ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Wane Ne Ya Danawa Kasashen Afrika “Tarkon Bashi”?

by CMG Hausa
3 years ago
Afrika

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Jaridar The Guardian ta Birtaniya, ya fitar da wani rahoto a baya-bayan nan, da ya yi kira ga cibiyoyin bayar da bashi na yammacin duniya, su saukaka tsarin biyan basussukan da suke bin kasashe masu karancin kudin shiga, musamman kasashen Afrika. 

Wannan rahoton na zuwa ne bayan cibiyar Debt Justice ta Birtaniyar, mai bibiyar yadda ake bayar da bashi tsakanin kasashen duniya, ta bankado wasu alkaluma dake nuna cewa, basussukan da cibiyoyin kudi na yammacin duniya ke bin kasashen Afrika, ya rubanya wanda kasar Sin ke binsu har sau 3, haka kuma kudin ruwansu ya ninka na Sin sau biyu.

  • Daya Daga Fasinjojin Jirgin Kasan Kaduna Zuwa Abuja: Dalilin Sakin Faifan Bidiyon Azabtar Da Mu – Barista Hassan

Tambayar a nan ita ce, shin wane ne ya danawa kasashen Afrika Tarkon Bashi?
Batun “Tarkon Bashi” wani abu ne da kasashen yamma suka kirkiro, bisa zargi mara tushe da suke wa kasar Sin da kakabawa kasashen Afrika bashi fiye da kima. Sai dai, sun tsallake tarin basussuka da kudin ruwa da cibiyoyin kudi na kasashensu suka laftawa kasashen na Afrika.
Karya fure take ba ta ’ya’ya. Yanzu ga gaskiya ta fito, amma kasashen masu neman haifar da kiyayya tsakanin Sin da aminanta na Afrika, kawai saboda kishin karbuwar da ta samu, sun yi gum.
Duk wanda ya je kasashen na Afrika, zai ga yadda kasar Sin ta taimaka wajen gaggauta samar da kayayyaki na ci gaban da kyautatuwar rayuwa, daga kayayyakin more rayuwa, zuwa zuba jari da samar da aikin yi da tallafin karatu da na lafiya da bunkasa cinikayya da kafa kamfanoni, har ma da dakarun wanzar da zaman lafiya da sauransu. Hakika in ma bashi ne, an gani a aikace, domin duk wani katafaren aikin ci gaba a kasashen, za a ga cewa mafiya yawansu, Sin ce ta aiwatar. Duk da dimbin bashi da kasashen yamma suke bin kasashen, ba a ga wani abun a zo a gani da suka tabuka ba.
Bayan barkewar annobar COVID-19, kasar Sin ta amsa kiran kungiyar G20 na saukaka lokacin biyan bashi ga kasashe masu karancin kudin shiga, inda kawo yanzu ta sassauta biyan sama da dala biliyan 1.3, wanda ya dauki kaso 30 na jimilar shirin. Wannan ya sa kasar Sin ta zama kan gaba wajen aiwatar da shirin. A don haka ne ma, cibiyar Debt Justice ta yi kira ga kasashen yamma su tilastawa cibiyoyinsu na kudi aiwatar da shirin kamar dai yadda Sin ta yi.
Ina laifin mai taimakawa da kasancewa da kai a kowanne yanayi? Kasar Sin ta kasance mai amsa kiran kasashen Afrika a ko da yaushe, mai nuna kulawa a gare su, mai kare muradunsu a dandalin kasa da kasa, mai kai musu dauki cikin gaggawa, haka kuma mai jansu a jiki da yayata gogewarta gare su. Wadannan kadan ne daga cikin dalilan da ya sa kasashen ke kara aminta da ita. Kamar yadda shugaban Nijeriya ya taba furtawa da aka masa tambaya game da bashin kasar Sin, kofarsa a bude take ga duk wanda ke son taimakawa kasarsa, kuma kasar Sin ta kasancewa mai taimaka mata cikin sauki ba tare da sharadi ko katsalandan ba. Kuma shakka babu, irin hakan ne ke kasancewa a wajen dukkan kasashen nahiyar. (Fa’iza Mustapha)

ADVERTISEMENT
ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 
Daga Birnin Sin

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

November 17, 2025
Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

November 17, 2025
Next Post
Sojoji 2 Da Farar Hula 1 Sun Mutum A Wani Hatsarin Mota A Legas

Sojoji 2 Da Farar Hula 1 Sun Mutum A Wani Hatsarin Mota A Legas

LABARAI MASU NASABA

Bukatar Samar Da Cikkakken Tsaro Ga Hukumar Zabe

’Yansanda Sun Tura Tawaga Don Ceto Ɗaliban Da Aka Sace A Kebbi

November 18, 2025
Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

November 17, 2025
Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

November 17, 2025
An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

November 17, 2025
NBS

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

November 17, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

November 17, 2025
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

November 17, 2025
Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.