• English
  • Business News
Friday, October 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanaki biyu da suka gabata, kafofin yada labaran Najeriya da dama sun buga bayanin da wani shahararren dan siyasa mai suna Dakuku Peterside ya rubuta, mai taken “Mene ne Najeriya za ta iya koya daga ci gaban kasar Sin a fannin samar da wutar lantarki?” Kasidar ta yi nuni da cewa, a shekarar 2000, ma’aunin samar da wutar lantarki na kasar Sin ya kai fiye da tiriliyan 1.3 KWH, kusan kashi daya bisa uku na lantarki da kasar Amurka ta samar. Sai dai ya zuwa shekarar 2024, karfin samar da wutar lantarki na kasar Sin ya zarce KWH tiriliyan 10, kusan ninki biyun na Amurka, kuma a daga cikin lantarkin, wanda aka samu daga makamashi mai tsabta ya kai kimanin kaso 55%. To, ko ta yaya kasar Sin ta cimma nasarar hakan? Dalilin da mista Peterside ya bayar ya shafi manufar musamman ta kasar Sin, ta tsara shirin raya kasa duk shekaru biyar-biyar, wanda ke da matsayi na wajibi tamkar doka. Ya ce, ci gaban da kasar Sin ta samu ya tabbatar da cewa, duk wata kasa za ta iya samun babban ci gaba ta hanyar tsayawa tsayin daka kan aiwatar da wasu nagartattun manufofi.

Tsokacin da Mista Peterside ya yi daidai ne. Saboda yin amfani da tsare-tsare na matsakaita, da na dogon lokaci wajen jagorantar aikin raya tattalin arziki da zamantakewar al’umma, hanya ce mai muhimmanci ga jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin wajen gudanar da mulki a kasar. Tun daga shekarun 1950, kasar Sin ta fara tsarawa da aiwatar da shirye-shiryen raya kasa na shekaru biyar biyar, kuma yanzu muna cikin wa’adin shirin raya kasa na shekaru 5 na 14, wanda kasar Sin ta tsara. Hakika “Shirin shekaru biyar” na farko zuwa na biyar sun baiwa kasar Sin damar kafa wani cikakken tsarin masana’antu da na tattalin arziki. Kana “Shirin shekaru biyar” na shida zuwa na tara, sun ba jama’ar kasar Sin damar samun kyakkyawan yanayin rayuwa gaba daya. Ban da haka, a cikin wa’adin ” shirin shekaru biyar” na goma zuwa na goma sha biyu, jimillar tattalin arzikin kasar Sin ya daga zuwa matsayi na biyu a duniya. Sa’an nan, a cikin shekaru kusan 10 da suka wuce, wato a cikin wa’adin “shirin shekaru 5” na 13 da na 14, kasar Sin ta gina al’umma mai ingancin rayuwa, kuma karfin tattalin arzikinta, da na kimiyya da fasaha, sun kai wani sabon matsayi. Bisa alkaluman da kasar Sin ta fitar, an ce, a yayin “shirin shekaru biyar” na 14 da za a kawo karshensa a bana, ana sa ran karuwar tattalin arzikin kasar Sin za ta zarce dalar Amurka triliyan 4.9, adadin da ya zarta jimillar tattalin arzikin kasar da ke matsayi na uku a duniya a fannin karfin tattalin arziki.

  • Sauye-sauyen Tinubu Suna Taimaka Wa Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya — Minista
  • EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi

Me ya sa “Shirin shekaru biyar” na kasar Sin ya iya haifar da irin wadannan dimbin alfanu? Dalili shi ne wasu halayen musamman na shirin. Bisa tsokacin da mista Li Zhongjie, masanin ilimin tarihin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ya yi, “shirin shekaru biyar” na kasar Sin ya hada da halayen musamman na bin doka, da sanya moriyar jama’a a gaban komai, da daukar mataki bisa ainihin yanayin da ake ciki, da kokarin tabbatar da aiwatarwar manufofi.

A cikin wadannan halayen musamman, “sanya moriyar jama’a a gaban komai” na nufin: Na farko, yayin da ake tsara “Shirin shekaru 5”, dole ne a gudanar da bincike a tsanake a wurare daban-daban, da kuma sauraron ra’ayoyi daga kowane bangare. Misali, lokacin da aka tsara shirin “Shirin shekaru biyar” karo na 14, wasu shekaru biyar da suka gabata, baya ga gudanar da binciken, an kuma aiwatar da aikin neman ra’ayin jama’a kan layi, wato ta shafin yanar gizo na Intanet, a watan Agustan 2020, an kuma samu sama da shawarwari miliyan 1.018 daga masu amfani da yanar gizo. Na biyu, burin da ake neman cimmawa ta hanyar tsara “Shirin shekaru biyar” shi ne tabbatar da ci gaban tattalin arziki, da kokarin biyan bukatun al’umma na fannoni daban daban. Saboda haka, duk wani “shirin shekaru 5” na kunshe da dimbin manufofin inganta rayuwar jama’a. Ma iya cewa, ana inganta zaman rayuwar jama’ar kasar Sin ne, ta hanyar aiwatar da “shirye-shiryen shekaru biyar” daya bayan daya.

