• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Ko Kun San Tarihin Kurkukun Gontanamu Bay?

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
in Rahotonni
0
Gontanamu bay
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gontanamo dai wani sansani ne na sojojin Amurka da yake a Kasar Kyuba, kuma shi kadai ne sansanin sojojin Amurka a wata Kasa Mai bin tsarin kwaminisanci.

Shi dai wannan sansani yana Kudu maso Yammacin Kasar ta Kyuba, kusan tafiyar mil 400 daga garin Miyami, kuma sama da mutanen Kasar Amurka kimanin 3000 ne a wannan sansani, wadanda suka hada da sojoji da farar hula da kuma iyalansu.

  • Turai Ta San Ra’ayin Amurka Kan Dangantakar Dake Tsakaninsu

Wannan sansani ya samo asali ne daga tarihin tsohon tsarin sansanonin Amurka a Kasashen Duniya. Tsarawa da kuma sanya wannan sansani a Kasar Kyuba ya faru ne tun lokacin da akai yaki tsakanin Kasar Amurka da Kasar Spaniya, lokacin da sojojin Amurka suka samu galaba akan sojojin Spaniya na rundunar “Caribbean’’ a kusa da garin Santiago da ke Kasar Kyuba a shekarar 1898.

A shekarar 1903 ne dai Kasar Amurka ta karbi hayar yankin daga Kasar Kyuba domin amfani da shi a matsayin tashar shan mai ga rundunar sojojinta na ruwa, amma a shekarar 1934 wa’adin yarjejeniyar da Kasashen biyu suka yi ya cika.

A lokacin da shugaban Kasar Amurka Eisenhower ya yanke huldar jakadanci da Kasar Kyuba a shekarar 1961, sai dubban ’yan gudun hijira na Kasar Kyuba suka cika sansanin. Kai da shekara ta zagayo ma sai jami’an sojan Kasar ta Kyuba su kai kaura zuwa sansanin na watanni da dama, a lokacin rikici akan makamai masu linzami na Kasar ta kyuba.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

A shekara ta 1964 sansanin sojojin ruwan akan dole ya zama mai dogaro da kansa bayan shugaba Fidel Castro ya yanke wa sansanin wutar lantarki da kuma ruwan sha.

A shekarar 1991 sansanin ya zama wani masauki na wucin gadi ga dubban masu kaura daga Kasar Haiti, wadanda suka gudu domin tsoron juyin mulkin sojoji a kasar. Haka zalika a shekarar 1994 an yi wa wasu makauratan kimanin su 45,000 daga Cuba da Haiti masauki na wucingadi a wannan sansani.

Kamar yadda bayanai suka nunar daga Kasar ta Amurka, babban burin wannan sansani shi ne, ya kasance a matsayin wani sansani na samar da kayayyakin aiki ga rundunar sojojin ruwa na yakin Caribbean jiddan walahairan suna sintiri a kewayen sansanin.

To tuni dai sansanin na Guantanamo Bay ya dawo cikin labarun yau kullum, kuma a farkon shekara ta 2002 ne aka gina wani kurkuku a sansanin da ya haifar da kace-na ce a halin yanzu, wanda a ke kira da Turanci (Camp D-Ray) in da ake tsare da musulmi ’yan gwagwarmaya musamman ma wadanda ake zarginsu da alaka da kungiyar Al-Ka’ida da Taliban.

Tarzoma a kurkukun guantanamo
Wasu masu gadin kurkukun soji na tsibirin Guantanamo sun yi ta harbe- harbe da harsashen roba don kwantar da tarzomar da ta barke a gidan kurkukun.
Tarzomar ta abku ne lokacin da ake kokarin mai da fursunonin dakunan da ake tsare da su.

Jami’ai a gidan kurkukun na gwamnatin Amurka dake Cuba sun ce wasu fursunoni ne suka yi amfani da wasu makamai da suka harhada don hana komawa da su cikin dakunansu.

Zaman dar-dar ya karu a gidan kurkukun sakamakon yajin kin cin abinci da wasu fursunonin suka fara tun a watan Fabrairu, bayan da wasu fursunoni suka zargi masu gadinsu da bincika Kur’anan da suke amfani da su kan ko suna dauke da wasu abubuwa da aka haramta.

Jami’an gidan kurkukun na Guantanamo sun ce fursuna guda ne kawai ya samu raunuka lokacin tarzomar.

Kungiyoyin Kare Hakkin bil-‘Adama da lauyoyi sun ce, wannan na faruwa ne sakamakon gazawar da hukumomin suka yi wajen yanke shawarar yadda za su tafiyar da fursunonin, da akasarin su sun shafe fiye da shekaru goma.

Bayanai dai sun ce Jami’an gwamnatin Amurka sun riga sun ba da umarnin a saki kimanin casa’in daga cikin fursunonin, amma kuma har yanzu ana ci gaba da rike.

Wannan kuwa na faruwa ne sakamakon wasu dalilai da suka shafi ka’idojin fitar da su daga gidan kurkukun, da kuma tunanin yiwuwar musguna musu bayan an maishe su kasashensu.

Yawan fursunonin da ke yajin kin cin abinci a guantanamo ya kai 100
Yawan fursunonin da ke yajin kin cin abinci a gidan kurkukun ihunka banza da Amurka ta kafa a tsibirin Guantanamo sun kai 100 daga cikin 166 da ake tsare da su a halin yanzu.

Tun a ranar 6 ga watan Fabarairun da ya gabata ne dai fursunonin suka soma yajin kin cin abinci, kuma 20 daga cikinsu na a cikin mawuyacin hali, inda tuni hukumomin gidan yarin suka soma yi masu duren abinci ta hanyar saka masu wani bututu da ke isa a uwar hanjinsu.

Laftal-kanar Samuel House, daya daga cikin manyan jami’an gidan yarin na Guantanamo, ya ce yanzu haka akwai wasu fursunoni biyar da aka kwantar a asibiti sakamakon yadda suka tagayyara.

Su dai wadannan fursunoni sun shiga yajin kin cin abinci ne domin nuna rashin amincewarsu dangane da yadda ake tsare da su ba tare da an gurfanar da su a gaban alkali ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Honarabul Datti Babawo: Yadda Al’umma Ke Cin Gajiyar Shirinsa Na Bunkasa Kiwon Lafiya

Next Post

2023: Ana Rantsar Da Ni Zan Fara Sauya Fasalin Nijeriya – Atiku

Related

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

6 days ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

1 week ago
Fyade
Rahotonni

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

2 weeks ago
APC
Manyan Labarai

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

2 weeks ago
Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Sanar Da Dakatar Da Ayyukanta Saboda Alhinin Rasuwar Buhari
Labarai

Na Shiga Aikin Soja Domin Gujewa Yin Auren Fari Da Ƙuruciya — Buhari

3 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

3 weeks ago
Next Post
2023: Ana Rantsar Da Ni Zan Fara Sauya Fasalin Nijeriya –  Atiku

2023: Ana Rantsar Da Ni Zan Fara Sauya Fasalin Nijeriya - Atiku

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi HaÉ—in Gwiwa

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi HaÉ—in Gwiwa

August 1, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

August 1, 2025
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto DimokuraÉ—iyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto DimokuraÉ—iyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

August 1, 2025
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

August 1, 2025
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

August 1, 2025
An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.