ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Liverpool Za Ta Kai Labari Ba Tare Da Muhammad Salah Ba?

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
Salah

Yayin da kungiya irin ta Real Madrid ke tunkaho da zaratan ‘yanwasan gaba hudu da suka hada da Kylian Mbappe da Jude Bellingham da Binicius Jr da kuma Rodrygo, wadanda ka iya dama lissafin duk wata kungiya da ta yi karo da ita, shin kungiya irin Liberpool ya za ta kasance idan yau ba ta tare da tauraron dan gabanta Mohamed Salah ba? Wanda shi ne jagoran kungiyar a yanzu.

Kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid ka iya dogaro da kowanne daga cikin zaratan nata hudu a ranar da take cikin bukata kuma ya fitar da ita kunya, kamar yadda Mbappe ya ci kwallo uku da ya sallami Manchester City (6-3 jimilla gida da waje) ya kuma kai kungiyarsa matakin kungiyoyi 16 na gasar Zakarun Turai a ranar Laraba a filin wasa na Estadio Santiago Bernabeu.

  • Kasar Philippines Za Ta Dandana Kudarta Game Da Gudummawar Soja Da Amurka Ta Ba Ta
  • Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Kara Haraji Kan Kayayyakinta 

Wannan tambaya da ake yi kan Liberpool idan ba ta tare da Salah ta kara bayyana bayan karawar kungiyar a gidan Aston Billa inda suka yi canjaras 2-2. Tauraron na Masar ne ya fara daga raga a karawar ta Laraba inda a minti na 29 ya ci wa Liberpool kwallo da taimakon Diogo Jota, kafin kuma Y. Tielemans ya farke a minti na 38 wannan kuwa duk da cewa ba ya kan ganiyarsa a wasan na ranar Laraba.

ADVERTISEMENT

Sai kuma O. Watkins ya sa Aston Billa a gaba ana shirin tafiya hutun rabin lokaci da kwallo ta biyu, wadda kuma T. Aledander-Arnold ya farke wa Liberpool a minti na 61 da taimakon Salah. kwallon da Salah ya ci da kuma wadda ya bayar aka farke sun sa a yanzu yana da kwallo 39 da yake da hannu a ciki a wannan kakar a Premier a bana – inda ya ci kwallo 24 ya kuma taimaka aka zura guda 15.

Haka kuma da wadannan alkaluma Salah din ya zama danwasa na biyar da ya ci kwallo fiye da 15 ya kuma bayar da taimako aka ci 15 a Premier a bana, inda ya shiga rukunin su Eric Cantona, da Matt le Tissier, da Thierry Henry da kuma Eden Hazard, kuma shi har yanzu yana ci gaba da buga wasa wanda hakan yake nufin zai iya kafa sabon wani tarihin kafin karshen kakar wasa ta bana.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

Salah ya kasance danwasa na farko a gasar Premier da ya ci ya kuma bayar aka ci a wasanni daban-daban har goma a kaka daya. Sannan shi ne danwasa na farko da ya yi haka a daya daga cikin manyan gasar Turai biyar tun bayan Lionel Messi da ya yi wannan bajinta a kakar 2014-15, inda ya yi wa Barcelona hakan da kwallo 11.

Sai dai babban abin da yake gaban kungiyar kwallon kafa ta Liberpool ko kuma yake ci mata tuwo a kwarya shi ne kasancewar a karshen wannan kakar kwantiragin Muhammad Salah zai kare kuma har kawo yanzu bai sake sabon kwantiragin ba, tunda har yanzu ba su cimma wata yatrjejeniya ba wadda za ta saka ya ci gaba da zama a kungiyar ta Liberpool.

Mai koyuar da ‘yan wasan kungiyar, Arne Slot ya ce kwazon da Mohamed Salah ke yi a wasannin bana, zai kara yin tsada idan Liberpool za ta tsawaita kwantiraginsa kuma dan wasan na tawagar Masar zai cika shekara 33 da haihuwa cikin watan Yuni lokacin da yarjejeniyarsa za ta kare da kungiyar ta Liberpool wadda take buga wasanninta a katafaren filin wasa na Anfield.

To sai dai dan wasan, yana taka rawar gani a kakar nan fiye da bajintar da ya yi a kungiyar a kakar wasa ta 2017 domin shine ya karbi kyautar fitatcen dan wasa a karawar da Liberpool ta doke Manchester City 2-0 ranar Lahadi a Etihad a Premier League kuma hakan ne ya sa Liberpool ta ci gaba da zama ta daya a kan teburin Premier da tazarar maki 11 tsakani da Arsenal ta biyu da tazarar maki 20 tsakani da Manchester City ta hudu.

Muhammad Salah ya ci kwallo 30 a kakar nan 25 daga ciki a Premier League, na farko da yake da hannu a cin kwallo 40 ko fiye da haka a kaka biyu a babbar gasar ta Ingila. Haka kuma shi ne kan gaba mai hannu a cin kwallo 50 a dukkan karawa a bana tsakanin manyan gasar Turai biyar da suka hada da Premier ta Ingila da La liga da Seria A da Lig 1 na faransa da Bundes Liga ta Jamus.

Liberpool tana da wani tsari da take taka tsantsan kan tsawaita yarjejeniya da duk wani dan wasanta da ya kai shekara 30 da haihuwa kuma hakan ne yasa shima dan wasa Birgil Ban Dijk har yanzu kungiyar bata kara masa sabon kwantiragi ba tare da dan wasa Trend Aledandre Arnold dan Ingila, wanda tuni kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid ta shiga tattaunawa da shi domin ya koma kasar Spaniya da buga wasa.

Liberpool, wadda take jan ragamar teburin Premier League ta karbi bakunci kungiyar kwallon kafa ta Newcastle United a ranar Laraba a gasar Premier kuma daga nan za ta je ta buga wasa da kungiyar kwallon kafa ta Paris St Germain wasan zagaye na biyu a gasar cin kofin zakarun turai na Champions League ranar Laraba 5 ga watan Maris.

Salah
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
  • Abba Ibrahim Wada
    FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
  • Abba Ibrahim Wada
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
Wasanni

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
Wasanni

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

June 22, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
Wasanni

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
Next Post
Shugabar Tanzaniya Ta Yaba Da Yadda Ake Ci Gaba Da Samun Karuwar Jigilar Kayayyaki A Tashar Tanga Da Sin Ta Inganta

Shugabar Tanzaniya Ta Yaba Da Yadda Ake Ci Gaba Da Samun Karuwar Jigilar Kayayyaki A Tashar Tanga Da Sin Ta Inganta

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.