ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabancin Majalisa: Na Fi Kowa Cancanta, Ni Kadai Na Kawo Kudiri 78, Guda 21 Shugaban Kasa Ya Sa Wa Hannu – Hon Abbas Tajudeen

by Bashir Bello, Abuja
3 years ago
majalisa

Dan Majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Zariya a Majalisar wakilai ta taraiya Abuja, Honarabul Abbas Tajudeen, ya bayyana cewa yana daga cikin mutane 15 da suka fi kowa dadewa a Majalisar Dokokin tarayyar Nijeriya wanda kuma ya kasance daga shiyyar Arewa maso yamma.

A wata zantawa da manema labarai a garin Abuja, Hon Tajudeen wanda kuma ya kasance Shugaban Kwamitin a kan Kasa (filaye) da sufuri, ya nunar da cewa a wannan Majalisar karo na goma, zai koma karo na hudu kenan domin ci gaba da ayyukan al’umma a Majalisar.

Ya ce, “a bisa kwarewa na aiki da kuma gudunmuwar dana bayar a Majalisar musamman a kan abin da ya shafi dokoki wanda a yau bamu san gobe ba, babu wani dan Majalisar daya kawo dokoki masu mahimmaci akalla guda 78 kuma yake da dokoki guda 21 wanda shugaban Kasa ya saka musu hannu kamar ni.

ADVERTISEMENT

“Sannan na dade a Majalisar kusan na shekaru goma sha biyu kuma na rike mukamai daban-daban, kana daidai gwargwado tsakani na da ma’aikatan da kuma abokan aiki sauran yan Majalisar, ina da tarihi mai kyau a wajen su tare da shaidar zaman lafiya da fahimtar juna da zamantakewa.

“Don haka, idan Jam’iyyar mu ta kebe wannan Kujerar izuwa Arewa ta yamma, Kusan babu wanda yake gaba da ni wajen dadewa shi yasa nima nake ganin lokaci ya yi da zan fito domin neman wannan Kujerar ta shugaban Majalisar.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

Acewarsa, koda a yanzu Jam’iyyar su ba ta fito ta bayyana matsayarta ba, amma ya zama dole ne sai idan mutum ya fito ya tallata kan sa tare da ra’ayin sa na neman bukatar kamin idan lokacin da Jam’iyyar za ta fito ta bayyana ra’ayin ta tare da su masu ruwa da tsaki da sauran yan Majalisar, toh a lokacin an riga an san da shi don haka zaizo da sauki idan ya kasance shiyyar da yake nema aka ba damar.

“Mun tabbatar da maganar shiyya dole ne saboda a yadda muka samu kanmu a kasar yanzu wanda shugaban Kasa da Mataimakinsa Musulmai ne, Jam’iyyar ba zata yarda ta watsar da damar ba da cewa kowa yaje ya nema domin idan aka yi haka, zai iya kasancewa shugaban Majalisar dattijai ya zama musulmi, shugaban Majalisar Tarayya ya kasance musulmi, don haka na tabbata Jam’iyya za ta so a ce kowace shiyyar an yi musu adalci tare da basu hakkin su.

“Duk wanda kaji yana magana a kan a bude neman ko neman cancanta, yana yi ne bisa son ra’ayin kansa domin idan aka duba a lokacin da aka dawo mulkin damakoradiya a 1999, shugaban Kasa a wancan lokacin ya fito da kudu maso gabas ne, kuma mataimakin sa ya fito daga Arewa masu Gabas ne, don haka idan aka duba yanayin yadda aka raba mukamai a wanchan lokacin, ya yi daidai da irin tunanin mu ne a yanzu.

“Domin Arewa ta yamma wacce ta fi kowace shiyyar yawan Jama’a, sai a ba ta kakakin Majalisar, kudu maso gabas a basu shugaban Majalisar dattawa, haka kudu maso kudu a basu mataimakin kakakin Majalisar, kana Arewa ta tsakiya a bata mataimakin shugaban Majalisar dattawa, shi yasa har yau har gobe shawarar da muke ba Gwamnati kenan da ayi amfani da irin wannan tsari da aka yi amfani da shi a baya saboda shi ne adalci.

“Hakika yin hakan, zai kara takaita korafi a kasar musamman a irin wannan gabar da kawuna sun rarrabu bisa addini da kuma kabilanci saboda yadda aka shigo wannan Zabe a kan muslim muslim tiketi, dole mu yi hattara wajen ganin cewa kowace shiyyar an bata hakkin ta domin tabbatar da zaman lafiya a kasar.” Inji shi

Da yake martani kan abokan adawar su, Hon. Abbas Tajudeen ya kara da cewa kasancewar takwarorin su sun fi su yawa kuma suna ganin zasu iya kwace wannan Kujerar tun da ba doka ce tace sai wadanda suke da Gwamnati a hannu ne kadai zasu iya zama kan Kujerar ta kakakin Majalisar ko shugaban Majalisar dattijai ba, ya bayyana cewa wannan ya zama kalubale gare su na yadda suka samu kansu a Jam’iyyar APC.

Ya ce, “Dole mu yi hattara domin idan mu yan takarar bamu hada kanmu ba muka tsayar da wanda muke ganin shi ne mafi alheri a gare mu, irin wannan abu da ake fadi mai yuwa ne wanda hakan yasa mu yan takarar mu takwas mukayi taro a gidan kakakin Majalisar inda mu ka yi alkawari a kan kowa Allah Ya ba a cikin mu, sauran zasu hada kai da shi wajen gudanar da harkokin.

Acewarsa, Dan Majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Zariya Hon. Abbas Tajudeen, wannan yana daya daga cikin matakan da suka dauka wajen ganin basu bada dama ga Jam’iyyar adawa sun zo sun yi nasara akan su ba.

  • Buhari Ya Gabatar Da Kudirin Dokar Kare Bayanai A Majalisa
majalisa
Bashir Bello, Abuja
+ postsBio
  • Bashir Bello, Abuja
    https://hausa.leadership.ng/author/bashir-bello-abuja/
    Sanata Kaka Lawan Ya Gabatar Da Kudirin Tattara Dokokin Nijeriya Na Tsawon Shekara 19
  • Bashir Bello, Abuja
    https://hausa.leadership.ng/author/bashir-bello-abuja/
    Majalisar Dattawa Ta Amince Da Kudirin Gaggauta Aikin Makarantar Kwastam A Bauchi
  • Bashir Bello, Abuja
    https://hausa.leadership.ng/author/bashir-bello-abuja/
    APC Ce Za Ta Yi Nasarar Samar Da Shugabanci A Majalisa – Hon. Wase
  • Bashir Bello, Abuja
    https://hausa.leadership.ng/author/bashir-bello-abuja/
    Ba Za Mu Lamunci Dauki-Dora A Shugabancin Majalisa Ba —Kawu Sumaila

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
majalisa
Siyasa

Muna Da Yan Takarar Gwamna A Jihohi 28 Don Shiga Zaben 2027

September 6, 2026
Next Post
NALDA Ta Samar Da Makarantun Horas Da Manoma A Ogun, Katsina, Abiya Da Borno

NALDA Ta Samar Da Makarantun Horas Da Manoma A Ogun, Katsina, Abiya Da Borno

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.