Muhammad Maitela">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Shugaban Majalisar Dattijai Ya Taya Shugaba Buhari Murnar Cika Shekara 78 A Duniya

by Muhammad Maitela
December 20, 2020
in LABARAI
2 min read
Shugaban Majalisar Dattijai
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Shugaban majalisar dattawan Nijeriya, Sanata Ahmad Ibrahim Lawan ya taya shugaban kasa, Muhammadu Buhari murnar zagayowar cikar sa shekaru 78 da haihuwa, wanda ya yi daidai da ranar Alhamis da ta gabata.

Sanata Lawan, ya bayyana hakan a takardar sanarwar manema labarai wadda ofishin sa ta fitar kana kuma wadda ya rattaba wa hannu a ranar Laraba inda ya bayyana ranar a matsayin mai muhimmanci ga yan Nijeriya baki daya.

samndaads

”Ina mai farincikin haduwa da yan uwa da iyala, abokai, jami’an gwamnati, na huldar yau da kullum da shugaban kasa wajen taya shi murnar wannan muhimiyyar rana wadda yake bikin tunawa da cikar sa a wannan matsayi na shekaru a cikin koshin lafiya da karsashi.”

”A duk shekarun da shugaba Buhari ya yi, bai gushe ba ya na gudanar da shugabancin kasar nan cike da nuna cikakkiyar jajircewar sa wajen ganin ya samar da hadin kai, zaman lafiya da ci gaban Nijeriya tare da samarwa yan kasa walwala.” In ji shi.

”Saboda haka ina kira ga dukkan yan kasa su fadada tunanin su da hangen nesa, kana su ci gaba da tsayawa kafaza da kafada tare da bayar da cikakken goyon baya ga manufofin gwamnatin shugaban kasa a wannan aiki da yake yi wajen sanya kshin kasa a zukatan yan Nijeriya.”

”Kuma a matsayi na na dan jama’iyar APC, ina mai farin ciki da yadda shugaba Buhari ya damra aniyar gyare-gyare da sake gina wannan kasaitarciyar jama’iyar tamu don ganin ta cimma burinta na shugabantar Nijeriya a cikin kyakkywan yanayi tare da ci gaban mulkin dimukuradiyyk da tattalin arziki.”

”Sannan a bangaren mu na yan majalisar dokoki na tarayya za mj ci gaba da aiki cikin tsanaki da kwanciyar hankali tsakanin mu da bangaren zartswa domin samun dawamamen zaman lafiya da ci gaban Nijeriya da al’ummarta baki daya.”

A karshe ya ce, a wannan rana mai muhimmanci ta zagoyowar ranar da aka haifi shugaban kasa Muhammadu Buhari, wanda a ciki ya ke addu’a ga Allah madaukakin sarki ya ci gaba da bai shugaba Buhari fasaha, karfin gwiwa da lafiya don samun ci gaba da jagorantar Nijeriya a matsayin da yan kasa ke muradi.

SendShareTweetShare
Previous Post

Buhari Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Faruk, Gwamnan Soja Na Farko A Arewaci Maso Yamma

Next Post

Dan Majalisar Wakilai Alhaji Muktar Dandutse Ya Horas Da Matasa Dabarun Noman Shinkafa Na Zamani A Mazabarsa

RelatedPosts

Misali Daga Kebbi: Yadda Kananan Hukumomi Suka Shiga Uku A Nijeriya

Misali Daga Kebbi: Yadda Kananan Hukumomi Suka Shiga Uku A Nijeriya

by Muhammad Maitela
2 hours ago
0

Kamar dai yadda aka sani kananan hukumomi sune suka kasance...

Abubuwan Da Suka Biyo Bayan Canja Shugabannin Tsaron Nijeriya

’Yan Yankin Arewa Maso Gabas Sun Bayyana Ra’ayoyinsu Kan Sauke Shugabannin Tsaro

by Muhammad Maitela
2 hours ago
0

Biyo bayan sauke shugabannin tsaron Nijeriya tare da nada sababbi...

Ya Kashe Mata Da Yaro Da Shebur

by Muhammad Maitela
2 hours ago
0

A yau aka kama wani mutum mai shekaru 28, Chukwuemeka...

Next Post
Alhaji Muktar Dandutse

Dan Majalisar Wakilai Alhaji Muktar Dandutse Ya Horas Da Matasa Dabarun Noman Shinkafa Na Zamani A Mazabarsa

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version