• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Tsige Fubara: Gwamnonin PDP Za Su Gana Da Wike A Abuja

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnonin jam’iyyar PDP za su gana da ministan babban birnin tarayya, Abuja, Nyesom Wike, kan halin da ake ciki a Jihar Ribas, yayin da ake neman tsige gwamnan Jihar, Siminalayi Fubara.

Darakta Janar na kungiyar gwamnonin PDP, CID Maduabum, ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar bayan taron kungiyar a ranar Talata.

  • Malaman Makaranta 1,700 Sun Koka Kan Rashin Biyan Su Albashin Shekaru 3 
  • CBN Ya Rufe Wasu Bankuna 754 Sakamakon Shiga Matsaloli

Gwamnonin za su gana da ministan a yau Laraba a ofishinsa.

Shugaban kungiyar, Gwamna Bala Mohammed na jihar Bauchi, ne zai jagoranci wasu gwamnoni kusan 10 na jam’iyyar PDP zuwa ofishin ministan babban birnin tarayya Abuja domin tattaunawa.

“Bayan shawarar da aka cimma a taron kungiyar gwamnonin PDP a ranar Talata, 31 ga watan Oktoba, za mu ziyarci Ministan babban birnin tarayya Abuja, domin sasanci,” in ji sanarwar.

Labarai Masu Nasaba

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

Kungiyar ta yi taro ne a ranar Talata inda ta bukaci ‘yan siyasa a Kudu-maso-Kudu da su yi wani abu don warware rikicin cikin ruwan sanyi.

Wadanda suka halarci taron sun hada da: Gwamna Bala Mohammed (Bauchi), Gwamna Ahmadu Fintiri (Adamawa), Gwamna Sheriff Oborevwori (Delta), Gwamna Ademola Adeleke (Osun), Gwamna Seyi Makinde (Oyo), Gwamna Caleb Mutfwang (Filato), Gwamna Godwin Obaseki. (Edo), Gwamna Kefas Agbu (Taraba), Gwamna Dauda Lawal (Zamfara), Gwamna Siminalayi Fubara (Ribas) da Mataimakin Gwamna Ifeanyi Ossai (Enugu).

A wajen taron, gwamnonin PDP sun yi maraba da shiga tsakani da shugaba Bola Tinubu ya yi ta hanyar ganawa da Fubara da Wike a fadar Aso Villa da ke Abuja da yammacin ranar Talata domin warware rikicin.

Ganawar da shugaban kasar ya yi da ‘yan siyasar biyu na PDP ya biyo bayan yunkurin tsige Fubara da majalisar dokokin jihar Ribas ta yi a ranar Litinin.

Majalisar dokokin jihar ta zargi gwamnan da aikata munanan ayyukan da ba su dace ba a matsayinsa na gwamna.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FubaraGwamnonin PDPSulhuWike
ShareTweetSendShare
Previous Post

Malaman Makaranta 1,700 Sun Koka Kan Rashin Biyan Su Albashin Shekaru 3 

Next Post

Yanzu-yanzu: ‘Yansanda Sun Cafke Shugaban NLC, Joe Ajaero A Imo

Related

Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

7 hours ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

14 hours ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

17 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

18 hours ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

1 day ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

1 day ago
Next Post
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

Yanzu-yanzu: 'Yansanda Sun Cafke Shugaban NLC, Joe Ajaero A Imo

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.