewa da tsofaffin takardun kudi.

Olaiya Simileoluwa, wani mazaunin Legas ya ce, “Akwai rudani a cikin wannan lamari. Kotun koli ta ce tsofaffin takardun naira za su ci gaba da aiki har zuwa watan Disamba, bankuna sun fara rarraba tsofaffin takardun kudi, amma kuma direbobin bas, manyan kantuna, gidajen mai, da sauran su ba sa karbar tsofaffin kudin. An dai jefa kasar nan cikin babban rudani. ”

Hakazalika, Kate Hensley Haziel wadda ita ma da ke zaune a Legas ta ce, “Ina ganin bayan hukuncin kotun koli, tsofaffin naira 500 da 1000 za su ci gaba da zama kudi bisa tsarin doka har zuwa Disamba 2023. Akwai bukatar CBN ya yi magana da ‘yan Nijeriya. Mutane da yawa har yanzu suna cikin rudani game da ko za su karbi tsoffin kudin ko kuma a’a. ”

‘Shugaba Buhari Ya Bukaci CBN Ya Martaba Hukuncin Kotun Koli’
Wani masani kan harkokin kudi, Gbolade Idakolo, ya ce ya kamata Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya umarci gwamnan CBN da martaba hukuncin kotun koli.

“Tsarin sake fasalin naira ya durkusar da tattalin arzikin kasa da sama da tiriliyan guda a cikin harkokin kasuwanci. Yawancin kananan masana’antu sun rufe shagunansu saboda mu’amalarsu da tsabar kudi kai-tsaye.

“Tsarin ya kara wahalhalu ga al’ummar da ke cikin damuwa, kuma hukuncin kotun koli zai kasance babban taimako ne ga mutanen kasar nan,” in ji shi.

CBN
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Labarai

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Next Post
majalisar kasa

An Fara Gwagwarmayar Neman Shugabancin Majalisun Kasa

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.