• English
  • Business News
Thursday, October 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabancin PDP: Yankin Arewa Ta Tsakiya Ya Dage Kan Cika Wa’adin Ayu

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
PDP

Kungiyar ‘ya’yan jam’iyyar PDP na yankin arewa ta tsakiya ta fara tattaunawa da shugabannin jam’iyyar PDP domin fitar da shugaban jam’iyyar na kasa daga yanki domin samun damar kammala wa’adin mulkin Dakta Iyorchia Ayu.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da jam’iyyar ta sanar da ranar gudanar da babban taron kwamitin zartarwa da ta tsara za a yi a ranakun 17 da 18 ga Afrilun 2024.

  • An Gudanar Da Zaman Sakatarori Na Taron Kiyaye Tsaro Na SCO Karo Na 19
  • Bayani A Kan Zakkar Shan Ruwa Da Sallar Idi

Rahotanni sun bayyana cewa tattaunawar a tsakanin shugabanni jam’iyyar a yankin ya yi nisa.
Wata majiya mai tushe ta ce, “Muna tsammanin yankin zai bayyana zabinsa kafin babban taron kwamitin zartarwa.”

Cikin mutanen da ake tsammanin za a fitar sun hada da tsohon shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki daga Jihar Kwara da Sanata Gabriel Suswam wanda suka fito daga wuri daya da Ayu a Jihar Benuwai.
Haka kuma an bayyana cewa shugabannin jam’iyyar a yankin sun gana a Abuja domin gudanar da shirye-shiryen cimma wannan burin nasu.

Wadanda suka halarci ganawar sun hada da shugabannin jam’iyyar na jihohi shida da ke yankin arewa ta tsakiya ciki har da na Abuja da kuma sauran wakilai da aka zaba.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

Sakamakon ganawar ya nuna cewa mahalarta tron sun amince shugabancin PDP ya tsaya a yankin arewa ta tsakiya domin kammala wa’adin mulkin Ayu, yayin mafi yawanci suka amince da cewa Damagum ya ci gaba da rike mukaminsa na mataimakin shugaban jam’iyyar na kasa.

Majiya a wurin taron ta bayyana cewa ana tsammanin gwamnan Jihar Filato, Caleb Muftwang zai shirya taron shugabannin yankin domin tattauna yadda za a cimma samun wannan nasara.

Majiyar ta ce, “Da yake yanzu zaben 2023 ya shude, muna tsammanin shugabannin jam’iyyar za su yi abin da ya dace wajen sake fasalin jam’iyyarmu dpmin ta dawo kan hayyacinta.

“Lokacin da Ayu yake shugabancin jam’iyyar ya yi kokari sosai, shi ya sa mu mutanen yankin arewa na tsakiya muka hadu wuri guda tare da amincewa a maye gurbinsa daga cikinmu, saboda matsayar da aka cimma a 2023 har yanzu tana aiki. Tsarin mulkin jam’iyyarmu ya amince da haka.

“Mun gudanar da taro kan wannan matsalar. Idan za mu iya tunawa dai, shugabanninmu sun gudanar da ganawa a Abuja, bayan taron kwamitin gudanarwa na jam’iyyar.”

A dai mika shugabancin jam’iyyar PDP a yankin arewa ta tsakiya kafin zaben 2023, wanda Ayu ya zama shugabanta ba tare da wata hamayyya ba.

An dai zabi Ayu ne domin ya maye gurbin Prince Uche Secondus wanda aka cire daga mukaminsa bisa rawar da mai gidansa a siyasa ya taka kan lamarin.

Ya dai fuskanci matsin lamba daga wurin Wike Nyesom Wike shugaban gwamnonin PDP biyar da suka balle da ake kira G-5, tun bayan da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya lashe zaben fitar da gwani na neman tikitin zama dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP.

Bayan samun takaddama mai zafi, daga karshe dai an cire Ayu a matsayin shugaban PDP, inda aka sa mataimakin shugaban jam’iyyar na yankin arewa, Illiya Damagum dan asalin Jihar Yobe da ke yankin arewa maso gabas a matsayin mukaddashin shugaba tun daga ranar 28 ga Maris na 2023.

A yanzu haka dai kwamitin gudanarwa na jam’iyyar da Damagum yake jagoranta yana shan matsin lamba kan gudanar da babban taron jam’iyyar na kasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
Ku Nisanci Shiga Siyasa, Gargaɗin INEC Ga Sabbin Kwamishinoninta

Zaben Edo Da Ondo: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gana Da Hukumar Zabe

LABARAI MASU NASABA

Yajin aiki

Gwamnatin Tarayya Ta Jajantawa Waɗanda Fashewar Tankar Mai Ta Rutsa Da Su A Neja 

October 23, 2025
Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas

Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas

October 23, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Diflomasiyyar Shugabanni Na Matukar Taka Rawar Gani Wajen Jagorantar Dangantakar Sin Da Amurka

October 22, 2025
NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

October 23, 2025
Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

October 22, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Ɗan Shekara 15 Da Ake Zargi Da Yin Fashi Da Makami A Gombe

October 22, 2025
Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

October 22, 2025
An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

October 22, 2025
Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

October 22, 2025
Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

October 22, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.