Sa’an nan, “bin doka” yana nufin, yayin da aka tsara “shirin na shekaru biyar”, dole ne a bar dukkan jam’iyyun siyasa su yi tattaunawa mai zurfi a kansa, kana majalisar gudanarwar kasar Sin ta kula da aikin tsara shirin, kafin daga bisani majalissun dokokin kasar Sin su tantance shirin da kada kuri’a don zartar da shi, inda ake aiwatar da dukkan ayyukan bisa tsarin dimokuradiyya da kuma doka. Bugu da kari, kowace shekara, majalisar wakilan jama’ar kasar Sin ta kan yi bitar ci gaba da aka samu, a kokarin aiwatar da “shirin na shekaru biyar” da aka tsara.

Labarai Masu Nasaba

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka

Ban da haka, bayan da aka tsara “shirin shekaru 5”, yana da muhimmanci a aiwatar da shi. A kasar Sin, bayan da aka gabatar da wani “shiri na shekaru 5”, dole ne a aiwatar da shi yadda ake bukata. Kwamitin tsakiya na jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, da majalisar gudanarwar kasar za su tsara salon aiwatar da dukkan ayyuka, da raba su ga sassa da yankuna daban-daban, don a aiwatar da su a matakai daban daban. Bayan haka, hukumomi daban daban su kan gudanar da ayyukan sa ido a tsakiyar wa’adin shirin, kuma za a tantance ainihin sakamakon da aka samu bayan karewar shirin.

Ta wadannan halayen musamman, za a iya ganin abubuwan da za su tabbatar da aiwatar da shirin na raya kasa: Na farko, kokarin kare muhimman muradun jama’a, da tabbatar da yanke shawara ta wata hanya mai dacewa, kuma bisa tsarin dimokuradiyya. Na biyu, yin amfani da tsare-tsaren shari’a wajen tabbatar da ingancin shirin da aka tsara, da mai da shi karkashin sa ido da aka yi masa. Na uku, tun daga gwamnatin tsakiya zuwa kananan hukumomi, dole ne a aiwatar da shirin raya kasa a tsanake, domin tabbatar da cimma burin da aka sanya a gaba. A cikin wadannan abubuwa, ana iya ganin ruhin dimokuradiyya da bin doka da oda, da kuma yanayin aiki na mai da hankali, da nuna sanin ya kamata, wadanda suka kasance tushen ci gaban kasar Sin.

A cewar mista Peterside, ta hanyar koyi da fasahohin kasar Sin, Najeriya za ta iya cin gajiyar dimbin albarkatun kasa da take da su, don tabbatar da cikar burinta na raya tattalin arziki. Ni ma na yi imanin cewa, Najeriya za ta iya yin hakan, tare da samun biyan bukata. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi

Next Post

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

Related

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang
Ra'ayi Riga

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

3 days ago
Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka

4 days ago
Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang
Ra'ayi Riga

Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang

6 days ago
Labaran Xinjiang a Zane: Yadda Hamada Ta Zama Gonaki
Ra'ayi Riga

Labaran Xinjiang a Zane: Yadda Hamada Ta Zama Gonaki

1 week ago
Komai Nisan Dare Gari Zai Waye
Ra'ayi Riga

Komai Nisan Dare Gari Zai Waye

2 weeks ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

2 weeks ago
Next Post
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Taya Grand Duke Guillaume Na Luxembourg Murnar Hawa Karagar Mulki

Xi Ya Taya Grand Duke Guillaume Na Luxembourg Murnar Hawa Karagar Mulki

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Sabbin Gonakin Da Za A Magance Zaizayewar Kasa A Sin A Karshen Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Na 14 Sun Kai Muraba’in Kilomita 340,000

Sabbin Gonakin Da Za A Magance Zaizayewar Kasa A Sin A Karshen Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Na 14 Sun Kai Muraba’in Kilomita 340,000

October 3, 2025
Jami’in MDD: Kayataccen Hutun “Golden Week Plus” Na Kasar Sin Ya Nuna Tasirin Yawon Bude Ido A Duniya 

Jami’in MDD: Kayataccen Hutun “Golden Week Plus” Na Kasar Sin Ya Nuna Tasirin Yawon Bude Ido A Duniya 

October 3, 2025
Lamine Yamal Zai Shafe Mako 3 Yana Jinya

Lamine Yamal Zai Shafe Mako 3 Yana Jinya

October 3, 2025
Xi Da Takwaransa Na Singapore Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 35 Da Kulla Huldar Diflomasiyya

Xi Da Takwaransa Na Singapore Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 35 Da Kulla Huldar Diflomasiyya

October 3, 2025
Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin

Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin

October 3, 2025
Yadda Na Ji Bayan Faduwa Zaben 2015 – Jonathan 

Ko Jonathan Zai Iya Ja Da Tinubu A 2027?

October 3, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

October 3, 2025
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

October 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.