• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Wane Ne Ya Danawa Kasashen Afrika “Tarkon Bashi”?

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shin Wane Ne Ya Danawa Kasashen Afrika “Tarkon Bashi”?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Jaridar The Guardian ta Birtaniya, ya fitar da wani rahoto a baya-bayan nan, da ya yi kira ga cibiyoyin bayar da bashi na yammacin duniya, su saukaka tsarin biyan basussukan da suke bin kasashe masu karancin kudin shiga, musamman kasashen Afrika. 

Wannan rahoton na zuwa ne bayan cibiyar Debt Justice ta Birtaniyar, mai bibiyar yadda ake bayar da bashi tsakanin kasashen duniya, ta bankado wasu alkaluma dake nuna cewa, basussukan da cibiyoyin kudi na yammacin duniya ke bin kasashen Afrika, ya rubanya wanda kasar Sin ke binsu har sau 3, haka kuma kudin ruwansu ya ninka na Sin sau biyu.

  • Daya Daga Fasinjojin Jirgin Kasan Kaduna Zuwa Abuja: Dalilin Sakin Faifan Bidiyon Azabtar Da Mu – Barista Hassan

Tambayar a nan ita ce, shin wane ne ya danawa kasashen Afrika Tarkon Bashi?
Batun “Tarkon Bashi” wani abu ne da kasashen yamma suka kirkiro, bisa zargi mara tushe da suke wa kasar Sin da kakabawa kasashen Afrika bashi fiye da kima. Sai dai, sun tsallake tarin basussuka da kudin ruwa da cibiyoyin kudi na kasashensu suka laftawa kasashen na Afrika.
Karya fure take ba ta ’ya’ya. Yanzu ga gaskiya ta fito, amma kasashen masu neman haifar da kiyayya tsakanin Sin da aminanta na Afrika, kawai saboda kishin karbuwar da ta samu, sun yi gum.
Duk wanda ya je kasashen na Afrika, zai ga yadda kasar Sin ta taimaka wajen gaggauta samar da kayayyaki na ci gaban da kyautatuwar rayuwa, daga kayayyakin more rayuwa, zuwa zuba jari da samar da aikin yi da tallafin karatu da na lafiya da bunkasa cinikayya da kafa kamfanoni, har ma da dakarun wanzar da zaman lafiya da sauransu. Hakika in ma bashi ne, an gani a aikace, domin duk wani katafaren aikin ci gaba a kasashen, za a ga cewa mafiya yawansu, Sin ce ta aiwatar. Duk da dimbin bashi da kasashen yamma suke bin kasashen, ba a ga wani abun a zo a gani da suka tabuka ba.
Bayan barkewar annobar COVID-19, kasar Sin ta amsa kiran kungiyar G20 na saukaka lokacin biyan bashi ga kasashe masu karancin kudin shiga, inda kawo yanzu ta sassauta biyan sama da dala biliyan 1.3, wanda ya dauki kaso 30 na jimilar shirin. Wannan ya sa kasar Sin ta zama kan gaba wajen aiwatar da shirin. A don haka ne ma, cibiyar Debt Justice ta yi kira ga kasashen yamma su tilastawa cibiyoyinsu na kudi aiwatar da shirin kamar dai yadda Sin ta yi.
Ina laifin mai taimakawa da kasancewa da kai a kowanne yanayi? Kasar Sin ta kasance mai amsa kiran kasashen Afrika a ko da yaushe, mai nuna kulawa a gare su, mai kare muradunsu a dandalin kasa da kasa, mai kai musu dauki cikin gaggawa, haka kuma mai jansu a jiki da yayata gogewarta gare su. Wadannan kadan ne daga cikin dalilan da ya sa kasashen ke kara aminta da ita. Kamar yadda shugaban Nijeriya ya taba furtawa da aka masa tambaya game da bashin kasar Sin, kofarsa a bude take ga duk wanda ke son taimakawa kasarsa, kuma kasar Sin ta kasancewa mai taimaka mata cikin sauki ba tare da sharadi ko katsalandan ba. Kuma shakka babu, irin hakan ne ke kasancewa a wajen dukkan kasashen nahiyar. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Sace Mutun 6, Sun Bukaci Miliyan 50 Matsayin Kudin Fansa A Katsina

Next Post

Sojoji 2 Da Farar Hula 1 Sun Mutum A Wani Hatsarin Mota A Legas

Related

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

13 hours ago
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

14 hours ago
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko
Daga Birnin Sin

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

15 hours ago
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba
Daga Birnin Sin

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

16 hours ago
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai
Daga Birnin Sin

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

17 hours ago
An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya
Daga Birnin Sin

An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

18 hours ago
Next Post
Sojoji 2 Da Farar Hula 1 Sun Mutum A Wani Hatsarin Mota A Legas

Sojoji 2 Da Farar Hula 1 Sun Mutum A Wani Hatsarin Mota A Legas

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

June 28, 2025
Hoton Tallan Taliyar Indomie

Indomie Ta Kaddamar Da Shirin Gangamin Abinci Mai Gina Jiki Na ‘Ingantaccen Abinci Domin Nasara’

June 28, 2025
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.