• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Liverpool Za Ta Kai Labari Ba Tare Da Muhammad Salah Ba?

by Abba Ibrahim Wada
7 months ago
in Wasanni
0
Shin Liverpool Za Ta Kai Labari Ba Tare Da Muhammad Salah Ba?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da kungiya irin ta Real Madrid ke tunkaho da zaratan ‘yanwasan gaba hudu da suka hada da Kylian Mbappe da Jude Bellingham da Binicius Jr da kuma Rodrygo, wadanda ka iya dama lissafin duk wata kungiya da ta yi karo da ita, shin kungiya irin Liberpool ya za ta kasance idan yau ba ta tare da tauraron dan gabanta Mohamed Salah ba? Wanda shi ne jagoran kungiyar a yanzu.

Kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid ka iya dogaro da kowanne daga cikin zaratan nata hudu a ranar da take cikin bukata kuma ya fitar da ita kunya, kamar yadda Mbappe ya ci kwallo uku da ya sallami Manchester City (6-3 jimilla gida da waje) ya kuma kai kungiyarsa matakin kungiyoyi 16 na gasar Zakarun Turai a ranar Laraba a filin wasa na Estadio Santiago Bernabeu.

  • Kasar Philippines Za Ta Dandana Kudarta Game Da Gudummawar Soja Da Amurka Ta Ba Ta
  • Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Kara Haraji Kan Kayayyakinta 

Wannan tambaya da ake yi kan Liberpool idan ba ta tare da Salah ta kara bayyana bayan karawar kungiyar a gidan Aston Billa inda suka yi canjaras 2-2. Tauraron na Masar ne ya fara daga raga a karawar ta Laraba inda a minti na 29 ya ci wa Liberpool kwallo da taimakon Diogo Jota, kafin kuma Y. Tielemans ya farke a minti na 38 wannan kuwa duk da cewa ba ya kan ganiyarsa a wasan na ranar Laraba.

Sai kuma O. Watkins ya sa Aston Billa a gaba ana shirin tafiya hutun rabin lokaci da kwallo ta biyu, wadda kuma T. Aledander-Arnold ya farke wa Liberpool a minti na 61 da taimakon Salah. kwallon da Salah ya ci da kuma wadda ya bayar aka farke sun sa a yanzu yana da kwallo 39 da yake da hannu a ciki a wannan kakar a Premier a bana – inda ya ci kwallo 24 ya kuma taimaka aka zura guda 15.

Haka kuma da wadannan alkaluma Salah din ya zama danwasa na biyar da ya ci kwallo fiye da 15 ya kuma bayar da taimako aka ci 15 a Premier a bana, inda ya shiga rukunin su Eric Cantona, da Matt le Tissier, da Thierry Henry da kuma Eden Hazard, kuma shi har yanzu yana ci gaba da buga wasa wanda hakan yake nufin zai iya kafa sabon wani tarihin kafin karshen kakar wasa ta bana.

Labarai Masu Nasaba

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

Salah ya kasance danwasa na farko a gasar Premier da ya ci ya kuma bayar aka ci a wasanni daban-daban har goma a kaka daya. Sannan shi ne danwasa na farko da ya yi haka a daya daga cikin manyan gasar Turai biyar tun bayan Lionel Messi da ya yi wannan bajinta a kakar 2014-15, inda ya yi wa Barcelona hakan da kwallo 11.

Sai dai babban abin da yake gaban kungiyar kwallon kafa ta Liberpool ko kuma yake ci mata tuwo a kwarya shi ne kasancewar a karshen wannan kakar kwantiragin Muhammad Salah zai kare kuma har kawo yanzu bai sake sabon kwantiragin ba, tunda har yanzu ba su cimma wata yatrjejeniya ba wadda za ta saka ya ci gaba da zama a kungiyar ta Liberpool.

Mai koyuar da ‘yan wasan kungiyar, Arne Slot ya ce kwazon da Mohamed Salah ke yi a wasannin bana, zai kara yin tsada idan Liberpool za ta tsawaita kwantiraginsa kuma dan wasan na tawagar Masar zai cika shekara 33 da haihuwa cikin watan Yuni lokacin da yarjejeniyarsa za ta kare da kungiyar ta Liberpool wadda take buga wasanninta a katafaren filin wasa na Anfield.

To sai dai dan wasan, yana taka rawar gani a kakar nan fiye da bajintar da ya yi a kungiyar a kakar wasa ta 2017 domin shine ya karbi kyautar fitatcen dan wasa a karawar da Liberpool ta doke Manchester City 2-0 ranar Lahadi a Etihad a Premier League kuma hakan ne ya sa Liberpool ta ci gaba da zama ta daya a kan teburin Premier da tazarar maki 11 tsakani da Arsenal ta biyu da tazarar maki 20 tsakani da Manchester City ta hudu.

Muhammad Salah ya ci kwallo 30 a kakar nan 25 daga ciki a Premier League, na farko da yake da hannu a cin kwallo 40 ko fiye da haka a kaka biyu a babbar gasar ta Ingila. Haka kuma shi ne kan gaba mai hannu a cin kwallo 50 a dukkan karawa a bana tsakanin manyan gasar Turai biyar da suka hada da Premier ta Ingila da La liga da Seria A da Lig 1 na faransa da Bundes Liga ta Jamus.

Liberpool tana da wani tsari da take taka tsantsan kan tsawaita yarjejeniya da duk wani dan wasanta da ya kai shekara 30 da haihuwa kuma hakan ne yasa shima dan wasa Birgil Ban Dijk har yanzu kungiyar bata kara masa sabon kwantiragi ba tare da dan wasa Trend Aledandre Arnold dan Ingila, wanda tuni kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid ta shiga tattaunawa da shi domin ya koma kasar Spaniya da buga wasa.

Liberpool, wadda take jan ragamar teburin Premier League ta karbi bakunci kungiyar kwallon kafa ta Newcastle United a ranar Laraba a gasar Premier kuma daga nan za ta je ta buga wasa da kungiyar kwallon kafa ta Paris St Germain wasan zagaye na biyu a gasar cin kofin zakarun turai na Champions League ranar Laraba 5 ga watan Maris.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: LiverpoolSalah
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Kiyaye Girmama Kasashen Tsibirai Na Yankin Tekun Pasifik

Next Post

Shugabar Tanzaniya Ta Yaba Da Yadda Ake Ci Gaba Da Samun Karuwar Jigilar Kayayyaki A Tashar Tanga Da Sin Ta Inganta

Related

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack
Wasanni

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

2 days ago
Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 
Wasanni

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

4 days ago
Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein
Wasanni

Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein

5 days ago
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana
Wasanni

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

6 days ago
Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana
Wasanni

Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana

6 days ago
Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda
Wasanni

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

1 week ago
Next Post
Shugabar Tanzaniya Ta Yaba Da Yadda Ake Ci Gaba Da Samun Karuwar Jigilar Kayayyaki A Tashar Tanga Da Sin Ta Inganta

Shugabar Tanzaniya Ta Yaba Da Yadda Ake Ci Gaba Da Samun Karuwar Jigilar Kayayyaki A Tashar Tanga Da Sin Ta Inganta

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.