• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Kasar Tunisiya Ya Gana Da Wang Yi

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shugaban Kasar Tunisiya Ya Gana Da Wang Yi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jiya Litinin, shugaban kasar Tunisiya Kais Saied ya gana da mamban ofishin siyasa na kwamitin tsakiyar Jam’iyyar Kwaminis ta Kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar Wang Yi a birnin Tunis, fadar mulkin kasar Tunisiya.

Da farko, Kais Saied ya bukaci Wang Yi da ya mika sakon gaisuwarsa ga shugaba Xi Jinping, yana mai cewa, ya amince da ra’ayoyin da shugaba Xi ya gabatar game da tafiyar da harkokin kasa, ya kuma yaba wa kasar Sin dangane da babbar nasarar da ta cimma a fannin zamanintar da kasar, haka kuma, ya yaba matuka kan sakamakon da aka cimma cikin shekaru 60 da suka gabata, bisa hadin gwiwa da bunkasuwar dangantaka a tsakanin kasashen biyu. Ya ce, ko da yake, akwai nisa a tsakanin kasar Sin da kasar Tunisiya, amma jama’ar kasashen biyu suna da zumunci mai zurfi a tsakaninsu, kuma kasarsa tana godiya ga kasar Sin bisa goyon bayan da ta dade tana nuna mata, lamarin da ya taimaka wajen raya kasar da kyautata zaman rayuwar al’umma. Ya ce a nan gaba kuma, kasar Tunisiya za ta ci gaba da goyon bayan shawarar “Ziri daya da hanya daya”, da koyon fasahohin kasar Sin wajen zamanintar da kasar Tunisiya bisa yanayin da take ciki. Haka kuma, kasar Tunisiya tana tsayawa tsayin daka wajen martaba manufar “kasar Sin kasa daya tak”, da kuma kudurin MDD mai lamba 2758, domin goyon bayan kasar Sin wajen kula da harkokin kasarta.

  • Kasar Sin Tana Da Cikakken Karfin Harhada Da Kera Jiragen Ruwa
  • Sin Ta Riga Ta Bayar Da Gudunmawar Da Ake Bukata Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

A nasa bangare, Wang Yi ya mika sakon gaisuwar shugaban kasar Sin Xi Jinping ga shugaba Saied, ya ce, tun bayan kulla huldar diflomasiyya a tsakanin kasar Sin da kasar Tunisiya shekaru 60 da suka gabata, dangantakar dake tsakanin kasashen biyu ta bunkasa yadda ya kamata. Kuma, abu mafi muhimmanci shi ne, bangarori biyu suna girmama juna, da nunawa juna adalci, da karfafa fahimtar juna a tsakaninsu, da kuma habaka hadin gwiwarsu, domin cimma moriyar juna. Kwanan baya, shugabannin kasashen biyu sun zanta ta wayar tarho, inda suka kara daidaita hanyar raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu. Kasar Sin tana godiya ga kasar Tunisiya, domin irin goyon bayan da ta nuna wa kasar Sin kan manyan batutuwan dake shafar ‘yancin kan kasar Sin, a sa’i daya kuma, kasar Sin tana goyon bayan kasar Tunisiya, wajen kare mulkin kai da ‘yancin kanta, da kuma kiyaye mutuncin al’ummar kasarta, kana, kasar Sin tana goyon bayan kasar Tunisiya wajen neman hanyar bunkasuwa bisa halin da take ciki, da aiwatar da gyare-gyaren raya kasa cikin ‘yanci.

Bugu da kari, shugaba Saied da minista Wang Yi, sun yi musayar ra’ayoyi kan rikicin Isra’ila da Falesdinu.

A wannan rana, Wang Yi ya kuma gana da takwaransa na kasar Tunisiya Nabil Ammar a birnin Tunisiya.

Labarai Masu Nasaba

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Wang Yi ya ce, kasar Sin a shirye take ta yi mu’amala da kasar Tunisiya wajen inganta fasahohin gudanawar harkokin kasa, kuma tana goyon bayan kasar Tunisiya wajen kara karfinta na neman bunkasuwa cikin ‘yancin kai, domin samun ci gaba da wadata cikin hadin gwiwa.

A nasa bangare kuma, minista Ammar ya ce, kasarsa tana mai da matukar hankali wajen zurfafa zumuncin dake tsakanin kasashen biyu, kuma, tana godiya ga kasar Sin dangane da taimako da goyon bayan da ta nuna mata. Kasar Tunisiya tana fatan yin hadin gwiwa da kasar Sin wajen inganta dangantakar dake tsakanin kasashen biyu zuwa wani sabon matsayi. (Mai Fassarawa: Maryam Yang)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfirkaAlakar Sin da AfirkaKasar SinMinistan harkokin wajen sin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Wajen Taron Dandalin Tattauna Tattalin Arzikin Duniya

Next Post

Yanzu-yanzu: Wani Abu Ya Fashe A Tashar Iskar Gas A Ibadan

Related

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana
Daga Birnin Sin

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

18 hours ago
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

18 hours ago
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping
Daga Birnin Sin

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

19 hours ago
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

20 hours ago
Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

21 hours ago
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

22 hours ago
Next Post
Yanzu-yanzu: Wani Abu Ya Fashe A Tashar Iskar Gas A Ibadan

Yanzu-yanzu: Wani Abu Ya Fashe A Tashar Iskar Gas A Ibadan

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

September 6, 2025
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

September 6, 2025
Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

September 6, 2025
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

September 6, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

September 6, 2025
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

September 6, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

September 6, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

September 6, 2025
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.