• English
  • Business News
Wednesday, September 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabancin Majalisa: Na Fi Kowa Cancanta, Ni Kadai Na Kawo Kudiri 78, Guda 21 Shugaban Kasa Ya Sa Wa Hannu – Hon Abbas Tajudeen

by Bashir Bello, Abuja
2 years ago
in Siyasa
0
Shugabancin Majalisa: Na Fi Kowa Cancanta, Ni Kadai Na Kawo Kudiri 78, Guda 21 Shugaban Kasa Ya Sa Wa Hannu – Hon Abbas Tajudeen
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan Majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Zariya a Majalisar wakilai ta taraiya Abuja, Honarabul Abbas Tajudeen, ya bayyana cewa yana daga cikin mutane 15 da suka fi kowa dadewa a Majalisar Dokokin tarayyar Nijeriya wanda kuma ya kasance daga shiyyar Arewa maso yamma.

A wata zantawa da manema labarai a garin Abuja, Hon Tajudeen wanda kuma ya kasance Shugaban Kwamitin a kan Kasa (filaye) da sufuri, ya nunar da cewa a wannan Majalisar karo na goma, zai koma karo na hudu kenan domin ci gaba da ayyukan al’umma a Majalisar.

Ya ce, “a bisa kwarewa na aiki da kuma gudunmuwar dana bayar a Majalisar musamman a kan abin da ya shafi dokoki wanda a yau bamu san gobe ba, babu wani dan Majalisar daya kawo dokoki masu mahimmaci akalla guda 78 kuma yake da dokoki guda 21 wanda shugaban Kasa ya saka musu hannu kamar ni.

“Sannan na dade a Majalisar kusan na shekaru goma sha biyu kuma na rike mukamai daban-daban, kana daidai gwargwado tsakani na da ma’aikatan da kuma abokan aiki sauran yan Majalisar, ina da tarihi mai kyau a wajen su tare da shaidar zaman lafiya da fahimtar juna da zamantakewa.

“Don haka, idan Jam’iyyar mu ta kebe wannan Kujerar izuwa Arewa ta yamma, Kusan babu wanda yake gaba da ni wajen dadewa shi yasa nima nake ganin lokaci ya yi da zan fito domin neman wannan Kujerar ta shugaban Majalisar.

Labarai Masu Nasaba

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

Acewarsa, koda a yanzu Jam’iyyar su ba ta fito ta bayyana matsayarta ba, amma ya zama dole ne sai idan mutum ya fito ya tallata kan sa tare da ra’ayin sa na neman bukatar kamin idan lokacin da Jam’iyyar za ta fito ta bayyana ra’ayin ta tare da su masu ruwa da tsaki da sauran yan Majalisar, toh a lokacin an riga an san da shi don haka zaizo da sauki idan ya kasance shiyyar da yake nema aka ba damar.

“Mun tabbatar da maganar shiyya dole ne saboda a yadda muka samu kanmu a kasar yanzu wanda shugaban Kasa da Mataimakinsa Musulmai ne, Jam’iyyar ba zata yarda ta watsar da damar ba da cewa kowa yaje ya nema domin idan aka yi haka, zai iya kasancewa shugaban Majalisar dattijai ya zama musulmi, shugaban Majalisar Tarayya ya kasance musulmi, don haka na tabbata Jam’iyya za ta so a ce kowace shiyyar an yi musu adalci tare da basu hakkin su.

“Duk wanda kaji yana magana a kan a bude neman ko neman cancanta, yana yi ne bisa son ra’ayin kansa domin idan aka duba a lokacin da aka dawo mulkin damakoradiya a 1999, shugaban Kasa a wancan lokacin ya fito da kudu maso gabas ne, kuma mataimakin sa ya fito daga Arewa masu Gabas ne, don haka idan aka duba yanayin yadda aka raba mukamai a wanchan lokacin, ya yi daidai da irin tunanin mu ne a yanzu.

“Domin Arewa ta yamma wacce ta fi kowace shiyyar yawan Jama’a, sai a ba ta kakakin Majalisar, kudu maso gabas a basu shugaban Majalisar dattawa, haka kudu maso kudu a basu mataimakin kakakin Majalisar, kana Arewa ta tsakiya a bata mataimakin shugaban Majalisar dattawa, shi yasa har yau har gobe shawarar da muke ba Gwamnati kenan da ayi amfani da irin wannan tsari da aka yi amfani da shi a baya saboda shi ne adalci.

“Hakika yin hakan, zai kara takaita korafi a kasar musamman a irin wannan gabar da kawuna sun rarrabu bisa addini da kuma kabilanci saboda yadda aka shigo wannan Zabe a kan muslim muslim tiketi, dole mu yi hattara wajen ganin cewa kowace shiyyar an bata hakkin ta domin tabbatar da zaman lafiya a kasar.” Inji shi

Da yake martani kan abokan adawar su, Hon. Abbas Tajudeen ya kara da cewa kasancewar takwarorin su sun fi su yawa kuma suna ganin zasu iya kwace wannan Kujerar tun da ba doka ce tace sai wadanda suke da Gwamnati a hannu ne kadai zasu iya zama kan Kujerar ta kakakin Majalisar ko shugaban Majalisar dattijai ba, ya bayyana cewa wannan ya zama kalubale gare su na yadda suka samu kansu a Jam’iyyar APC.

Ya ce, “Dole mu yi hattara domin idan mu yan takarar bamu hada kanmu ba muka tsayar da wanda muke ganin shi ne mafi alheri a gare mu, irin wannan abu da ake fadi mai yuwa ne wanda hakan yasa mu yan takarar mu takwas mukayi taro a gidan kakakin Majalisar inda mu ka yi alkawari a kan kowa Allah Ya ba a cikin mu, sauran zasu hada kai da shi wajen gudanar da harkokin.

Acewarsa, Dan Majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Zariya Hon. Abbas Tajudeen, wannan yana daya daga cikin matakan da suka dauka wajen ganin basu bada dama ga Jam’iyyar adawa sun zo sun yi nasara akan su ba.

  • Buhari Ya Gabatar Da Kudirin Dokar Kare Bayanai A Majalisa

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Zuwa Karshen Maris Yawan Kudaden Musayar Ketare Da Sin Take Da Su Ya Kai Dala Biliyan 3183.9

Next Post

NALDA Ta Samar Da Makarantun Horas Da Manoma A Ogun, Katsina, Abiya Da Borno

Related

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

16 hours ago
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa
Siyasa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

3 days ago
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC
Siyasa

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

4 days ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Siyasa

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

7 days ago
2027: Fastocin Takarar Shugaban Ƙasa Na Gwamnan Bauchi Sun Bayyana
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya GargaÉ—i Magoya Bayan Wike A PDP

7 days ago
Ina Da Yaƙinin Tinubu Ne Zai Lashe Zaɓen 2027 — Wike
Siyasa

Ina Da Yaƙinin Tinubu Ne Zai Lashe Zaɓen 2027 — Wike

1 week ago
Next Post
NALDA Ta Samar Da Makarantun Horas Da Manoma A Ogun, Katsina, Abiya Da Borno

NALDA Ta Samar Da Makarantun Horas Da Manoma A Ogun, Katsina, Abiya Da Borno

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

September 9, 2025
IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

September 9, 2025
An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

September 9, 2025
Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

September 9, 2025
Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

September 9, 2025
Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

September 9, 2025
Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

September 9, 2025
Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

September 9, 2025
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Babu Shirin Gaggawa Wajen Fara Aiwatar Da Harajin Kashi 5 Na Man Fetur – Minista

September 9, 2025
Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

September 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.