CRI Hausa">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home DAGA BIRNIN SIN

Shugaban Tanzania Ya Tattauna Da Mininstan Wajen Sin Game Da Hadin Gwiwar Kasashen Biyu

by CRI Hausa
January 9, 2021
in DAGA BIRNIN SIN
1 min read
Shugaban Tanzania Ya Tattauna Da Mininstan Wajen Sin Game Da Hadin Gwiwar Kasashen Biyu
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Shugaban Tanzania, John Magufuli, ya gana a jiya Juma’a, da mamban majalisar gudanarwar Sin, kuma ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, dake ziyara a Tanzania.

Shugaba John Magufuli, ya ce Sin ta samu gagarumar nasara ta fuskar ci gaban tattalin arziki kuma hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya a tsakanin kasashen biyu, ta kasance ta moriyar juna. Ya ce a shirye Tanzania take, ta zurfafa dangantakarta da Sin da fadada fitar da kayayyaki zuwa kasar da kara jan hankalin Sinawa masu zuba jari.
A nasa bangaren, Wang Yi, ya ce Tanzania ce kasa ta farko a nahiyar Afrika da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya ziyarta bayan ya hau karagar mulki a shekarar 2013. Kuma yayin ziyarar, shugaba Xi ya ce Sin za ta bi ka’idojin tsare gaskiya da samun sakamako a zahirance da tabbatar da aminci da kyakkyawar fata, yayin da take hulda da nahiyar.
A cewar Wang Yi, kasar Sin na goyon bayan kamfanoninta su zuba jari a Tanzania da fadada hadin gwiwar kasashen biyu a bangaren samar da ababen more rayuwa da albarkatu da makamashi da noma da kiwo da samar da kayayyaki da magunguna da kiwon lafiya da sauran bangarori.
Har ila yau a jiya, ministan na Sin ya tattauana da takwaransa na Tanzania, Palamagamba Kabudi, inda suka kira taron manema labarai na hadin gwiwa. (Mai fassarawa: Fa’iza Mustapha daga CRI Hausa)

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Mukadashin Jakadan Sin A Najeirya: Ziyarar Wang Yi A Najeriya Ta Haifar Da Gagarumin Sakamako

Next Post

Ziyarar Wang Yi A Afirka Za Ta Zurfafa Hulda Tsakanin Sin Da Afirka Bayan Ganin Bayan COVID-19

RelatedPosts

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Duba Marasa Lafiya Sama Da 4,000 A Ghana A 2020

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Duba Marasa Lafiya Sama Da 4,000 A Ghana A 2020

by CRI Hausa
4 hours ago
0

Tawagar jami’an lafiya ta kasar Sin kashi na 9 dake...

Amurka Ta Kasa Magance Matsalar Rashin Daidaito A Cikin Al’ummarta

Amurka Ta Kasa Magance Matsalar Rashin Daidaito A Cikin Al’ummarta

by CRI Hausa
4 hours ago
0

Sakamakon bazuwar cutar COVID-19, wadda ta raunana tattalin arzikin duniya...

Mike Pompeo Zai Kammala Aikinsa Na Ministan Harkokin Waje

Mike Pompeo Zai Kammala Aikinsa Na Ministan Harkokin Waje

by CRI Hausa
5 hours ago
0

A cikin kwanaki 10 da wani abu da suka gabata,...

Next Post
Ziyarar Wang Yi A Afirka Za Ta Zurfafa Hulda Tsakanin Sin Da Afirka Bayan Ganin Bayan COVID-19

Ziyarar Wang Yi A Afirka Za Ta Zurfafa Hulda Tsakanin Sin Da Afirka Bayan Ganin Bayan COVID-19

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version