ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Ko Kun San Tarihin Kurkukun Gontanamu Bay?

by Rabi'u Ali Indabawa
4 years ago
Gontanamu bay

Gontanamo dai wani sansani ne na sojojin Amurka da yake a Kasar Kyuba, kuma shi kadai ne sansanin sojojin Amurka a wata Kasa Mai bin tsarin kwaminisanci.

Shi dai wannan sansani yana Kudu maso Yammacin Kasar ta Kyuba, kusan tafiyar mil 400 daga garin Miyami, kuma sama da mutanen Kasar Amurka kimanin 3000 ne a wannan sansani, wadanda suka hada da sojoji da farar hula da kuma iyalansu.

  • Turai Ta San Ra’ayin Amurka Kan Dangantakar Dake Tsakaninsu

Wannan sansani ya samo asali ne daga tarihin tsohon tsarin sansanonin Amurka a Kasashen Duniya. Tsarawa da kuma sanya wannan sansani a Kasar Kyuba ya faru ne tun lokacin da akai yaki tsakanin Kasar Amurka da Kasar Spaniya, lokacin da sojojin Amurka suka samu galaba akan sojojin Spaniya na rundunar “Caribbean’’ a kusa da garin Santiago da ke Kasar Kyuba a shekarar 1898.

ADVERTISEMENT

A shekarar 1903 ne dai Kasar Amurka ta karbi hayar yankin daga Kasar Kyuba domin amfani da shi a matsayin tashar shan mai ga rundunar sojojinta na ruwa, amma a shekarar 1934 wa’adin yarjejeniyar da Kasashen biyu suka yi ya cika.

A lokacin da shugaban Kasar Amurka Eisenhower ya yanke huldar jakadanci da Kasar Kyuba a shekarar 1961, sai dubban ’yan gudun hijira na Kasar Kyuba suka cika sansanin. Kai da shekara ta zagayo ma sai jami’an sojan Kasar ta Kyuba su kai kaura zuwa sansanin na watanni da dama, a lokacin rikici akan makamai masu linzami na Kasar ta kyuba.

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

A shekara ta 1964 sansanin sojojin ruwan akan dole ya zama mai dogaro da kansa bayan shugaba Fidel Castro ya yanke wa sansanin wutar lantarki da kuma ruwan sha.

A shekarar 1991 sansanin ya zama wani masauki na wucin gadi ga dubban masu kaura daga Kasar Haiti, wadanda suka gudu domin tsoron juyin mulkin sojoji a kasar. Haka zalika a shekarar 1994 an yi wa wasu makauratan kimanin su 45,000 daga Cuba da Haiti masauki na wucingadi a wannan sansani.

Kamar yadda bayanai suka nunar daga Kasar ta Amurka, babban burin wannan sansani shi ne, ya kasance a matsayin wani sansani na samar da kayayyakin aiki ga rundunar sojojin ruwa na yakin Caribbean jiddan walahairan suna sintiri a kewayen sansanin.

To tuni dai sansanin na Guantanamo Bay ya dawo cikin labarun yau kullum, kuma a farkon shekara ta 2002 ne aka gina wani kurkuku a sansanin da ya haifar da kace-na ce a halin yanzu, wanda a ke kira da Turanci (Camp D-Ray) in da ake tsare da musulmi ’yan gwagwarmaya musamman ma wadanda ake zarginsu da alaka da kungiyar Al-Ka’ida da Taliban.

Tarzoma a kurkukun guantanamo
Wasu masu gadin kurkukun soji na tsibirin Guantanamo sun yi ta harbe- harbe da harsashen roba don kwantar da tarzomar da ta barke a gidan kurkukun.
Tarzomar ta abku ne lokacin da ake kokarin mai da fursunonin dakunan da ake tsare da su.

Jami’ai a gidan kurkukun na gwamnatin Amurka dake Cuba sun ce wasu fursunoni ne suka yi amfani da wasu makamai da suka harhada don hana komawa da su cikin dakunansu.

Zaman dar-dar ya karu a gidan kurkukun sakamakon yajin kin cin abinci da wasu fursunonin suka fara tun a watan Fabrairu, bayan da wasu fursunoni suka zargi masu gadinsu da bincika Kur’anan da suke amfani da su kan ko suna dauke da wasu abubuwa da aka haramta.

Jami’an gidan kurkukun na Guantanamo sun ce fursuna guda ne kawai ya samu raunuka lokacin tarzomar.

Kungiyoyin Kare Hakkin bil-‘Adama da lauyoyi sun ce, wannan na faruwa ne sakamakon gazawar da hukumomin suka yi wajen yanke shawarar yadda za su tafiyar da fursunonin, da akasarin su sun shafe fiye da shekaru goma.

Bayanai dai sun ce Jami’an gwamnatin Amurka sun riga sun ba da umarnin a saki kimanin casa’in daga cikin fursunonin, amma kuma har yanzu ana ci gaba da rike.

Wannan kuwa na faruwa ne sakamakon wasu dalilai da suka shafi ka’idojin fitar da su daga gidan kurkukun, da kuma tunanin yiwuwar musguna musu bayan an maishe su kasashensu.

Yawan fursunonin da ke yajin kin cin abinci a guantanamo ya kai 100
Yawan fursunonin da ke yajin kin cin abinci a gidan kurkukun ihunka banza da Amurka ta kafa a tsibirin Guantanamo sun kai 100 daga cikin 166 da ake tsare da su a halin yanzu.

Tun a ranar 6 ga watan Fabarairun da ya gabata ne dai fursunonin suka soma yajin kin cin abinci, kuma 20 daga cikinsu na a cikin mawuyacin hali, inda tuni hukumomin gidan yarin suka soma yi masu duren abinci ta hanyar saka masu wani bututu da ke isa a uwar hanjinsu.

Laftal-kanar Samuel House, daya daga cikin manyan jami’an gidan yarin na Guantanamo, ya ce yanzu haka akwai wasu fursunoni biyar da aka kwantar a asibiti sakamakon yadda suka tagayyara.

Su dai wadannan fursunoni sun shiga yajin kin cin abinci ne domin nuna rashin amincewarsu dangane da yadda ake tsare da su ba tare da an gurfanar da su a gaban alkali ba.

Gontanamu bay
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
2023: Ana Rantsar Da Ni Zan Fara Sauya Fasalin Nijeriya –  Atiku

2023: Ana Rantsar Da Ni Zan Fara Sauya Fasalin Nijeriya - Atiku

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.