• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Ko Kun San Tarihin Kurkukun Gontanamu Bay?

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
in Rahotonni
0
Gontanamu bay
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gontanamo dai wani sansani ne na sojojin Amurka da yake a Kasar Kyuba, kuma shi kadai ne sansanin sojojin Amurka a wata Kasa Mai bin tsarin kwaminisanci.

Shi dai wannan sansani yana Kudu maso Yammacin Kasar ta Kyuba, kusan tafiyar mil 400 daga garin Miyami, kuma sama da mutanen Kasar Amurka kimanin 3000 ne a wannan sansani, wadanda suka hada da sojoji da farar hula da kuma iyalansu.

  • Turai Ta San Ra’ayin Amurka Kan Dangantakar Dake Tsakaninsu

Wannan sansani ya samo asali ne daga tarihin tsohon tsarin sansanonin Amurka a Kasashen Duniya. Tsarawa da kuma sanya wannan sansani a Kasar Kyuba ya faru ne tun lokacin da akai yaki tsakanin Kasar Amurka da Kasar Spaniya, lokacin da sojojin Amurka suka samu galaba akan sojojin Spaniya na rundunar “Caribbean’’ a kusa da garin Santiago da ke Kasar Kyuba a shekarar 1898.

A shekarar 1903 ne dai Kasar Amurka ta karbi hayar yankin daga Kasar Kyuba domin amfani da shi a matsayin tashar shan mai ga rundunar sojojinta na ruwa, amma a shekarar 1934 wa’adin yarjejeniyar da Kasashen biyu suka yi ya cika.

A lokacin da shugaban Kasar Amurka Eisenhower ya yanke huldar jakadanci da Kasar Kyuba a shekarar 1961, sai dubban ’yan gudun hijira na Kasar Kyuba suka cika sansanin. Kai da shekara ta zagayo ma sai jami’an sojan Kasar ta Kyuba su kai kaura zuwa sansanin na watanni da dama, a lokacin rikici akan makamai masu linzami na Kasar ta kyuba.

Labarai Masu Nasaba

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

A shekara ta 1964 sansanin sojojin ruwan akan dole ya zama mai dogaro da kansa bayan shugaba Fidel Castro ya yanke wa sansanin wutar lantarki da kuma ruwan sha.

A shekarar 1991 sansanin ya zama wani masauki na wucin gadi ga dubban masu kaura daga Kasar Haiti, wadanda suka gudu domin tsoron juyin mulkin sojoji a kasar. Haka zalika a shekarar 1994 an yi wa wasu makauratan kimanin su 45,000 daga Cuba da Haiti masauki na wucingadi a wannan sansani.

Kamar yadda bayanai suka nunar daga Kasar ta Amurka, babban burin wannan sansani shi ne, ya kasance a matsayin wani sansani na samar da kayayyakin aiki ga rundunar sojojin ruwa na yakin Caribbean jiddan walahairan suna sintiri a kewayen sansanin.

To tuni dai sansanin na Guantanamo Bay ya dawo cikin labarun yau kullum, kuma a farkon shekara ta 2002 ne aka gina wani kurkuku a sansanin da ya haifar da kace-na ce a halin yanzu, wanda a ke kira da Turanci (Camp D-Ray) in da ake tsare da musulmi ’yan gwagwarmaya musamman ma wadanda ake zarginsu da alaka da kungiyar Al-Ka’ida da Taliban.

Tarzoma a kurkukun guantanamo
Wasu masu gadin kurkukun soji na tsibirin Guantanamo sun yi ta harbe- harbe da harsashen roba don kwantar da tarzomar da ta barke a gidan kurkukun.
Tarzomar ta abku ne lokacin da ake kokarin mai da fursunonin dakunan da ake tsare da su.

Jami’ai a gidan kurkukun na gwamnatin Amurka dake Cuba sun ce wasu fursunoni ne suka yi amfani da wasu makamai da suka harhada don hana komawa da su cikin dakunansu.

Zaman dar-dar ya karu a gidan kurkukun sakamakon yajin kin cin abinci da wasu fursunonin suka fara tun a watan Fabrairu, bayan da wasu fursunoni suka zargi masu gadinsu da bincika Kur’anan da suke amfani da su kan ko suna dauke da wasu abubuwa da aka haramta.

Jami’an gidan kurkukun na Guantanamo sun ce fursuna guda ne kawai ya samu raunuka lokacin tarzomar.

Kungiyoyin Kare Hakkin bil-‘Adama da lauyoyi sun ce, wannan na faruwa ne sakamakon gazawar da hukumomin suka yi wajen yanke shawarar yadda za su tafiyar da fursunonin, da akasarin su sun shafe fiye da shekaru goma.

Bayanai dai sun ce Jami’an gwamnatin Amurka sun riga sun ba da umarnin a saki kimanin casa’in daga cikin fursunonin, amma kuma har yanzu ana ci gaba da rike.

Wannan kuwa na faruwa ne sakamakon wasu dalilai da suka shafi ka’idojin fitar da su daga gidan kurkukun, da kuma tunanin yiwuwar musguna musu bayan an maishe su kasashensu.

Yawan fursunonin da ke yajin kin cin abinci a guantanamo ya kai 100
Yawan fursunonin da ke yajin kin cin abinci a gidan kurkukun ihunka banza da Amurka ta kafa a tsibirin Guantanamo sun kai 100 daga cikin 166 da ake tsare da su a halin yanzu.

Tun a ranar 6 ga watan Fabarairun da ya gabata ne dai fursunonin suka soma yajin kin cin abinci, kuma 20 daga cikinsu na a cikin mawuyacin hali, inda tuni hukumomin gidan yarin suka soma yi masu duren abinci ta hanyar saka masu wani bututu da ke isa a uwar hanjinsu.

Laftal-kanar Samuel House, daya daga cikin manyan jami’an gidan yarin na Guantanamo, ya ce yanzu haka akwai wasu fursunoni biyar da aka kwantar a asibiti sakamakon yadda suka tagayyara.

Su dai wadannan fursunoni sun shiga yajin kin cin abinci ne domin nuna rashin amincewarsu dangane da yadda ake tsare da su ba tare da an gurfanar da su a gaban alkali ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Honarabul Datti Babawo: Yadda Al’umma Ke Cin Gajiyar Shirinsa Na Bunkasa Kiwon Lafiya

Next Post

2023: Ana Rantsar Da Ni Zan Fara Sauya Fasalin Nijeriya – Atiku

Related

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

10 hours ago
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya
Rahotonni

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

20 hours ago
Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin
Rahotonni

Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin

2 days ago
Yadda Sanata Barau Ke Samar da Masana Don Ci Gaban Kano
Rahotonni

Yadda Sanata Barau Ke Samar da Masana Don Ci Gaban Kano

2 days ago
Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu
Rahotonni

Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu

1 week ago
Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba
Rahotonni

Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba

1 week ago
Next Post
2023: Ana Rantsar Da Ni Zan Fara Sauya Fasalin Nijeriya –  Atiku

2023: Ana Rantsar Da Ni Zan Fara Sauya Fasalin Nijeriya - Atiku

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.