• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Dalibai Na Da Wakilai A Tattaunawa Tsakanin ASUU Da Gwamnati Kan Yajin Aikin ASUU Kuwa?

by Sallau Kaisi Dauda
3 years ago
ASUU

Ni ban san ma ina shugabanni Kungiyar Daliban Jami’o’in ta Kasa (NANS) da na jihohi suka shiga tun a lokacin da aka fara yajin aikin da ya ki ci ya ki cinyewa tsakanin ASUU da Gwamnatin Tarayya.

Shin suna ma raye kuwa? Shin suna ma da wakilai a cikin kwamitin da ake zaman tattaunawa tsakanin Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) da Gwamnatin tarayya?

  • Sai Mun Yi Gwajin Miyagun Kwayoyi Kafin Daura Aure A Abuja – NDLEA
  • APC Ta Dunkule Kan Tinubu, PDP Na Kokarin Sulhu Da Wike

Idan suna da su, ina su ke? Mai suka ce? Idan ba su da wakilai a zaman. To mai ya sa? Dole ya kamata a ce dalibai na da wakilci cikin zaman, domin lamarin ya shafe bangarori uku ne; ASUU, Gwamnatin Tarayya da kuma dalibai, saboda haka ya kamata kowa na da wakilci a zaman.

Gwamnati da wakilai dalibai kowa ya mallaki duk takardun bukatun ASUU, ta nan ne su daliban za su fahimci ina aka nufa.

Mai gwamnati ta ce za ta yi, mai ta ce ba za ta yi ba. Amma matukar dalibai basu da wakilai a cikin zaman, to cikin duhu za su kasance ko da yaushe. Domin ko an janye yajin aikin za a sa ke komawa.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

Domin bana ganin kaman shugabannin kungiyar dalibai na taimaka wa daliban yadda ya kamata domin kawo karshen wannan yajin aikin na ASUU.

Matakai da shugabannin kungiyar daliban suke dauka bai gamsar da ni kamar suna yi wa daliban shugabanci yadda ya kamata ba.

Kamata ya yi yadda mu ke ganin shugabannin ASUU da na Gwamnatin Tarayya kullum cikin gidan talabijin da jaridu, su ma a dinga ganin su haka muna jin inda suka dosa da sauransu kan lamarin.

Domin su za su matsa wa ASUU da gwamnati su yi abin da ya kamata. Idan kai da abu ya shafe ka kai tsaye baka nuna ka damu ba, to ina kuma ga wani daban?

Wannan yajin aikin ASUU ba wanda bai shafa ba, amma kai tsaye ta fi shafar daliban Jami’a. Saboda haka su ya kamata a fi jin su a ko da yaushe, amma shiru kake ji.

Na fahimci da ASUU da gwamnati kowa na da maganar banza a bakin shi. Idan fa har da gaske suke yi, to dole ASUU da gwamnati su daina fitowa suna jefa wa juna maganganun banza wanda bai dace ba. Sannan su daina fito da abin da da suka tattauna a zaman da suke yi har sai sun samu matsaya.

Saboda ‘yan jaridu da wadansu mutane na kara rura wutar yakin da ke tsakanin ASUU da gwamnati.

Su kuma shugabannin kungiyar daliban jami’a kamar ba sa raye a duniya. Dole su ma za su matsa wa ASUU da gwamnati su yi abin da ya kamata. Idan ba su da wakilai a zaman da ake yi, su nema dole suma a sa su cikin zaman.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman
Kananan Labarai

Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman

September 26, 2025
Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa
Kananan Labarai

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

May 23, 2025
Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya
Kananan Labarai

Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya

April 18, 2025
Next Post
Kasurgumin Dan Bindiga ‘Bello Turji’ Ya Rungumi Zaman Lafiya, Ya Koma Yakar ‘Yan Bindiga – Gwamnati

Kasurgumin Dan Bindiga 'Bello Turji' Ya Rungumi Zaman Lafiya, Ya Koma Yakar 'Yan Bindiga - Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.